< 1 Sama’ila 12 >

1 Sama’ila ya ce wa Isra’ilawa duka, “Na saurari abubuwan da kuka faɗa mini, na kuma naɗa muku sarki.
And Samuel said to all Israel: Behold I have hearkened to your voice in all that you said to me, and have made a king over you.
2 Yanzu kuna da sarki a matsayin shugaba, ni kuwa na tsufa har da furfura, yarana maza kuma suna tare da ku. Na yi shugabancinku tun ina yaro.
And now the king goeth before you: but I am old and greyheaded: and my sons are with you: having then conversed with you from my youth unto this day, behold here I am.
3 Ga ni a gabanku. Idan na yi wani abin da ba daidai ba sai ku faɗa a gaban Ubangiji, da gaban sarkin da ya keɓe. Ko na taɓa ƙwace saniya ko jakin wani? Ko na taɓa cuce wani, ko in danne hakkinsa? Ko na taɓa cin hanci daga hannun ɗayanku? Idan na taɓa yi ɗaya daga cikin waɗannan, sai ku faɗa mini, zan kuwa mayar masa.”
Speak of me before the Lord, and before his anointed, whether I have taken any man’s ox, or ass: If I have wronged any man, if I have oppressed any man, if I have taken a bribe at any man’s hand: and I will despise it this day, and will restore it to you.
4 Suka ce, “Ba ka cuci ko danne hakkin kowa ba, ba ka ƙwace kome daga hannun kowa ba.”
And they said: Thou hast not wronged us, nor oppressed us, nor taken ought at any man’s hand.
5 Sama’ila ya ce musu, “Ubangiji yă zama shaida a kanku, shafaffensa kuma yă zama shaida a wannan rana cewa ba ku same ni da wani laifin kome ba.” Suka ce, “I, shi ne shaida.”
And he said to them: The Lord is witness against you, and his anointed is witness this day, that you have not found any thing in my hand. And they said: He is witness.
6 Sa’an nan Sama’ila ya ce wa mutane, Ubangiji ne ya naɗa Musa da Haruna suka fitar da kakanninku daga Masar.
And Samuel said to the people: It is the Lord, who made Moses and Aaron, and brought our fathers out of the land of Egypt.
7 Yanzu ku tsaya nan zan yi fito-na-fito da ku da shaida a gaban Ubangiji kan dukan ayyuka masu alherin da Ubangiji ya aikata saboda ku da kakanninku.
Now therefore stand up, that I may plead in judgment against you before the Lord, concerning all the kindness of the Lord, which he hath shewn to you, and to your fathers:
8 Bayan da Yaƙub da’ya’yansa suka shiga Masar suka yi kukan neman taimako daga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya aika musu da Musa da Haruna. Su ne suka kawo kakanni-kakanninku daga Masar suka zauna a nan.
How Jacob went into Egypt, and your fathers cried to the Lord: and the Lord sent Moses and Aaron, and brought your fathers out of Egypt: and made them dwell in this place.
9 Amma suka manta da Ubangiji Allahnsu, shi kuma ya bashe su a hannun Sisera shugaban rundunar Hazor da kuma hannun Filistiyawa da sarkin Mowab wanda suka yi yaƙi da su.
And they forgot the Lord their God, and he delivered them into the hands of Sisara, captain of the army of Hasor, and into the hands of the Philistines, and into the hand of the king of Moab, and they fought against them.
10 Suka yi kuka a gaban Ubangiji suka ce, “Mun yi zunubi mun bar Ubangiji, muka bauta wa Ba’al da Ashtarot. Amma ka cece mu yanzu daga hannun abokan gābanmu, mu kuwa za mu bauta maka.”
But afterwards they cried to the Lord, and said: We have sinned, because we have forsaken the Lord, and have served Baalim and Astaroth: but now deliver us from the hand of our enemies, and we will serve thee.
11 Sai Ubangiji ya aiki Yerub-Ba’al da Bedan da Yefta da Sama’ila, ya cece ku daga hannun abokan gābanku a kowane gefe domin ku sami cikakken zaman lafiya.
And the Lord sent Jerobaal, and Badan, and Jephte, and Samuel, and delivered you from the hand of your enemies round about, and you dwelt securely.
12 Amma da kuka ga Nahash sarkin Ammonawa yana matsowa yă yaƙe, sai kuka ce mini, “Sam, muna so sarki yă shugabance mu.” Ko da yake Ubangiji Allahnku ne yake mulkinku.
But seeing that Naas king of the children of Ammon was come against you, you said to me: Nay, but a king shall reign over us: whereas the Lord your God was your king.
13 Yanzu ga sarkinku da kuka zaɓa wanda kuka nema, ga shi Ubangiji ya naɗa muku sarki.
Now therefore your king is here, whom you have chosen and desired: Behold the Lord hath given you a king.
14 In kuka ji tsoron Ubangiji, kuka bauta masa, kuka yi masa biyayya, ba ku kuwa ƙi bin umarninsa ba, in kuma ku da sarkin da yake mulkinku kun bi Ubangiji Allahnku, to, za ku zauna lafiya.
If you will fear the Lord, and serve him, and hearken to his voice, and not provoke the mouth of the Lord: then shall both you, and the king who reigneth over you, be followers of the Lord your God.
15 Amma in ba ku yi biyayya ga Ubangiji ba, in kuma kuka ƙi bin umarnansa, fushinsa zai zauna a kanku.
But if you will not hearken to the voice of the Lord, but will rebel against his words, the hand of the Lord shall be upon you, and upon your fathers.
16 Yanzu ku tsaya tsit ku ga abin da Ubangiji ke dab da yi a gabanku.
Now then stand, and see this great thing which the Lord will do in your sight.
17 Ba lokacin yankan alkama ke nan ba? Zan roƙi Ubangiji yă aiko da tsawa da ruwan sama, za ku kuwa gane wace irin mugunta kuka yi a gaban Ubangiji sa’ad da kuka roƙa a ba ku sarki.
Is it not wheat harvest today? I will call upon the Lord, and he shall send thunder and rain: and you shall know and see that you yourselves have done a great evil in the sight of the Lord, in desiring a king over you.
18 Sai Sama’ila ya roƙi Ubangiji, a ranar kuwa Ubangiji ya aiko da tsawa da ruwan sama. Dukan mutane suka ji tsoron Ubangiji da kuma Sama’ila.
And Samuel cried unto the Lord, and the Lord sent thunder and rain that day.
19 Dukan mutane suka ce wa Sama’ila, “Ka yi addu’a ga Ubangiji Allahnka saboda bayinka, domin kada mu mutu, gama mun ƙara wa kanmu zunubi da muka roƙa a yi mana sarki.”
And all the people greatly feared the Lord and Samuel. And all the people said to Samuel: Pray for thy servants to the Lord thy God, that we may not die, for we have added to all our sins this evil, to ask for a king.
20 Sama’ila ya ce, “Kada ku ji tsoro.” Kun yi waɗannan mugunta duk da haka kada ku bar bin Ubangiji, amma ku bauta wa Ubangiji da dukan zuciyarku.
And Samuel said to the people: Fear not, you have done all this evil: but yet depart not from following the Lord, but serve the Lord with all your heart.
21 Kada ku bi alloli marasa amfani. Ba za su iya yi muku kome nagari ba, ba kuwa za su iya cece ku ba, gama ba su da amfani.
And turn not aside after vain things which shall never profit you, nor deliver you, because they are vain.
22 Saboda suna mai girma da Ubangiji yake da shi, ba zai taɓa ƙin mutanensa ba. Gama Ubangiji ya ji daɗi da ya yi ku mutanensa.
And the Lord will not forsake his people for his great name’s sake: because the Lord hath sworn to make you his people.
23 Ni kam ba zai taɓa yiwu in yi wa Ubangiji zunubi ta wurin ƙin yin addu’a dominku ba. Zan koya muku hanyar da tana da kyau da ta kuma cancanta.
And far from me be this sin against the Lord, that I should cease to pray for you, and I will teach you the good and right way.
24 Amma ku amince za ku ji tsoron Ubangiji, ku bauta masa da aniya da dukan zuciyarku, kuna da manyan abubuwan da ya yi muku.
Therefore fear the Lord, and serve him in truth and with your whole heart, for you have seen the great works which he hath done among you.
25 Amma in kuka duƙufa cikin aikin mugunta da ku da sarkinku za a hallaka ku.
But if you will still do wickedly: both you and your king shall perish together.

< 1 Sama’ila 12 >