< 1 Sama’ila 11 >
1 Nahash mutumin Ammon ya haura ya kewaye Yabesh Gileyad da yaƙi. Dukan mutanen Yabesh suka ce masa, “Ka ƙulla amana da mu, mu kuwa za mu bauta maka.”
Så for Nahas, den Ammoniten, upp, och belade Jabes i Gilead. Och alle män i Jabes sade till Nahas: Gör ett förbund med oss, så vilje vi tjena dig.
2 Amma Nahash ya ce, “Zan ƙulla amana da ku kawai a kan sharaɗin cewa zan ƙwaƙulo idon dama na kowannenku, ta haka za a kunyata Isra’ila.”
Men Nahas, den Ammoniten, svarade dem: I så måtto vill jag göra ett förbund med eder, att jag stinger ut högra ögat på eder alla, och sätter eder till en försmädelse i hela Israel.
3 Dattawan Yabesh suka ce masa, “Ka ba mu kwana bakwai don mu aika manzanni a dukan ƙasar Isra’ila idan ba mu sami wanda zai cece mu ba, za mu ba da kanmu gare ka.”
Då sade till honom alle äldste i Jabes: Gif oss sju dagar, att vi måge sända bådskap i alla Israels gränsor; är då ingen hjelp, så vilje vi gå ut till dig.
4 Da manzannin suka zo Gibeya garin Shawulu, suka gaya wa mutane wannan sharaɗin, suka yi kuka mai zafi.
Så kommo bådskapen till Gibea Sauls, och sade detta för folkens öron. Då hof allt folket sina röst upp, och gret.
5 A daidai wannan lokacin kuwa Shawulu yana dawowa daga gona tare da shanunsa na noma, sai ya ce, “Me ya faru, mutane suna kuka haka?” Sai suka faɗa masa abin da mutanen Yabesh suka faɗa musu.
Och si, då kom Saul utaf markene, gångandes bakefter sitt fä, och sade: Hvad skadar folkena, att det gråter? Då förtäljde de honom de mäns ord af Jabes.
6 Da Shawulu ya ji, sa Ruhun Allah ya sauko a kansa da iko, ya husata ƙwarai.
Då kom Guds Ande öfver honom, när han dessa orden hörde, och hans vrede förgrymmade sig svårliga.
7 Ya ɗauki shanu biyu, ya yayyanka su gunduwa-gunduwa, ya aika da su ko’ina a ƙasar Isra’ila ta wurin manzanni cewa, “Duk wanda bai fita ya bi Shawulu da Sama’ila ba, haka za a yi da shanunsa.” Mutanen suka ji tsoron Ubangiji suka fita gaba ɗaya kamar mutum guda.
Och han tog ett par oxar, och styckade dem, och sände i alla Israels gränsor med bådskap, och lät säga: Den som icke utdrager efter Saul och Samuel, hans oxar skall man så göra. Så föll Herrans fruktan öfver folket, att de utdrogo såsom en man.
8 Mutanen Isra’ila sun kai dubu ɗari uku. Mutanen Yahuda kuma dubu talatin, sa’ad da Shawulu ya tara su a Bezek.
Och man räknade dem i Besek; och Israels barn voro tre resor hundradetusend män; och Juda barn tretiotusend.
9 Suka ce wa’yan aikan da suka zo, “Ku faɗa wa mutanen Yabesh Gileyad, ‘Gobe, kafin rana tă yi zafi, za ku sami ceto.’” Sa’ad da’yan aikan suka tafi, suka ba da saƙon nan ga mutanen Yabesh, sai suka farin ciki.
Och de sade till bådskapen, som komne voro: Säger de män i Jabes i Gilead: I morgon skolen I få hjelp, när solen är som hetast. Då desse bådskapen kommo, och förkunnade det de män i Jabes, vordo de glade.
10 Suka ce wa Ammonawa, “Gobe za mu miƙa wuya gare ku, ku kuma yi duk abin da kuka ga dama.”
Och de män i Jabes sade: I morgon vilje vi gå ut till eder, att I mågen göra oss allt det eder täckes.
11 Gari yana wayewa, sai Shawulu ya raba mutane kashi uku, a sa’a ta ƙarshe na daren sai suka fāɗa wa sansanin Ammonawa, suka kuma karkashe su har lokacin da rana ta yi zafi. Waɗanda suka kuɓuce kuwa suka warwatsu, har babu biyunsu da aka bari tare.
Den andra morgonen skickade Saul folket i tre hopar, och de kommo i lägret i morgonväktene, och slogo de Ammoniter allt intill dagen vardt som hetast. Och de som öfverblefvo, vordo så förskingrade, att icke två blefvo tillhopa.
12 Sai mutane suka ce wa Sama’ila, “Su wa suka ce, ‘Shawulu zai yi mulkinmu?’ A kawo mana su mu kashe.”
Då sade folket till Samuel: Hvar äro de, som sade: Skall Saul råda öfver oss? Låt de män komma här fram, att vi måge dräpa dem.
13 Shawulu ya ce, “Ba wanda zai mutu yau, gama Ubangiji ya kuɓutar da Isra’ila a wannan rana.”
Saul sade: På denna dagen skall ingen dö; ty Herren hafver i dag gjort salighet i Israel.
14 Sai Sama’ila ya ce wa mutane, “Ku zo mu tafi Gilgal, a can za a yi wankan sarauta.”
Samuel sade till folket: Kommer, låter oss gå till Gilgal, och der förnya Konungariket.
15 Don haka dukan mutane suka tafi Gilgal, suka tabbatar da Shawulu sarki a gaban Ubangiji. A can suka miƙa hadaya ta salama a gaban Ubangiji, Shawulu kuwa da dukan Isra’ila suka yi babban liyafa.
Så drog allt folket till Gilgal, och gjorde der Saul till Konung för Herranom i Gilgal, och offrade tackoffer inför Herranom. Och Saul med alla Israels män fröjdade sig der ganska storliga.