< 1 Sama’ila 11 >
1 Nahash mutumin Ammon ya haura ya kewaye Yabesh Gileyad da yaƙi. Dukan mutanen Yabesh suka ce masa, “Ka ƙulla amana da mu, mu kuwa za mu bauta maka.”
And it came to pass about a month after this that Naas, the Ammonite came up, and began to fight against Jabes Galaad. And all the men of Jabes said to Naas: Make a covenant with us, and we will serve thee.
2 Amma Nahash ya ce, “Zan ƙulla amana da ku kawai a kan sharaɗin cewa zan ƙwaƙulo idon dama na kowannenku, ta haka za a kunyata Isra’ila.”
And Naas the Ammonite answered them: On this condition will I make a covenant with you, that I may pluck out all your right eyes, and make you a reproach in all Israel.
3 Dattawan Yabesh suka ce masa, “Ka ba mu kwana bakwai don mu aika manzanni a dukan ƙasar Isra’ila idan ba mu sami wanda zai cece mu ba, za mu ba da kanmu gare ka.”
And the ancients of Jabes said to him: Allow us seven days, that we may send messengers to all the coasts of Israel: and if there be no one to defend us, we will come out to thee.
4 Da manzannin suka zo Gibeya garin Shawulu, suka gaya wa mutane wannan sharaɗin, suka yi kuka mai zafi.
The messengers therefore came to Gabaa of Saul: and they spoke these words in the hearing of the people: and all the people lifted up their voices, and wept.
5 A daidai wannan lokacin kuwa Shawulu yana dawowa daga gona tare da shanunsa na noma, sai ya ce, “Me ya faru, mutane suna kuka haka?” Sai suka faɗa masa abin da mutanen Yabesh suka faɗa musu.
And behold Saul came, following oxen out of the field, and he said: What aileth the people that they weep? And they told him the words of the men of Jabes.
6 Da Shawulu ya ji, sa Ruhun Allah ya sauko a kansa da iko, ya husata ƙwarai.
And the spirit of the Lord came upon Saul, when he had heard these words, and his anger was exceedingly kindled.
7 Ya ɗauki shanu biyu, ya yayyanka su gunduwa-gunduwa, ya aika da su ko’ina a ƙasar Isra’ila ta wurin manzanni cewa, “Duk wanda bai fita ya bi Shawulu da Sama’ila ba, haka za a yi da shanunsa.” Mutanen suka ji tsoron Ubangiji suka fita gaba ɗaya kamar mutum guda.
And taking both the oxen, he cut them in pieces, and sent them into all the coasts of Israel by messengers, saying: Whosoever shall not come forth, and follow Saul and Samuel, so shall it be done to his oxen. And the fear of the Lord fell upon the people, and they went out as one man.
8 Mutanen Isra’ila sun kai dubu ɗari uku. Mutanen Yahuda kuma dubu talatin, sa’ad da Shawulu ya tara su a Bezek.
And he numbered them in Bezec: and there were of the children of Israel three hundred thousand: and of the men of Juda thirty thousand.
9 Suka ce wa’yan aikan da suka zo, “Ku faɗa wa mutanen Yabesh Gileyad, ‘Gobe, kafin rana tă yi zafi, za ku sami ceto.’” Sa’ad da’yan aikan suka tafi, suka ba da saƙon nan ga mutanen Yabesh, sai suka farin ciki.
And they said to the messengers that came: Thus shall you say to the men of Jabes Galaad: Tomorrow, when the sun shall be hot, you shall have relief. The messengers therefore came, and told the men of Jabes: and they were glad.
10 Suka ce wa Ammonawa, “Gobe za mu miƙa wuya gare ku, ku kuma yi duk abin da kuka ga dama.”
And they said: In the morning we will come out to you: and you shall do what you please with us.
11 Gari yana wayewa, sai Shawulu ya raba mutane kashi uku, a sa’a ta ƙarshe na daren sai suka fāɗa wa sansanin Ammonawa, suka kuma karkashe su har lokacin da rana ta yi zafi. Waɗanda suka kuɓuce kuwa suka warwatsu, har babu biyunsu da aka bari tare.
And it came to pass, when the morrow was come that Saul put the people in three companies: and he came into the midst of the camp in the morning watch, and he slew the Ammonites until the day grew hot, and the rest were scattered, so that two of them were not left together.
12 Sai mutane suka ce wa Sama’ila, “Su wa suka ce, ‘Shawulu zai yi mulkinmu?’ A kawo mana su mu kashe.”
And the people said to Samuel: Who is he that said: Shall Saul reign over us? Bring the men and we will kill them.
13 Shawulu ya ce, “Ba wanda zai mutu yau, gama Ubangiji ya kuɓutar da Isra’ila a wannan rana.”
And Saul said: No man shall be killed this day, because the Lord this day hath wrought salvation in Israel:
14 Sai Sama’ila ya ce wa mutane, “Ku zo mu tafi Gilgal, a can za a yi wankan sarauta.”
And Samuel said to the people: Come and let us go to Galgal, and let us renew the kingdom there.
15 Don haka dukan mutane suka tafi Gilgal, suka tabbatar da Shawulu sarki a gaban Ubangiji. A can suka miƙa hadaya ta salama a gaban Ubangiji, Shawulu kuwa da dukan Isra’ila suka yi babban liyafa.
And all the people went to Galgal, and there they made Saul king before the Lord in Galgal, and they sacrificed there victims of peace before the Lord. And there Saul and all the men of Israel rejoiced exceedingly.