< 1 Sama’ila 12 >
1 Sama’ila ya ce wa Isra’ilawa duka, “Na saurari abubuwan da kuka faɗa mini, na kuma naɗa muku sarki.
And Samuel said unto all Israel, Behold, I have hearkened unto your voice in all that ye said unto me, and I have set a king over you.
2 Yanzu kuna da sarki a matsayin shugaba, ni kuwa na tsufa har da furfura, yarana maza kuma suna tare da ku. Na yi shugabancinku tun ina yaro.
And now, behold, the king is walking before you; and I am old and gray-headed; and my sons, behold, they are with you; and I have walked before you from my youth even until this day.
3 Ga ni a gabanku. Idan na yi wani abin da ba daidai ba sai ku faɗa a gaban Ubangiji, da gaban sarkin da ya keɓe. Ko na taɓa ƙwace saniya ko jakin wani? Ko na taɓa cuce wani, ko in danne hakkinsa? Ko na taɓa cin hanci daga hannun ɗayanku? Idan na taɓa yi ɗaya daga cikin waɗannan, sai ku faɗa mini, zan kuwa mayar masa.”
Behold, here am I; testify against me in the presence of the Lord, and in the presence of his anointed: Whose ox have I taken? or whose ass have I taken? or whom have I defrauded? whom have I oppressed? or from whose hand have I received any ransom so that I withdrew my eyes from him? and I will restore it you.
4 Suka ce, “Ba ka cuci ko danne hakkin kowa ba, ba ka ƙwace kome daga hannun kowa ba.”
And they said, Thou hast not defrauded us, nor hast thou oppressed us, and thou hast not taken from any man's hand the least.
5 Sama’ila ya ce musu, “Ubangiji yă zama shaida a kanku, shafaffensa kuma yă zama shaida a wannan rana cewa ba ku same ni da wani laifin kome ba.” Suka ce, “I, shi ne shaida.”
And he said unto them, The Lord is witness against you, and his anointed is witness this day, that ye have not found in my hand the least: and they answered, He is witness.
6 Sa’an nan Sama’ila ya ce wa mutane, Ubangiji ne ya naɗa Musa da Haruna suka fitar da kakanninku daga Masar.
And Samuel said unto the people, It is the Lord who did [wonders through] Moses and Aaron, and who brought your fathers up out of the land of Egypt.
7 Yanzu ku tsaya nan zan yi fito-na-fito da ku da shaida a gaban Ubangiji kan dukan ayyuka masu alherin da Ubangiji ya aikata saboda ku da kakanninku.
And now stand up, that I may hold judgment with you before the Lord concerning all the benefits of the Lord, which he hath done to you and to your fathers.
8 Bayan da Yaƙub da’ya’yansa suka shiga Masar suka yi kukan neman taimako daga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya aika musu da Musa da Haruna. Su ne suka kawo kakanni-kakanninku daga Masar suka zauna a nan.
When Jacob was come into Egypt, then did your fathers cry unto the Lord, and the Lord sent Moses and Aaron, and they brought forth your fathers out of Egypt, and caused them to dwell in this place.
9 Amma suka manta da Ubangiji Allahnsu, shi kuma ya bashe su a hannun Sisera shugaban rundunar Hazor da kuma hannun Filistiyawa da sarkin Mowab wanda suka yi yaƙi da su.
And when they forgot the Lord their God, he sold them into the hand of Sissera, the chief of the host of Chazor, and into the hand of the Philistines, and into the hand of the king of Moab, and they made war against them.
10 Suka yi kuka a gaban Ubangiji suka ce, “Mun yi zunubi mun bar Ubangiji, muka bauta wa Ba’al da Ashtarot. Amma ka cece mu yanzu daga hannun abokan gābanmu, mu kuwa za mu bauta maka.”
And they cried [then] unto the Lord, and said, We have sinned, because we have forsaken the Lord, and have served the Be'alim and the 'Ashtaroth; and now deliver us out of the hand of our enemies, and we will serve thee.
11 Sai Ubangiji ya aiki Yerub-Ba’al da Bedan da Yefta da Sama’ila, ya cece ku daga hannun abokan gābanku a kowane gefe domin ku sami cikakken zaman lafiya.
And the Lord sent Yerubba'al, and Bedan, and Yiphthach, and Samuel, and he delivered you out of the hand of your enemies on every side, so that ye dwelt safely.
12 Amma da kuka ga Nahash sarkin Ammonawa yana matsowa yă yaƙe, sai kuka ce mini, “Sam, muna so sarki yă shugabance mu.” Ko da yake Ubangiji Allahnku ne yake mulkinku.
But when ye saw that Nachash the king of the children of 'Ammon came against you, ye said unto me, No; but a king shall reign over us: when the Lord your God is your king.
13 Yanzu ga sarkinku da kuka zaɓa wanda kuka nema, ga shi Ubangiji ya naɗa muku sarki.
And now here is the king whom ye have chosen, whom ye have asked for! and, behold, the Lord hath set over you a king.
14 In kuka ji tsoron Ubangiji, kuka bauta masa, kuka yi masa biyayya, ba ku kuwa ƙi bin umarninsa ba, in kuma ku da sarkin da yake mulkinku kun bi Ubangiji Allahnku, to, za ku zauna lafiya.
If ye will fear the Lord, and serve him, and obey his voice, and will not rebel against the will of the Lord: then shall both ye and also the king that reigneth over you continue following the Lord your God.
15 Amma in ba ku yi biyayya ga Ubangiji ba, in kuma kuka ƙi bin umarnansa, fushinsa zai zauna a kanku.
But if ye will not hearken to the voice of the Lord, and rebel against the will of the Lord: then will the hand of the Lord be against you, as it was against your fathers.
16 Yanzu ku tsaya tsit ku ga abin da Ubangiji ke dab da yi a gabanku.
And now stand up and see this great thing, which the Lord is about doing before your eyes.
17 Ba lokacin yankan alkama ke nan ba? Zan roƙi Ubangiji yă aiko da tsawa da ruwan sama, za ku kuwa gane wace irin mugunta kuka yi a gaban Ubangiji sa’ad da kuka roƙa a ba ku sarki.
Is there not wheat-harvest today? I will call unto the Lord, and he will send thunders and rain; and ye will [thus] perceive and see that your wickedness is great, which ye have done, in the eyes of the Lord, to ask for yourselves a king.
18 Sai Sama’ila ya roƙi Ubangiji, a ranar kuwa Ubangiji ya aiko da tsawa da ruwan sama. Dukan mutane suka ji tsoron Ubangiji da kuma Sama’ila.
And Samuel called unto the Lord; and the Lord sent thunders and rain on that day: and all the people feared greatly the Lord and Samuel.
19 Dukan mutane suka ce wa Sama’ila, “Ka yi addu’a ga Ubangiji Allahnka saboda bayinka, domin kada mu mutu, gama mun ƙara wa kanmu zunubi da muka roƙa a yi mana sarki.”
And all the people said unto Samuel, Pray in behalf of thy servants unto the Lord thy God, that we may not die; for we have added unto all our sins yet this evil, to ask for ourselves a king.
20 Sama’ila ya ce, “Kada ku ji tsoro.” Kun yi waɗannan mugunta duk da haka kada ku bar bin Ubangiji, amma ku bauta wa Ubangiji da dukan zuciyarku.
And Samuel said unto the people, Fear not; ye have indeed done all this evil: yet turn not aside from following the Lord, and serve ye the Lord with all your heart;
21 Kada ku bi alloli marasa amfani. Ba za su iya yi muku kome nagari ba, ba kuwa za su iya cece ku ba, gama ba su da amfani.
And turn ye not aside; for then would ye go after vain things, which cannot profit nor deliver; because they are vain.
22 Saboda suna mai girma da Ubangiji yake da shi, ba zai taɓa ƙin mutanensa ba. Gama Ubangiji ya ji daɗi da ya yi ku mutanensa.
For the Lord will not forsake his people for the sake of his great name; because it hath pleased the Lord to make you a people unto himself.
23 Ni kam ba zai taɓa yiwu in yi wa Ubangiji zunubi ta wurin ƙin yin addu’a dominku ba. Zan koya muku hanyar da tana da kyau da ta kuma cancanta.
Moreover as for me, far be it from me that I should sin against the Lord by ceasing to pray in behalf of you; but I will teach you the good and the right way:
24 Amma ku amince za ku ji tsoron Ubangiji, ku bauta masa da aniya da dukan zuciyarku, kuna da manyan abubuwan da ya yi muku.
Only fear the Lord, and serve him in truth with all your heart; for see what great things he hath done with you.
25 Amma in kuka duƙufa cikin aikin mugunta da ku da sarkinku za a hallaka ku.
But if ye will in any wise do wickedly, both ye yourselves as also your king shall perish.