< 1 Sama’ila 11 >

1 Nahash mutumin Ammon ya haura ya kewaye Yabesh Gileyad da yaƙi. Dukan mutanen Yabesh suka ce masa, “Ka ƙulla amana da mu, mu kuwa za mu bauta maka.”
Or Nahas Hammonite monta, et se campa contre Jabés de Galaad. Et tous ceux de Jabés dirent à Nahas: Traite alliance avec nous, et nous te servirons.
2 Amma Nahash ya ce, “Zan ƙulla amana da ku kawai a kan sharaɗin cewa zan ƙwaƙulo idon dama na kowannenku, ta haka za a kunyata Isra’ila.”
Mais Nahas Hammonite leur répondit: Je traiterai [alliance] avec vous à cette condition, que je vous crève à tous l'œil droit, et que je mette cela pour opprobre sur tout Israël.
3 Dattawan Yabesh suka ce masa, “Ka ba mu kwana bakwai don mu aika manzanni a dukan ƙasar Isra’ila idan ba mu sami wanda zai cece mu ba, za mu ba da kanmu gare ka.”
Et les Anciens de Jabés lui dirent: Donne-nous sept jours de trêve, et nous enverrons des messagers par tous les quartiers d'Israël, et s'il n'y a personne qui nous délivre, nous nous rendrons à toi.
4 Da manzannin suka zo Gibeya garin Shawulu, suka gaya wa mutane wannan sharaɗin, suka yi kuka mai zafi.
Les messagers donc vinrent en Guib-ha-Saül, et dirent ces paroles devant le peuple; et tout le peuple éleva sa voix, et pleura.
5 A daidai wannan lokacin kuwa Shawulu yana dawowa daga gona tare da shanunsa na noma, sai ya ce, “Me ya faru, mutane suna kuka haka?” Sai suka faɗa masa abin da mutanen Yabesh suka faɗa musu.
Et voici Saül revenait des champs derrière ses bœufs; et il dit: Qu'est-ce qu'a ce peuple pour pleurer ainsi? Et on lui récita ce qu'avaient dit ceux de Jabés.
6 Da Shawulu ya ji, sa Ruhun Allah ya sauko a kansa da iko, ya husata ƙwarai.
Or l'Esprit de Dieu saisit Saül, lorsqu'il entendit ces paroles, et il fut embrasé de colère.
7 Ya ɗauki shanu biyu, ya yayyanka su gunduwa-gunduwa, ya aika da su ko’ina a ƙasar Isra’ila ta wurin manzanni cewa, “Duk wanda bai fita ya bi Shawulu da Sama’ila ba, haka za a yi da shanunsa.” Mutanen suka ji tsoron Ubangiji suka fita gaba ɗaya kamar mutum guda.
Et il prit une couple de bœufs, et les coupa en morceaux, et en envoya dans tous les quartiers d'Israël par des messagers exprès, en disant: On en fera de même aux bœufs de tous ceux qui ne sortiront point, et qui ne suivront point Saül et Samuel. Et la frayeur de l'Eternel tomba sur le peuple, et ils sortirent comme si ce n'eût été qu'un seul homme.
8 Mutanen Isra’ila sun kai dubu ɗari uku. Mutanen Yahuda kuma dubu talatin, sa’ad da Shawulu ya tara su a Bezek.
Et [Saül] les dénombra en Bézec; et il y eut trois cent mille hommes des enfants d'Israël, et trente mille des gens de Juda.
9 Suka ce wa’yan aikan da suka zo, “Ku faɗa wa mutanen Yabesh Gileyad, ‘Gobe, kafin rana tă yi zafi, za ku sami ceto.’” Sa’ad da’yan aikan suka tafi, suka ba da saƙon nan ga mutanen Yabesh, sai suka farin ciki.
Après ils dirent aux messagers qui étaient venus: Vous parlerez ainsi à ceux de Jabés de Galaad: Vous serez délivrés demain quand le soleil sera en sa force. Les messagers donc s'en revinrent, et rapportèrent cela à ceux de Jabés, qui [s'en] réjouirent.
10 Suka ce wa Ammonawa, “Gobe za mu miƙa wuya gare ku, ku kuma yi duk abin da kuka ga dama.”
Et ceux de Jabés dirent [aux Hammonites]: Demain nous nous rendrons à vous, et vous nous ferez tout ce qui vous semblera bon.
11 Gari yana wayewa, sai Shawulu ya raba mutane kashi uku, a sa’a ta ƙarshe na daren sai suka fāɗa wa sansanin Ammonawa, suka kuma karkashe su har lokacin da rana ta yi zafi. Waɗanda suka kuɓuce kuwa suka warwatsu, har babu biyunsu da aka bari tare.
Et dès le lendemain Saül mit le peuple en trois bandes, et ils entrèrent dans le camp sur la veille du matin, et ils frappèrent les Hammonites jusques vers la chaleur du jour; et ceux qui demeurèrent de reste furent tellement dispersés çà et là, qu'il n'en demeura pas deux ensemble.
12 Sai mutane suka ce wa Sama’ila, “Su wa suka ce, ‘Shawulu zai yi mulkinmu?’ A kawo mana su mu kashe.”
Et le peuple dit à Samuel: Qui est-ce qui dit: Saül régnera-t-il sur nous? Donnez-nous ces hommes-là, et nous les ferons mourir.
13 Shawulu ya ce, “Ba wanda zai mutu yau, gama Ubangiji ya kuɓutar da Isra’ila a wannan rana.”
Alors Saül dit: On ne fera mourir personne en ce jour, parce que l'Eternel a délivré aujourd'hui Israël.
14 Sai Sama’ila ya ce wa mutane, “Ku zo mu tafi Gilgal, a can za a yi wankan sarauta.”
Et Samuel dit au peuple: Venez, et allons à Guilgal, et nous y renouvellerons la Royauté.
15 Don haka dukan mutane suka tafi Gilgal, suka tabbatar da Shawulu sarki a gaban Ubangiji. A can suka miƙa hadaya ta salama a gaban Ubangiji, Shawulu kuwa da dukan Isra’ila suka yi babban liyafa.
Et tout le peuple s'en alla à Guilgal; et là ils établirent Saül pour Roi devant l'Eternel à Guilgal, et ils offrirent là des sacrifices de prospérité devant l'Eternel; et là, Saül et tous ceux d'Israël se réjouirent beaucoup.

< 1 Sama’ila 11 >