< 1 Sama’ila 10 >

1 Sai Sama’ila ya ɗauki’yar kwalabar mai, ya zuba man ɗin wa Shawulu a kansa, ya yi masa sumba yana cewa, “Ubangiji ya keɓe ka shugaba bisa gādonsa.
Or, Samuel prit le petit vase d’huile et le répandit sur la tête de Saül, puis il le baisa et dit: Voilà que le Seigneur t’a oint comme prince sur son héritage et tu délivreras son peuple des mains de ses ennemis, qui sont autour de lui. Et ceci sera pour toi le signe que Dieu t’a oint comme prince:
2 Sa’ad da ka rabu da ni yau, za ka sadu da mutum biyu kusa da kabarin Rahila a Zelza, a yankin Benyamin. Za su ce maka, ‘An sami jakunan da ka fita nema, yanzu haka mahaifinka ya bar damuwa kan jakunan ya koma damuwa a kanka, yana cewa, yaya zan gan ɗana?’
Lorsque tu t’en seras allé aujourd’hui d’auprès de moi, tu trouveras deux hommes près du sépulcre de Rachel, dans les confins de Benjamin, au midi, et ils te diront: Elles ont été trouvées les ânesses que tu étais allé rechercher, mais, les ânesses, laissées de côté, ton père est inquiet sur vous, et il dit: Que ferai-je au sujet de mon fils?
3 “Sa’an nan za ka ci gaba daga nan sai ka kai wajen babban itace na Tabor. Waɗansu mutum uku za su sadu da kai a hanyarsu zuwa wurin yin wa Allah sujada a Betel. Ɗaya yana ɗauke da’yan awaki uku, ɗaya yana ɗauke da burodi uku, ɗayan kuma yana ɗauke da salkar ruwan inabi.
Et lorsque tu t’en seras allé de là, que tu auras passé outre, et que tu seras venu au chêne de Thabor, là te rencontreront trois hommes, montant vers Dieu à Béthel: l’un portant trois chevreaux, l’autre trois miches de pain, et l’autre portant une cruche de vin.
4 Za su gaishe ka, su ba ka burodi biyu, kai kuwa sai ka karɓa.
Et lorsqu’ils t’auront salué, ils te donneront deux pains, et tu les recevras de leur main.
5 “Bayan wannan, za ka tafi Gebiya ta Allah, inda sansanin Filistiyawa yake. Kana shiga garin, za ka sadu da jerin gwanon annabawa suna gangarowa daga tudu, ana kaɗa garaya, ana bugan ganguna, ana hura sarewa, ana kuma bugan molo, a gabansu, su kuma za su yi ta annabci.
Après cela tu viendras sur la colline de Dieu, où est une garnison de Philistins; et lorsque tu seras entré là dans la ville, tu auras à ta rencontre une troupe de prophètes, descendant du haut lieu, et précédés de psaltérions, de tambours, de flûtes et de harpes, et les prophètes eux-mêmes prophétisant.
6 Ruhun Ubangiji zai sauko a kanka da iko, za ka kuma yi annabci tare da su. Za a canja ka ka zama dabam.
Et l’esprit du Seigneur se saisira de toi, et tu prophétiseras avec eux, et tu seras changé en un autre homme.
7 Da zarar waɗannan alamu sun cika, sai ka aikata duk abin da kana iya yi gama Allah yana tare da kai.
Quand donc tous ces signes te seront arrivés, fais tout ce que ta main rencontrera, parce que le Seigneur est avec toi.
8 “Ka sha gabana zuwa Gilgal. Lalle zan gangara wurinka domin in miƙa hadaya ta ƙonawa da hadayu na salama. Sai ka jira ni kwana bakwai sai na zo wurinka na kuma gaya maka abin da za ka yi.”
Et tu descendras avant moi à Galgala (car moi-même je descendrai vers toi), afin que tu offres une oblation, et que tu immoles des victimes pacifiques. Tu attendras pendant sept jours, jusqu’à ce que j’arrive près de toi, et je te montrerai ce que tu dois faire.
9 Da Shawulu ya juya zai bar Sama’ila, sai Allah ya canja wa Shawulu zuciya, alamun nan kuwa suka cika a ranar.
C’est pourquoi, lorsqu’il eut détourné son épaule, pour s’en aller d’auprès de Samuel, Dieu changea son cœur en un autre; et tous ces signes arrivèrent en ce jour-là.
10 Da suka iso Gibeya, jerin gwanon annabawa suka sadu da shi Ruhun Allah kuma ya sauko a kansa da iko, sai ya shiga yin annabci tare da su.
Et ils arrivèrent à la susdite colline, et voilà une bande de prophètes à sa rencontre; alors l’esprit du Seigneur se saisit de lui, et il prophétisa au milieu d’eux.
11 Sa’ad da dukan waɗanda suka san shi a dā suka gan shi yana annabci tare da annabawa, sai suka tambayi juna, suka ce, “Me ya faru da ɗan Kish? Shawulu ma yana cikin annabawa ne?”
Or tous ceux qui l’avaient connu hier et avant-hier, voyant qu’il était avec des prophètes, et qu’il prophétisait, s’entredirent: Qu’est-ce qui est arrivé au fils de Cis? est-ce que Saül est aussi du nombre des prophètes?
12 Wani mutumin da yake zama a can ya ce, “Wane ne kuma mahaifinsu?” Ta haka sai wannan ya zama karin magana cewa, “Shawulu ma yana cikin annabawa?”
Et l’un répondit à l’autre, disant: Et qui est leur père? C’est pourquoi est passé en proverbe: Est-ce que Saül est aussi parmi les prophètes?
13 Bayan da Shawulu ya gama annabci sai ya haura ya tafi tudu.
Mais il cessa de prophétiser, et il vint au haut lieu.
14 Sai ɗan’uwan mahaifin Shawulu ya tambaye shi da baransa ya ce, “Ina kuka je?” Shawulu ya ce, “Mun tafi neman jakuna, amma da ba mu same su ba sai muka tafi wurin Sama’ila.”
Et l’oncle de Saül lui dit, à lui et à son serviteur: Où êtes-vous allés? Ils répondirent: Chercher les ânesses; et comme nous ne les avons pas trouvées, nous sommes venus vers Samuel.
15 Ɗan’uwan mahaifin Shawulu ya ce, “Faɗa mini abin da Sama’ila ya ce maka.”
Son oncle lui dit encore: Fais-moi connaître ce que t’a dit Samuel.
16 Shawulu ya ce, “Ya tabbatar mana cewa an riga an sami jakuna.” Amma bai gaya wa ɗan’uwan mahaifinsa abin da Sama’ila ya ce game da sarauta ba.
Et Saül répondit à son oncle: Il nous a appris que les ânesses avaient été trouvées. Mais il ne lui découvrit rien du discours sur la royauté, que lui avait tenu Samuel.
17 Sama’ila ta tattara mutanen Isra’ila a gaban Ubangiji a Mizfa
Après cela, Samuel convoqua tout le peuple auprès du Seigneur à Maspha,
18 ya ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na fito da Isra’ila daga Masar, na kuma cece ku daga hannun Masarawa da dukan mulkokin da suka wahalshe ku.’
Et il dit aux enfants d’Israël: Voici ce que dit le Seigneur Dieu d’Israël: C’est moi qui ai retiré Israël de l’Égypte, et qui vous ai délivrés de la main des Egyptiens, et de la main de tous les rois qui vous affligeaient.
19 Amma yanzu kun ƙi Allahnku wanda ya cece ku daga dukan masifu da wahaloli. Kuka ce, ‘Sam, a naɗa mana sarki.’ Saboda haka yanzu sai ku zo gaban Ubangiji kabila-kabila da iyali-iyali.”
Mais vous aujourd’hui, vous avez rejeté votre Dieu, qui seul vous a sauvés de tous vos maux et de toutes vos tribulations, et vous avez dit: Point du tout; mais établissez un roi sur nous. Maintenant donc, tenez-vous devant le Seigneur, selon vos tribus, et selon vos familles.
20 Sa’ad da Sama’ila ya kawo dukan Isra’ila gaba, kabila-kabila, sai aka zaɓi kabilar Benyamin ta wurin jefa ƙuri’a.
Et Samuel fit approcher toutes les tribus d’Israël, et le sort tomba sur la tribu de Benjamin.
21 Sai ya kawo kabilar Benyamin gaba, iyali-iyali, aka zaɓi iyalin Matri. A ƙarshe aka zaɓi Shawulu ɗan Kish. Amma da aka neme shi sai ba a same shi ba.
Il fit donc approcher la tribu de Benjamin et ses familles, et la famille de Métri tomba au sort, et le sort arriva jusqu’à Saül, fils de Cis. Ils le cherchèrent donc, mais il ne se trouva pas.
22 Suka ƙara nemi bayani daga Ubangiji suka ce, “Mutumin ya zo nan kuwa?” Ubangiji ya ce, “I, ga shi can, ya ɓuya cikin kayayyaki.”
Et ils consultèrent après cela le Seigneur, pour savoir s’il devait venir en ce lieu-là. Et le Seigneur répondit: Voilà qu’il est caché dans sa maison.
23 Suka ruga suka kawo shi. Da ya tsaya cikin mutane, sai ya fi kowa tsayi.
C’est pourquoi ils coururent, et ils l’enlevèrent de là; et il se tint debout au milieu du peuple et il se trouva plus grand que tout le peuple de l’épaule et de la tête.
24 Sama’ila ya ce wa dukan mutane, “Kun ga wanda Ubangiji ya zaɓa ko? Ba wani kamar sa a cikin dukan mutane.” Sai mutane suka tā da murya suka ce, “Ran sarki yă daɗe.”
Et Samuel dit à tout le peuple: Certes, vous voyez quel est celui qu’a choisi le Seigneur, et qu’il n’y en a point de semblable dans tout le peuple. Alors tout le peuple s’écria et dit: Vive le roi!
25 Sama’ila kuwa ya bayyana wa mutane ƙa’idodin sarauta. Ya rubuta su cikin littafi ya ajiye a gaban Ubangiji. Sa’an nan ya sallame mutane, kowa ya koma gidansa.
Or, Samuel dit au peuple la loi du royaume, et il l’écrivit dans le livre, et il le déposa devant le Seigneur, et Samuel renvoya tout le peuple chacun dans sa maison.
26 Shawulu ma ya tafi gidansa a Gibeya tare da waɗansu jarumawan da Allah ya taɓa zuciyarsu.
Mais Saül aussi s’en alla dans sa maison à Gabaa; et s’en alla avec lui la partie de l’armée dont Dieu avait touché le cœur.
27 Amma waɗansu’yan iska suka ce, “Yaya wannan mutum zai iya cetonmu?” Suka rena shi suka ƙi su kawo masa kyautai. Amma Shawulu bai ce uffam ba.
Au contraire, les enfants de Bélial dirent: Est-ce qu’il pourra nous sauver, celui-là? Et ils le méprisèrent, et ils ne lui apportèrent point de présents; mais Saül feignait de ne pas entendre.

< 1 Sama’ila 10 >