< 1 Sama’ila 10 >

1 Sai Sama’ila ya ɗauki’yar kwalabar mai, ya zuba man ɗin wa Shawulu a kansa, ya yi masa sumba yana cewa, “Ubangiji ya keɓe ka shugaba bisa gādonsa.
Then Samuel took a small jar of olive oil and poured [some of] it on Saul’s head. Then he kissed Saul [on the cheek], and told him, “I am doing this because Yahweh has chosen you to be the leader of his Israeli people.
2 Sa’ad da ka rabu da ni yau, za ka sadu da mutum biyu kusa da kabarin Rahila a Zelza, a yankin Benyamin. Za su ce maka, ‘An sami jakunan da ka fita nema, yanzu haka mahaifinka ya bar damuwa kan jakunan ya koma damuwa a kanka, yana cewa, yaya zan gan ɗana?’
[And this will prove it to you]: When you leave me today, when you arrive near Rachel’s tomb at Zelzah, in the area where the descendants of Benjamin live, you will meet two men. They will say to you, ‘The donkeys have been found, but now your father is worrying about you, and he is asking people, “Have you seen my son?’”
3 “Sa’an nan za ka ci gaba daga nan sai ka kai wajen babban itace na Tabor. Waɗansu mutum uku za su sadu da kai a hanyarsu zuwa wurin yin wa Allah sujada a Betel. Ɗaya yana ɗauke da’yan awaki uku, ɗaya yana ɗauke da burodi uku, ɗayan kuma yana ɗauke da salkar ruwan inabi.
When you arrive at the [large] oak tree at Tabor [town], you will see three men coming toward you. They will be on their way to [worship] God at Bethel [town]. One of them will be leading three young goats, one will be carrying three loaves of bread, and one will be carrying a container of wine.
4 Za su gaishe ka, su ba ka burodi biyu, kai kuwa sai ka karɓa.
They will greet you, and they will offer you two of the loaves of bread. Accept them.
5 “Bayan wannan, za ka tafi Gebiya ta Allah, inda sansanin Filistiyawa yake. Kana shiga garin, za ka sadu da jerin gwanon annabawa suna gangarowa daga tudu, ana kaɗa garaya, ana bugan ganguna, ana hura sarewa, ana kuma bugan molo, a gabansu, su kuma za su yi ta annabci.
When you arrive at the hill [where people worship] God near Gibeah [town], where there is the camp where the Philistine soldiers stay, you will meet a group of prophets who will be coming down from the altar on top of the hill. There will be people in front of them who will be playing [various musical instruments]: a harp, a tambourine, a flute, and a lyre. And all of them will be speaking messages that come directly from God.
6 Ruhun Ubangiji zai sauko a kanka da iko, za ka kuma yi annabci tare da su. Za a canja ka ka zama dabam.
At that time the Spirit of Yahweh will come upon you, and you also will speak messages that come directly from God. (You will be changed/The Spirit of Yahweh will change you), so that you will become like a different person.
7 Da zarar waɗannan alamu sun cika, sai ka aikata duk abin da kana iya yi gama Allah yana tare da kai.
After those things occur, do whatever you think is right to do, and God will (be with/help) you.
8 “Ka sha gabana zuwa Gilgal. Lalle zan gangara wurinka domin in miƙa hadaya ta ƙonawa da hadayu na salama. Sai ka jira ni kwana bakwai sai na zo wurinka na kuma gaya maka abin da za ka yi.”
Then go ahead of me, down to Gilgal [city], and wait for me there, for seven days. Then I will join you there, to burn sacrifices and offer other sacrifices to enable you to maintain fellowship with God. When I arrive there, I will tell you what [other] things you should do.”
9 Da Shawulu ya juya zai bar Sama’ila, sai Allah ya canja wa Shawulu zuciya, alamun nan kuwa suka cika a ranar.
As Saul started to leave there, God changed Saul’s inner being. And all the things that Samuel had predicted happened on that day.
10 Da suka iso Gibeya, jerin gwanon annabawa suka sadu da shi Ruhun Allah kuma ya sauko a kansa da iko, sai ya shiga yin annabci tare da su.
When Saul and his servant arrived at Gibeah, they saw some prophets who were [speaking messages that came directly from God. As the prophets were] approaching Saul and his servant, God’s Spirit came upon Saul powerfully, and he also began to speak messages from God.
11 Sa’ad da dukan waɗanda suka san shi a dā suka gan shi yana annabci tare da annabawa, sai suka tambayi juna, suka ce, “Me ya faru da ɗan Kish? Shawulu ma yana cikin annabawa ne?”
When people who had known Saul previously heard him speaking messages from God as the prophets were doing, they said to each other, “What has happened to this son of Kish? Is he now really one of the (prophets/men who speak messages from God)?”
12 Wani mutumin da yake zama a can ya ce, “Wane ne kuma mahaifinsu?” Ta haka sai wannan ya zama karin magana cewa, “Shawulu ma yana cikin annabawa?”
One of the men who lived there replied, “[Saul cannot be a prophet, because] all prophets receive their power to speak messages from God, not from their parents.” And that is why, [when people hear about a report of someone prophesying, they think about what happened to Saul and] say, “[We are surprised about that person becoming a prophet, like] we were surprised to hear that Saul had really become one of the prophets.”
13 Bayan da Shawulu ya gama annabci sai ya haura ya tafi tudu.
When Saul finished speaking the messages that God gave him, he went to the place where the people offered sacrifices.
14 Sai ɗan’uwan mahaifin Shawulu ya tambaye shi da baransa ya ce, “Ina kuka je?” Shawulu ya ce, “Mun tafi neman jakuna, amma da ba mu same su ba sai muka tafi wurin Sama’ila.”
Later, Saul’s uncle [saw him there, and] asked him, “Where did you go?” Saul replied, “We went to look for the donkeys. When we could not find them, we came here to ask Samuel [if he could tell us where they were].”
15 Ɗan’uwan mahaifin Shawulu ya ce, “Faɗa mini abin da Sama’ila ya ce maka.”
Saul’s uncle replied, “What did Samuel tell you?”
16 Shawulu ya ce, “Ya tabbatar mana cewa an riga an sami jakuna.” Amma bai gaya wa ɗan’uwan mahaifinsa abin da Sama’ila ya ce game da sarauta ba.
Saul replied, “He assured us that the donkeys had been found.” But he did not tell his uncle what Samuel had said about him becoming the king [of Israel].
17 Sama’ila ta tattara mutanen Isra’ila a gaban Ubangiji a Mizfa
[Later] Samuel summoned the people of Israel to gather at Mizpah to [hear a message from] Yahweh.
18 ya ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na fito da Isra’ila daga Masar, na kuma cece ku daga hannun Masarawa da dukan mulkokin da suka wahalshe ku.’
After they arrived, he said to them, “This is what Yahweh, the God we Israeli people [worship], says: I brought you Israeli people out of Egypt. I rescued your [ancestors] from the power of the rulers of Egypt and from all the other kings who oppressed them.
19 Amma yanzu kun ƙi Allahnku wanda ya cece ku daga dukan masifu da wahaloli. Kuka ce, ‘Sam, a naɗa mana sarki.’ Saboda haka yanzu sai ku zo gaban Ubangiji kabila-kabila da iyali-iyali.”
I am the one who saves you from all your troubles and difficulties. But today you have rejected me, your God, and you have said, ‘We don’t care! Give us a king!’ So [I will do what you want]. Now have [representatives of] your tribes and [of] your clans stand here in the presence of Yahweh.’”
20 Sa’ad da Sama’ila ya kawo dukan Isra’ila gaba, kabila-kabila, sai aka zaɓi kabilar Benyamin ta wurin jefa ƙuri’a.
When those representatives came near to Samuel, [God indicated that] he had chosen someone from the tribe descended from Benjamin.
21 Sai ya kawo kabilar Benyamin gaba, iyali-iyali, aka zaɓi iyalin Matri. A ƙarshe aka zaɓi Shawulu ɗan Kish. Amma da aka neme shi sai ba a same shi ba.
Then Samuel told representatives of the tribe of Benjamin to come forward, and God indicated that [from that tribe] he had chosen someone from the family of Matri, and then God indicated that [from the family of Matri] he had chosen Saul, the son of Kish. But when they looked for Saul, they could not find him.
22 Suka ƙara nemi bayani daga Ubangiji suka ce, “Mutumin ya zo nan kuwa?” Ubangiji ya ce, “I, ga shi can, ya ɓuya cikin kayayyaki.”
So they asked Yahweh, “Where is Saul?” Yahweh replied, “He is hiding among the army equipment.”
23 Suka ruga suka kawo shi. Da ya tsaya cikin mutane, sai ya fi kowa tsayi.
So they quickly went there [and found him, ] and brought him [in front of all the people]. They could see that [truly] he was a head taller than anyone else.
24 Sama’ila ya ce wa dukan mutane, “Kun ga wanda Ubangiji ya zaɓa ko? Ba wani kamar sa a cikin dukan mutane.” Sai mutane suka tā da murya suka ce, “Ran sarki yă daɗe.”
Then Samuel said to all the people there, “This is the man whom Yahweh has chosen to be your king. Among all us Israeli people, there is no one like him!” Then all the people shouted, “We hope that this king will live a long time!”
25 Sama’ila kuwa ya bayyana wa mutane ƙa’idodin sarauta. Ya rubuta su cikin littafi ya ajiye a gaban Ubangiji. Sa’an nan ya sallame mutane, kowa ya koma gidansa.
Then Samuel told the people what things the king would force them to do, and all the things the king was required to do. He wrote all those things on a scroll, and then he put it in a sacred place in the temple. Then Samuel sent all the people home.
26 Shawulu ma ya tafi gidansa a Gibeya tare da waɗansu jarumawan da Allah ya taɓa zuciyarsu.
When Saul returned to his home in Gibeah [town], a group of men decided to continually accompany Saul. They did that because God (motivated them/put it in their minds) to do that.
27 Amma waɗansu’yan iska suka ce, “Yaya wannan mutum zai iya cetonmu?” Suka rena shi suka ƙi su kawo masa kyautai. Amma Shawulu bai ce uffam ba.
But some worthless men said, “(How can this man save us [from our enemies]?/This man will not be able to save us [from our enemies].)” [RHQ] They despised him, and refused to give him any gifts [to show that they would be loyal to him]. But Saul did not say anything [to rebuke them].

< 1 Sama’ila 10 >