< 1 Sama’ila 11 >

1 Nahash mutumin Ammon ya haura ya kewaye Yabesh Gileyad da yaƙi. Dukan mutanen Yabesh suka ce masa, “Ka ƙulla amana da mu, mu kuwa za mu bauta maka.”
Så drog ammonitten Nahas op og kringsatte Jabes i Gilead, og alle Jabes' menn sa til Nahas: Gjør fred med oss, så vil vi tjene dig.
2 Amma Nahash ya ce, “Zan ƙulla amana da ku kawai a kan sharaɗin cewa zan ƙwaƙulo idon dama na kowannenku, ta haka za a kunyata Isra’ila.”
Men ammonitten Nahas svarte dem: På det vilkår vil jeg gjøre fred med eder at det høire øie stikkes ut på eder alle; den skjensel vil jeg legge på hele Israel.
3 Dattawan Yabesh suka ce masa, “Ka ba mu kwana bakwai don mu aika manzanni a dukan ƙasar Isra’ila idan ba mu sami wanda zai cece mu ba, za mu ba da kanmu gare ka.”
Da sa Jabes eldste til ham: Gi oss frist i syv dager, så vi kan sende bud rundt om i hele Israels land! Er det da ingen som hjelper oss, så vil vi overgi oss til dig.
4 Da manzannin suka zo Gibeya garin Shawulu, suka gaya wa mutane wannan sharaɗin, suka yi kuka mai zafi.
Da sendebudene kom til Sauls Gibea og bar frem sitt ærend for folket, brast alt folket i gråt.
5 A daidai wannan lokacin kuwa Shawulu yana dawowa daga gona tare da shanunsa na noma, sai ya ce, “Me ya faru, mutane suna kuka haka?” Sai suka faɗa masa abin da mutanen Yabesh suka faɗa musu.
I samme stund kom Saul gående hjem fra marken bakefter sine okser. Og Saul sa: Hvad er det i veien med folket siden de gråter? Og de fortalte ham hvad mennene fra Jabes hadde sagt.
6 Da Shawulu ya ji, sa Ruhun Allah ya sauko a kansa da iko, ya husata ƙwarai.
Da Saul hørte dette, kom Guds Ånd over ham, og hans vrede optendtes høilig.
7 Ya ɗauki shanu biyu, ya yayyanka su gunduwa-gunduwa, ya aika da su ko’ina a ƙasar Isra’ila ta wurin manzanni cewa, “Duk wanda bai fita ya bi Shawulu da Sama’ila ba, haka za a yi da shanunsa.” Mutanen suka ji tsoron Ubangiji suka fita gaba ɗaya kamar mutum guda.
Og han tok et par okser og hugg dem i stykker og sendte stykkene om i hele Israels land med sendebudene og lot si: Den som ikke drar ut efter Saul og Samuel, med hans okser skal det gjøres likedan. Da falt det en redsel fra Herren over folket, og de drog ut som en mann.
8 Mutanen Isra’ila sun kai dubu ɗari uku. Mutanen Yahuda kuma dubu talatin, sa’ad da Shawulu ya tara su a Bezek.
Han mønstret dem i Besek, og Israels barn var tre hundre tusen, og Judas menn tretti tusen.
9 Suka ce wa’yan aikan da suka zo, “Ku faɗa wa mutanen Yabesh Gileyad, ‘Gobe, kafin rana tă yi zafi, za ku sami ceto.’” Sa’ad da’yan aikan suka tafi, suka ba da saƙon nan ga mutanen Yabesh, sai suka farin ciki.
Og de sa til sendebudene som var kommet: Så skal I si til mennene i Jabes i Gilead: Imorgen, når solen brenner hett, skal det komme hjelp til eder. Da sendebudene kom og meldte dette til mennene i Jabes, blev de glade,
10 Suka ce wa Ammonawa, “Gobe za mu miƙa wuya gare ku, ku kuma yi duk abin da kuka ga dama.”
og de sa til ammonittene: Imorgen vil vi overgi oss til eder, så kan I gjøre med oss aldeles som I finner for godt!
11 Gari yana wayewa, sai Shawulu ya raba mutane kashi uku, a sa’a ta ƙarshe na daren sai suka fāɗa wa sansanin Ammonawa, suka kuma karkashe su har lokacin da rana ta yi zafi. Waɗanda suka kuɓuce kuwa suka warwatsu, har babu biyunsu da aka bari tare.
Dagen efter stilte Saul folket op i tre hoper, og i morgenvakten trengte de midt inn i leiren og hugg ammonittene ned, til dagen blev het; og de som blev tilbake, spredtes, så det ikke blev to sammen tilbake av dem.
12 Sai mutane suka ce wa Sama’ila, “Su wa suka ce, ‘Shawulu zai yi mulkinmu?’ A kawo mana su mu kashe.”
Da sa folket til Samuel: Hvem var det som sa: Skal Saul være konge over oss? La oss få fatt i disse menn, så vi kan drepe dem.
13 Shawulu ya ce, “Ba wanda zai mutu yau, gama Ubangiji ya kuɓutar da Isra’ila a wannan rana.”
Da sa Saul: På denne dag skal ingen drepes; for idag har Gud hjulpet Israel til seier.
14 Sai Sama’ila ya ce wa mutane, “Ku zo mu tafi Gilgal, a can za a yi wankan sarauta.”
Og Samuel sa til folket: Kom, la oss gå til Gilgal for å stadfeste kongedømmet der!
15 Don haka dukan mutane suka tafi Gilgal, suka tabbatar da Shawulu sarki a gaban Ubangiji. A can suka miƙa hadaya ta salama a gaban Ubangiji, Shawulu kuwa da dukan Isra’ila suka yi babban liyafa.
Da gikk alt folket til Gilgal, og der i Gilgal gjorde de Saul til konge for Herrens åsyn; og de ofret der takkoffer for Herrens åsyn. Og Saul og alle Israels menn gledet sig der storlig.

< 1 Sama’ila 11 >