< 1 Sama’ila 10 >
1 Sai Sama’ila ya ɗauki’yar kwalabar mai, ya zuba man ɗin wa Shawulu a kansa, ya yi masa sumba yana cewa, “Ubangiji ya keɓe ka shugaba bisa gādonsa.
And he took Samuel [the] flask of oil and he poured [it] on head his and he kissed him and he said ¿ In-deed he has anointed you Yahweh (to ruler over people his over of Israel and you she will retain among a people Yahweh and you you deliver him from [the] hand of enemies its from round about and this of you [will be] the sign he has anointed you Yahweh *X*) over inheritance his to ruler.
2 Sa’ad da ka rabu da ni yau, za ka sadu da mutum biyu kusa da kabarin Rahila a Zelza, a yankin Benyamin. Za su ce maka, ‘An sami jakunan da ka fita nema, yanzu haka mahaifinka ya bar damuwa kan jakunan ya koma damuwa a kanka, yana cewa, yaya zan gan ɗana?’
When going you this day from with me and you will find two men near [the] tomb of Rachel in [the] territory of Benjamin at Zelzah and they will say to you they have been found the she-asses which you went to seek and there! he has abandoned father your [the] matter of the she-asses and he is anxious to you saying what? will I do for son my.
3 “Sa’an nan za ka ci gaba daga nan sai ka kai wajen babban itace na Tabor. Waɗansu mutum uku za su sadu da kai a hanyarsu zuwa wurin yin wa Allah sujada a Betel. Ɗaya yana ɗauke da’yan awaki uku, ɗaya yana ɗauke da burodi uku, ɗayan kuma yana ɗauke da salkar ruwan inabi.
And you will pass on from there and beyond and you will come to [the] great tree of Tabor and they will find you there three men going up to God Beth-el one [will be] carrying - three kids and one [will be] carrying three round loaves of bread and one [will be] carrying a skin of wine.
4 Za su gaishe ka, su ba ka burodi biyu, kai kuwa sai ka karɓa.
And they will ask of you to welfare and they will give to you two bread[s] and you will take [them] from hand their.
5 “Bayan wannan, za ka tafi Gebiya ta Allah, inda sansanin Filistiyawa yake. Kana shiga garin, za ka sadu da jerin gwanon annabawa suna gangarowa daga tudu, ana kaɗa garaya, ana bugan ganguna, ana hura sarewa, ana kuma bugan molo, a gabansu, su kuma za su yi ta annabci.
After thus you will come Gibeah of God where [are] there [the] garrisons of [the] Philistines and it will be when coming you there the city and you will meet a company of prophets coming down from the high place and [will be] before them lyre and tambourine and flute and harp and they [will be] prophesying.
6 Ruhun Ubangiji zai sauko a kanka da iko, za ka kuma yi annabci tare da su. Za a canja ka ka zama dabam.
And it will rush on you [the] spirit of Yahweh and you will prophesy with them and you will be changed into a man another.
7 Da zarar waɗannan alamu sun cika, sai ka aikata duk abin da kana iya yi gama Allah yana tare da kai.
And it will be that (they will come *Q(k)*) the signs these to you do for yourself [that] which it will find hand your for God [is] with you.
8 “Ka sha gabana zuwa Gilgal. Lalle zan gangara wurinka domin in miƙa hadaya ta ƙonawa da hadayu na salama. Sai ka jira ni kwana bakwai sai na zo wurinka na kuma gaya maka abin da za ka yi.”
And you will go down before me Gilgal and there! I [am] about to come down to you to offer up burnt offerings to sacrifice sacrifices of peace offerings seven days may you wait until come I to you and I will make known to you [that] which you will do.
9 Da Shawulu ya juya zai bar Sama’ila, sai Allah ya canja wa Shawulu zuciya, alamun nan kuwa suka cika a ranar.
And it was when turned he shoulder his to go from with Samuel and he changed for him God a heart another and they came all the signs these on the day that.
10 Da suka iso Gibeya, jerin gwanon annabawa suka sadu da shi Ruhun Allah kuma ya sauko a kansa da iko, sai ya shiga yin annabci tare da su.
And they came there Gibeah towards and there! a company of prophets to meet him and it rushed on him [the] spirit of God and he prophesied in midst of them.
11 Sa’ad da dukan waɗanda suka san shi a dā suka gan shi yana annabci tare da annabawa, sai suka tambayi juna, suka ce, “Me ya faru da ɗan Kish? Shawulu ma yana cikin annabawa ne?”
And it was every [one who] knew him from yesterday three days ago and they saw and there! with prophets [he is] prophesying and it said the people each to neighbor his what? this has it happened to [the] son of Kish ¿ also [is] Saul among the prophets.
12 Wani mutumin da yake zama a can ya ce, “Wane ne kuma mahaifinsu?” Ta haka sai wannan ya zama karin magana cewa, “Shawulu ma yana cikin annabawa?”
And he answered a man from there and he said and who? [is] father their there-fore it became a proverb ¿ also [is] Saul among the prophets.
13 Bayan da Shawulu ya gama annabci sai ya haura ya tafi tudu.
And he finished from prophesying and he came the high place.
14 Sai ɗan’uwan mahaifin Shawulu ya tambaye shi da baransa ya ce, “Ina kuka je?” Shawulu ya ce, “Mun tafi neman jakuna, amma da ba mu same su ba sai muka tafi wurin Sama’ila.”
And he said [the] uncle of Saul to him and to servant his where? did you go and he said to seek the she-asses and we saw that there not and we went to Samuel.
15 Ɗan’uwan mahaifin Shawulu ya ce, “Faɗa mini abin da Sama’ila ya ce maka.”
And he said [the] uncle of Saul tell! please to me what? did he say to you Samuel.
16 Shawulu ya ce, “Ya tabbatar mana cewa an riga an sami jakuna.” Amma bai gaya wa ɗan’uwan mahaifinsa abin da Sama’ila ya ce game da sarauta ba.
And he said Saul to uncle his certainly he told to us that they had been found the she-asses and [the] word of the kingship not he told to him which he had said Samuel.
17 Sama’ila ta tattara mutanen Isra’ila a gaban Ubangiji a Mizfa
And he called together Samuel the people to Yahweh Mizpah.
18 ya ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na fito da Isra’ila daga Masar, na kuma cece ku daga hannun Masarawa da dukan mulkokin da suka wahalshe ku.’
And he said - to [the] people of Israel. Thus he says Yahweh [the] God of Israel I I brought up Israel from Egypt and I delivered you from [the] hand of Egypt and from [the] hand of all the kingdoms that were oppressing you.
19 Amma yanzu kun ƙi Allahnku wanda ya cece ku daga dukan masifu da wahaloli. Kuka ce, ‘Sam, a naɗa mana sarki.’ Saboda haka yanzu sai ku zo gaban Ubangiji kabila-kabila da iyali-iyali.”
And you this day you have rejected God your who he [is] a deliverer of you from all calamities your and troubles your and you have said to him for a king you will appoint over us and therefore present yourselves before Yahweh to tribes your and to families your.
20 Sa’ad da Sama’ila ya kawo dukan Isra’ila gaba, kabila-kabila, sai aka zaɓi kabilar Benyamin ta wurin jefa ƙuri’a.
And he brought near Samuel all [the] tribes of Israel and it was taken by lot [the] tribe of Benjamin.
21 Sai ya kawo kabilar Benyamin gaba, iyali-iyali, aka zaɓi iyalin Matri. A ƙarshe aka zaɓi Shawulu ɗan Kish. Amma da aka neme shi sai ba a same shi ba.
And he brought near [the] tribe of Benjamin (to families its *Q(K)*) and it was taken by lot [the] clan of Matri and he was taken by lot Saul [the] son of Kish and they sought him and not he was found.
22 Suka ƙara nemi bayani daga Ubangiji suka ce, “Mutumin ya zo nan kuwa?” Ubangiji ya ce, “I, ga shi can, ya ɓuya cikin kayayyaki.”
And they enquired again by Yahweh ¿ has he come yet here [the] man. And he said Yahweh here! he [is] hiding himself into the baggage.
23 Suka ruga suka kawo shi. Da ya tsaya cikin mutane, sai ya fi kowa tsayi.
And they ran and they took him from there and he presented himself in among the people and he was tall more than all the people from shoulder his and up-wards.
24 Sama’ila ya ce wa dukan mutane, “Kun ga wanda Ubangiji ya zaɓa ko? Ba wani kamar sa a cikin dukan mutane.” Sai mutane suka tā da murya suka ce, “Ran sarki yă daɗe.”
And he said Samuel to all the people ¿ do you see [the one] whom he has chosen him Yahweh for there not [is] like him among all the people and they shouted all the people and they said may he live the king.
25 Sama’ila kuwa ya bayyana wa mutane ƙa’idodin sarauta. Ya rubuta su cikin littafi ya ajiye a gaban Ubangiji. Sa’an nan ya sallame mutane, kowa ya koma gidansa.
And he spoke Samuel to the people [the] right[s] of the kingship and he wrote in the book and he set [it] before Yahweh and he sent away Samuel all the people each man to own house his.
26 Shawulu ma ya tafi gidansa a Gibeya tare da waɗansu jarumawan da Allah ya taɓa zuciyarsu.
And also Saul he went to own house his Gibeah towards and they went with him the army which he had touched God heart their.
27 Amma waɗansu’yan iska suka ce, “Yaya wannan mutum zai iya cetonmu?” Suka rena shi suka ƙi su kawo masa kyautai. Amma Shawulu bai ce uffam ba.
And sons of worthlessness they said what? will he deliver us this one and they despised him and not they brought to him a gift and he was like [one who] kept silent.