< 1 Sama’ila 12 >

1 Sama’ila ya ce wa Isra’ilawa duka, “Na saurari abubuwan da kuka faɗa mini, na kuma naɗa muku sarki.
Då sade Samuel till hela Israel: Si, jag hafver hört edra röst uti allt det I mig sagt hafven, och hafver gjort en Konung öfver eder.
2 Yanzu kuna da sarki a matsayin shugaba, ni kuwa na tsufa har da furfura, yarana maza kuma suna tare da ku. Na yi shugabancinku tun ina yaro.
Och si, der går nu edar Konung för eder; men jag är gammal och grå vorden, och mine söner äro när eder, och jag hafver gångit för eder, ifrå min ungdom allt intill denna dag.
3 Ga ni a gabanku. Idan na yi wani abin da ba daidai ba sai ku faɗa a gaban Ubangiji, da gaban sarkin da ya keɓe. Ko na taɓa ƙwace saniya ko jakin wani? Ko na taɓa cuce wani, ko in danne hakkinsa? Ko na taɓa cin hanci daga hannun ɗayanku? Idan na taɓa yi ɗaya daga cikin waɗannan, sai ku faɗa mini, zan kuwa mayar masa.”
Si, här är jag: Svarer mig inför Herranom och hans smorda, om jag någons mans oxa eller åsna tagit hafver? Om jag hafver någrom gjort öfvervåld och orätt? Om jag någon undertryckt hafver? Om jag af någons mans hand hafver tagit gåfvor, och hållit det hemliga? Så vill jag gifva eder det igen.
4 Suka ce, “Ba ka cuci ko danne hakkin kowa ba, ba ka ƙwace kome daga hannun kowa ba.”
De sade: Du hafver intet öfvervåld eller orätt gjort oss, ej heller någon undertryckt; ej heller af någons mans hand något tagit.
5 Sama’ila ya ce musu, “Ubangiji yă zama shaida a kanku, shafaffensa kuma yă zama shaida a wannan rana cewa ba ku same ni da wani laifin kome ba.” Suka ce, “I, shi ne shaida.”
Han sade till dem: Herren och hans smorde vare vittne emot eder i dag, att i intet hafven funnit i mine hand. De sade: Ja, vare vittne.
6 Sa’an nan Sama’ila ya ce wa mutane, Ubangiji ne ya naɗa Musa da Haruna suka fitar da kakanninku daga Masar.
Och Samuel sade till folket: Ja, Herren, som Mose och Aaron gjort hafver, och förde edra fäder utur Egypti land.
7 Yanzu ku tsaya nan zan yi fito-na-fito da ku da shaida a gaban Ubangiji kan dukan ayyuka masu alherin da Ubangiji ya aikata saboda ku da kakanninku.
Så går nu fram, att jag må döma eder för Herranom, öfver all Herrans rättfärdighet, som han med eder och edra fäder gjort hafver.
8 Bayan da Yaƙub da’ya’yansa suka shiga Masar suka yi kukan neman taimako daga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya aika musu da Musa da Haruna. Su ne suka kawo kakanni-kakanninku daga Masar suka zauna a nan.
Då Jacob var kommen in uti Egypten, ropade edra fäder till Herran. Och Herren sände Mose och Aaron, att de skulle föra edra fäder utur Egypten, och lät bo dem på detta rum.
9 Amma suka manta da Ubangiji Allahnsu, shi kuma ya bashe su a hannun Sisera shugaban rundunar Hazor da kuma hannun Filistiyawa da sarkin Mowab wanda suka yi yaƙi da su.
Men när de förgåto Herran sin Gud, sålde han dem under Sisera våld, höfvitsmansens i Hazor, och uti de Philisteers våld, och uti de Moabiters Konungs våld; de stridde emot dem.
10 Suka yi kuka a gaban Ubangiji suka ce, “Mun yi zunubi mun bar Ubangiji, muka bauta wa Ba’al da Ashtarot. Amma ka cece mu yanzu daga hannun abokan gābanmu, mu kuwa za mu bauta maka.”
Och de ropade till Herran, och sade: Vi hafve syndat, att vi hafve öfvergifvit Herran, och tjent Baalim och Astaroth; men frälsa oss nu ifrå våra fiendars hand, så vilje vi tjena dig.
11 Sai Ubangiji ya aiki Yerub-Ba’al da Bedan da Yefta da Sama’ila, ya cece ku daga hannun abokan gābanku a kowane gefe domin ku sami cikakken zaman lafiya.
Då sände Herren JerubBaal, Bedan, Jephthah och Samuel, och frälste eder utur edra fiendars händer, allt omkring, och lät eder bo tryggeliga.
12 Amma da kuka ga Nahash sarkin Ammonawa yana matsowa yă yaƙe, sai kuka ce mini, “Sam, muna so sarki yă shugabance mu.” Ko da yake Ubangiji Allahnku ne yake mulkinku.
När I då sågen att Nahas, Ammons barnas Konung, Kom emot eder, saden I till mig: Icke du, utan en Konung skall råda öfver oss; ändock Herren edar Gud var edar Konung.
13 Yanzu ga sarkinku da kuka zaɓa wanda kuka nema, ga shi Ubangiji ya naɗa muku sarki.
Nu, här hafven I edar Konung, den I utvalt och begärat hafven; ty, si, Herren hafver satt en Konung öfver eder.
14 In kuka ji tsoron Ubangiji, kuka bauta masa, kuka yi masa biyayya, ba ku kuwa ƙi bin umarninsa ba, in kuma ku da sarkin da yake mulkinku kun bi Ubangiji Allahnku, to, za ku zauna lafiya.
Om I nu frukten Herran, och tjenen honom, och hören hans röst, och icke ären Herrans mun ohörige, så skolen både I och edar Konung, som öfver eder råder, efterfölja Herran edar Gud.
15 Amma in ba ku yi biyayya ga Ubangiji ba, in kuma kuka ƙi bin umarnansa, fushinsa zai zauna a kanku.
Om I icke hören Herrans röst, utan ären Herrans mun ohörige, så skall Herrans hand vara emot eder och edra fäder.
16 Yanzu ku tsaya tsit ku ga abin da Ubangiji ke dab da yi a gabanku.
Går också nu fram, och ser det stora ärende, som Herren göra skall för edor ögon.
17 Ba lokacin yankan alkama ke nan ba? Zan roƙi Ubangiji yă aiko da tsawa da ruwan sama, za ku kuwa gane wace irin mugunta kuka yi a gaban Ubangiji sa’ad da kuka roƙa a ba ku sarki.
Är icke nu hveteanden? Dock vill jag åkalla Herran, att han skall låta dundra och regna, att I skolen förnimma och se det stora onda, som I för Herrans ögon gjort hafven, att I hafven bedts eder Konung.
18 Sai Sama’ila ya roƙi Ubangiji, a ranar kuwa Ubangiji ya aiko da tsawa da ruwan sama. Dukan mutane suka ji tsoron Ubangiji da kuma Sama’ila.
Och då Samuel åkallade Herran, lät Herren den samma dagen dundra och regna; då fruktade allt folket Herran och Samuel ganska storliga;
19 Dukan mutane suka ce wa Sama’ila, “Ka yi addu’a ga Ubangiji Allahnka saboda bayinka, domin kada mu mutu, gama mun ƙara wa kanmu zunubi da muka roƙa a yi mana sarki.”
Och sade alle till Samuel: Bed för dina tjenare Herran din Gud, att vi icke dö; ty öfver alla våra synder hafve vi ock gjort detta onda, att vi beddes oss Konung.
20 Sama’ila ya ce, “Kada ku ji tsoro.” Kun yi waɗannan mugunta duk da haka kada ku bar bin Ubangiji, amma ku bauta wa Ubangiji da dukan zuciyarku.
Och Samuel sade till folket: Frukter eder intet, I hafven sannerliga gjort allt det onda; dock träder icke af ifrå Herranom, utan tjener Herranom af allo hjerta.
21 Kada ku bi alloli marasa amfani. Ba za su iya yi muku kome nagari ba, ba kuwa za su iya cece ku ba, gama ba su da amfani.
Och viker icke efter fåfängelig ting; ty det gagnar eder intet, och kan intet hjelpa eder, efter det en fåfängelig ting är.
22 Saboda suna mai girma da Ubangiji yake da shi, ba zai taɓa ƙin mutanensa ba. Gama Ubangiji ya ji daɗi da ya yi ku mutanensa.
Förty Herren öfvergifver icke sitt folk, för sitt stora Namns skull; ty Herren hafver begynt till att göra eder sig sjelfvom till ett folk.
23 Ni kam ba zai taɓa yiwu in yi wa Ubangiji zunubi ta wurin ƙin yin addu’a dominku ba. Zan koya muku hanyar da tana da kyau da ta kuma cancanta.
Vare ock fjerran ifrå mig, att jag så skulle synda emot Herran, att jag skulle aflåta bedja för eder, och lära eder den goda och rätta vägen.
24 Amma ku amince za ku ji tsoron Ubangiji, ku bauta masa da aniya da dukan zuciyarku, kuna da manyan abubuwan da ya yi muku.
Allenast frukter Herran, och tjener honom troliga af allo hjerta; förty I hafven sett huru stor ting han gör med eder.
25 Amma in kuka duƙufa cikin aikin mugunta da ku da sarkinku za a hallaka ku.
Men om I gören det ondt är, så skolen både I och edar Konung förgås.

< 1 Sama’ila 12 >