< 1 Sama’ila 11 >

1 Nahash mutumin Ammon ya haura ya kewaye Yabesh Gileyad da yaƙi. Dukan mutanen Yabesh suka ce masa, “Ka ƙulla amana da mu, mu kuwa za mu bauta maka.”
And, about a month afterward, it happened that Nahash the Ammonite ascended and began to fight against Jabesh Gilead. And all the men of Jabesh said to Nahash, “Consider a pact with us, and we will serve you.”
2 Amma Nahash ya ce, “Zan ƙulla amana da ku kawai a kan sharaɗin cewa zan ƙwaƙulo idon dama na kowannenku, ta haka za a kunyata Isra’ila.”
And Nahash the Ammonite responded to them, “With this will I strike a pact with you: if I may pluck out all your right eyes, and set you as a disgrace against all of Israel.”
3 Dattawan Yabesh suka ce masa, “Ka ba mu kwana bakwai don mu aika manzanni a dukan ƙasar Isra’ila idan ba mu sami wanda zai cece mu ba, za mu ba da kanmu gare ka.”
And the elders of Jabesh said to him: “Grant to us seven days, so that we may send messengers to all the borders of Israel. And if there is no one who may defend us, we will go out to you.”
4 Da manzannin suka zo Gibeya garin Shawulu, suka gaya wa mutane wannan sharaɗin, suka yi kuka mai zafi.
Therefore, the messengers arrived at Gibeah of Saul. And they spoke these words in the hearing of the people. And all the people lifted up their voice and wept.
5 A daidai wannan lokacin kuwa Shawulu yana dawowa daga gona tare da shanunsa na noma, sai ya ce, “Me ya faru, mutane suna kuka haka?” Sai suka faɗa masa abin da mutanen Yabesh suka faɗa musu.
And behold, Saul arrived, following oxen from the field. And he said, “What has happened to the people that they would weep?” And they explained to him the words of the men from Jabesh.
6 Da Shawulu ya ji, sa Ruhun Allah ya sauko a kansa da iko, ya husata ƙwarai.
And the Spirit of the Lord rose up within Saul when he had heard these words, and his fury was enraged exceedingly.
7 Ya ɗauki shanu biyu, ya yayyanka su gunduwa-gunduwa, ya aika da su ko’ina a ƙasar Isra’ila ta wurin manzanni cewa, “Duk wanda bai fita ya bi Shawulu da Sama’ila ba, haka za a yi da shanunsa.” Mutanen suka ji tsoron Ubangiji suka fita gaba ɗaya kamar mutum guda.
And taking both the oxen, he cut them into pieces, and he sent them into all the borders of Israel, by the hands of messengers, saying, “Whoever will not go out and follow Saul and Samuel, so shall it be done to his oxen.” Therefore, the fear of the Lord entered into the people, and they went out like one man.
8 Mutanen Isra’ila sun kai dubu ɗari uku. Mutanen Yahuda kuma dubu talatin, sa’ad da Shawulu ya tara su a Bezek.
And he took a census of them at Bezek. And there were three hundred thousand of the sons of Israel. And there were thirty thousand of the men of Judah.
9 Suka ce wa’yan aikan da suka zo, “Ku faɗa wa mutanen Yabesh Gileyad, ‘Gobe, kafin rana tă yi zafi, za ku sami ceto.’” Sa’ad da’yan aikan suka tafi, suka ba da saƙon nan ga mutanen Yabesh, sai suka farin ciki.
And they said to the messengers who had arrived: “So shall you say to the men who are of Jabesh Gilead: ‘Tomorrow, when the sun will be hot, you shall have salvation.’” Therefore, the messengers went and announced it to the men of Jabesh, who became joyful.
10 Suka ce wa Ammonawa, “Gobe za mu miƙa wuya gare ku, ku kuma yi duk abin da kuka ga dama.”
And they said, “In the morning, we will go out to you. And you may do whatever you please with us.”
11 Gari yana wayewa, sai Shawulu ya raba mutane kashi uku, a sa’a ta ƙarshe na daren sai suka fāɗa wa sansanin Ammonawa, suka kuma karkashe su har lokacin da rana ta yi zafi. Waɗanda suka kuɓuce kuwa suka warwatsu, har babu biyunsu da aka bari tare.
And it happened that, when the next day had arrived, Saul arranged the people into three parts. And he entered into the middle of the camp at the early morning watch, and he struck down the Ammonites until the day grew hot. Then the remainder were dispersed, so much so that not even two of them were left together.
12 Sai mutane suka ce wa Sama’ila, “Su wa suka ce, ‘Shawulu zai yi mulkinmu?’ A kawo mana su mu kashe.”
And the people said to Samuel: “Who is the one who said, ‘Should Saul reign over us?’ Present the men, and we will put them to death.”
13 Shawulu ya ce, “Ba wanda zai mutu yau, gama Ubangiji ya kuɓutar da Isra’ila a wannan rana.”
And Saul said: “No one shall be killed on this day. For today the Lord has accomplished salvation in Israel.”
14 Sai Sama’ila ya ce wa mutane, “Ku zo mu tafi Gilgal, a can za a yi wankan sarauta.”
Then Samuel said to the people, “Come, and let us go to Gilgal, and let us renew the kingdom there.”
15 Don haka dukan mutane suka tafi Gilgal, suka tabbatar da Shawulu sarki a gaban Ubangiji. A can suka miƙa hadaya ta salama a gaban Ubangiji, Shawulu kuwa da dukan Isra’ila suka yi babban liyafa.
And all the people traveled to Gilgal. And there they made Saul king, in the sight of the Lord at Gilgal. And there they immolated victims of peace, before the Lord. And there Saul and all the men of Israel rejoiced exceedingly.

< 1 Sama’ila 11 >