< 1 Sama’ila 11 >

1 Nahash mutumin Ammon ya haura ya kewaye Yabesh Gileyad da yaƙi. Dukan mutanen Yabesh suka ce masa, “Ka ƙulla amana da mu, mu kuwa za mu bauta maka.”
و ناحاش عمونی برآمده، در برابر یابیش جلعاد اردو زد، و جمیع اهل یابیش به ناحاش گفتند: «با ما عهد ببند و تو را بندگی خواهیم نمود.»۱
2 Amma Nahash ya ce, “Zan ƙulla amana da ku kawai a kan sharaɗin cewa zan ƙwaƙulo idon dama na kowannenku, ta haka za a kunyata Isra’ila.”
ناحاش عمونی به ایشان گفت: «به این شرط با شما عهد خواهم بست که چشمان راست جمیع شما کنده شود، و این را بر تمامی اسرائیل عار خواهم ساخت.»۲
3 Dattawan Yabesh suka ce masa, “Ka ba mu kwana bakwai don mu aika manzanni a dukan ƙasar Isra’ila idan ba mu sami wanda zai cece mu ba, za mu ba da kanmu gare ka.”
و مشایخ یابیش به وی گفتند: «ما را هفت روز مهلت بده تا رسولان به تمامی حدود اسرائیل بفرستیم، و اگر برای مارهاننده‌ای نباشد نزد تو بیرون خواهیم آمد.»۳
4 Da manzannin suka zo Gibeya garin Shawulu, suka gaya wa mutane wannan sharaɗin, suka yi kuka mai zafi.
پس رسولان به جبعه شاول آمده، این سخنان رابه گوش قوم رسانیدند، و تمامی قوم آواز خود رابلند کرده، گریستند.۴
5 A daidai wannan lokacin kuwa Shawulu yana dawowa daga gona tare da shanunsa na noma, sai ya ce, “Me ya faru, mutane suna kuka haka?” Sai suka faɗa masa abin da mutanen Yabesh suka faɗa musu.
و اینک شاول در عقب گاوان از صحرامی آمد، و شاول گفت: «قوم را چه شده است که می‌گریند؟» پس سخنان مردان یابیش را به او بازگفتند.۵
6 Da Shawulu ya ji, sa Ruhun Allah ya sauko a kansa da iko, ya husata ƙwarai.
و چون شاول این سخنان را شنید روح خدا بر وی مستولی گشته، خشمش به شدت افروخته شد.۶
7 Ya ɗauki shanu biyu, ya yayyanka su gunduwa-gunduwa, ya aika da su ko’ina a ƙasar Isra’ila ta wurin manzanni cewa, “Duk wanda bai fita ya bi Shawulu da Sama’ila ba, haka za a yi da shanunsa.” Mutanen suka ji tsoron Ubangiji suka fita gaba ɗaya kamar mutum guda.
پس یک جفت گاو را گرفته، آنهارا پاره پاره نمود و به‌دست قاصدان به تمامی حدود اسرائیل فرستاده، گفت: «هر‌که در عقب شاول و سموئیل بیرون نیاید، به گاوان او چنین کرده شود.» آنگاه ترس خداوند بر قوم افتاد که مثل مرد واحد بیرون آمدند.۷
8 Mutanen Isra’ila sun kai dubu ɗari uku. Mutanen Yahuda kuma dubu talatin, sa’ad da Shawulu ya tara su a Bezek.
و ایشان را در بازق شمرد و بنی‌اسرائیل سیصد هزار نفر و مردان یهودا سی هزار بودند.۸
9 Suka ce wa’yan aikan da suka zo, “Ku faɗa wa mutanen Yabesh Gileyad, ‘Gobe, kafin rana tă yi zafi, za ku sami ceto.’” Sa’ad da’yan aikan suka tafi, suka ba da saƙon nan ga mutanen Yabesh, sai suka farin ciki.
پس به رسولانی که آمده بودند گفتند: «به مردمان یابیش جلعاد چنین گویید: فردا وقتی که آفتاب گرم شود برای شماخلاصی خواهد شد.» و رسولان آمده، به اهل یابیش خبر دادند، پس ایشان شاد شدند.۹
10 Suka ce wa Ammonawa, “Gobe za mu miƙa wuya gare ku, ku kuma yi duk abin da kuka ga dama.”
ومردان یابیش گفتند: «فردا نزد شما بیرون خواهیم آمد تا هرچه در نظرتان پسند آید به ما بکنید.»۱۰
11 Gari yana wayewa, sai Shawulu ya raba mutane kashi uku, a sa’a ta ƙarshe na daren sai suka fāɗa wa sansanin Ammonawa, suka kuma karkashe su har lokacin da rana ta yi zafi. Waɗanda suka kuɓuce kuwa suka warwatsu, har babu biyunsu da aka bari tare.
و در فردای آن روز شاول قوم را به سه فرقه تقسیم نمود و ایشان در پاس صبح به میان لشکرگاه آمده، عمونیان را تا گرم شدن آفتاب می‌زدند، و باقی ماندگان پراکنده شدند به حدی که دو نفر از ایشان در یک جا نماندند.۱۱
12 Sai mutane suka ce wa Sama’ila, “Su wa suka ce, ‘Shawulu zai yi mulkinmu?’ A kawo mana su mu kashe.”
و قوم به سموئیل گفتند: «کیست که گفته است! آیا شاول بر ما سلطنت نماید؟ آن کسان رابیاورید تا ایشان را بکشیم.»۱۲
13 Shawulu ya ce, “Ba wanda zai mutu yau, gama Ubangiji ya kuɓutar da Isra’ila a wannan rana.”
اما شاول گفت: «کسی‌امروز کشته نخواهد شد زیرا که خداوندامروز در اسرائیل نجات به عمل آورده است.»۱۳
14 Sai Sama’ila ya ce wa mutane, “Ku zo mu tafi Gilgal, a can za a yi wankan sarauta.”
و سموئیل به قوم گفت: «بیایید تا به جلجال برویم و سلطنت را در آنجا از سر نو برقرار کنیم.»۱۴
15 Don haka dukan mutane suka tafi Gilgal, suka tabbatar da Shawulu sarki a gaban Ubangiji. A can suka miƙa hadaya ta salama a gaban Ubangiji, Shawulu kuwa da dukan Isra’ila suka yi babban liyafa.
پس تمامی قوم به جلجال رفتند، و آنجا درجلجال، شاول را به حضور خداوند پادشاه ساختند، و در آنجا ذبایح سلامتی به حضورخداوند ذبح نموده، شاول و تمامی مردمان اسرائیل در آنجا شادی عظیم نمودند.۱۵

< 1 Sama’ila 11 >