< 1 Sama’ila 1 >

1 Akwai wani mutum daga Ramatayim, mutumin Zuf daga ƙasar tuddan Efraim, sunansa Elkana, ɗan Yeroham, shi jikan Elihu ɗan Tohu, tattaɓa kunnen Zuf, mutumin Efraim.
Il y avait un homme de Ramathaïm-Zophim, dans la montagne d'Éphraïm. Son nom était Elkana, fils de Jerocham, fils d'Élihu, fils de Tohu, fils de Zuph, Éphraïmite.
2 Yana da mata biyu, ɗaya sunanta Hannatu, ɗayan kuwa ana kiranta Feninna. Ita Feninna tana da’ya’ya, amma Hannatu ba ta da’ya’ya.
Il avait deux femmes. Le nom de l'une était Anne, et le nom de l'autre Peninna. Peninna eut des enfants, mais Anne n'eut point d'enfants.
3 Shekara-shekara wannan mutum yakan haura daga garinsa zuwa Shilo domin yin sujada da miƙa hadayu ga Ubangiji Maɗaukaki. A can kuwa’ya’yan Eli maza biyu, Hofni da Finehas su ne firistoci na Ubangiji.
Cet homme montait d'année en année hors de sa ville pour se prosterner et sacrifier à l'Éternel des armées à Silo. Les deux fils d'Eli, Hophni et Phinées, prêtres de l'Éternel, étaient là.
4 Duk sa’ad da rana ta kewayo don Elkana yă miƙa hadaya, yakan ba da kashin nama ga matarsa Feninna da dukan’ya’yanta maza da mata.
Le jour où Elkana offrit un sacrifice, il donna des portions à Peninna, sa femme, à tous ses fils et à toutes ses filles;
5 Amma Hannatu kuwa sai yă ba ta babban rabo gama yana ƙaunarta ko da yake Ubangiji ya kulle mahaifarta.
mais il donna une double portion à Anne, car il aimait Anne, mais l'Éternel lui avait fermé les entrailles.
6 Saboda Ubangiji ya kulle mahaifarta, sai kishiyarta ta dinga tsokanarta don tă ba ta haushi.
Son rival la provoquait durement, pour l'irriter, parce que Yahvé avait fermé ses entrailles.
7 Wannan ya ci gaba shekara da shekaru. Duk lokacin da Hannatu ta haura zuwa haikalin Ubangiji, sai kishiyarta tă tsokane ta har tă yi ta kuka tă kuma ƙi cin abinci.
Ainsi, année après année, quand elle montait à la maison de l'Éternel, sa rivale l'irritait. Elle pleurait donc, et ne mangeait pas.
8 Elkana mijinta kuwa yakan ce mata, “Hannatu don me kike kuka? Me ya sa ba za ki ci abinci ba? Don me kika karaya? Ashe, ban fi’ya’ya goma a gare ki ba?”
Elkana, son mari, lui dit: « Anne, pourquoi pleures-tu? Pourquoi ne manges-tu pas? Pourquoi ton cœur est-il affligé? Ne suis-je pas meilleur pour toi que dix fils? »
9 Wata rana sa’ad da suka gama ci da sha a Shilo, Hannatu ta miƙe tsaye. Eli firist kuwa yana zaune a kujera a bakin ƙofar haikalin Ubangiji.
Et Anne se leva, après qu'on eut fini de manger et de boire à Silo. Or, le sacrificateur Eli était assis sur son siège, près du poteau de la porte du temple de Yahvé.
10 A cikin baƙin ciki, Hannatu ta yi kuka mai zafi ta yi addu’a ga Ubangiji.
Elle était dans l'amertume de l'âme, et elle priait Yahvé en pleurant amèrement.
11 Ta yi ta cewa, “Ya Ubangiji Maɗaukaki. In har ka dubi baƙin cikin baiwarka, ka tuna da ni, ba ka kuma manta da baiwarka ba, amma ka ba ta ɗa, ni ma zan miƙa shi ga Ubangiji dukan rayuwarsa, aska kuwa ba za tă taɓa kansa ba.”
Elle fit un vœu et dit: « Yahvé des armées, si tu regardes l'affliction de ton serviteur et te souviens de moi, et si tu n'oublies pas ton serviteur, mais que tu donnes à ton serviteur un garçon, je le donnerai à Yahvé tous les jours de sa vie, et aucun rasoir ne viendra sur sa tête. »
12 Yayinda take addu’a ga Ubangiji, Eli ya lura da bakinta.
Comme elle continuait à prier devant Yahvé, Eli vit sa bouche.
13 Hannatu tana addu’a a zuci, ba a jin muryarta, sai leɓunanta ne kawai suna motsi. Eli kuwa ya yi tsammani ta bugu ne.
Or Anne parlait dans son cœur. Seules ses lèvres bougeaient, mais on n'entendait pas sa voix. Aussi Éli pensa-t-il qu'elle était ivre.
14 Sai ya ce mata, “Har yaushe za ki ci gaba da maye? Ki daina shan ruwan inabi.”
Eli lui dit: « Jusqu'à quand seras-tu ivre? Débarrasse-toi de ton vin! »
15 Hannatu ta ce, “Ba haka ba ne, ranka yă daɗe, ni mace ce da take cikin matsala ƙwarai da gaske. Ban sha ruwan inabi ba, ko wani abu mai sa maye, ina dai faɗa wa Ubangiji abin da yake damuna ne.
Anne répondit: « Non, mon seigneur, je suis une femme à l'esprit chagrin. Je n'ai bu ni vin ni boisson forte, mais j'ai répandu mon âme devant Yahvé.
16 Kada ka yi zato baiwarka’yar iska ce. Ina addu’a a nan saboda yawan azaba da baƙin cikin da nake ciki.”
Ne considère pas ta servante comme une femme méchante, car j'ai parlé dans l'abondance de ma plainte et de ma provocation. »
17 Eli ya ce, “In haka ne, to, ki sauka lafiya, Allah na Isra’ila kuma yă ba ki abin da kika roƙa daga gare shi.”
Eli répondit: « Va en paix; et que le Dieu d'Israël exauce la demande que tu lui as adressée. »
18 Ta ce, bari baiwarka tă sami tagomashi a idonka. Sai ta yi tafiyarta ta je ta ci wani abu, fuskarta kuwa ba tă ƙara kasance da baƙin ciki ba.
Elle dit: « Que ta servante trouve grâce à tes yeux. » La femme s'en alla donc et mangea, et l'expression de son visage n'était plus triste.
19 Kashegari da sassafe suka tashi suka yi sujada a gaban Ubangiji, sai suka koma garinsu a Rama. Elkana kuwa ya kwana da matarsa Hannatu, Ubangiji kuma ya tuna da ita.
Ils se levèrent de bon matin et se prosternèrent devant l'Éternel, puis ils s'en retournèrent et rentrèrent dans leur maison à Rama. Elkana connut alors Hannah, sa femme, et Yahvé se souvint d'elle.
20 Ana nan sai Hannatu ta yi ciki, ta kuma haifi ɗa. Ta ba shi suna Sama’ila; tana cewa, “Domin na roƙe shi daga wurin Ubangiji.”
Lorsque le temps fut venu, Anne conçut et enfanta un fils; elle lui donna le nom de Samuel, en disant: « Parce que je l'ai demandé à l'Éternel. »
21 Da shekara ta kewayo, sai Elkana da iyalinsa suka sāke tafi Shilo domin su yi hadaya ga Ubangiji, yă kuma cika alkawarin da ya yi.
L'homme Elkana et toute sa maison montèrent pour offrir à Yahvé le sacrifice annuel et son vœu.
22 Hannatu kuwa ba tă bi su ba. Ta gaya wa mijinta cewa, “Sai bayan na yaye yaron, zan kai shi in miƙa shi a gaban Ubangiji, yă kuma kasance a wurin koyaushe.”
Mais Anne ne monta pas, car elle dit à son mari: « Pas avant que l'enfant soit sevré; alors je l'amènerai, afin qu'il se présente devant l'Éternel et qu'il y reste pour toujours. »
23 Elkana mijinta ya ce mata, “Ki yi abin da kika ga ya fi miki kyau. Ki jira har sai bayan kin yaye shi. Ubangiji dai ya cika maganarsa.” Saboda haka matar ta tsaya a gida, ta yi ta renon ɗanta har ta yaye shi.
Elkana, son mari, lui dit: « Fais ce qui te semble bon. Attends que tu l'aies sevré; seulement, que Yahvé accomplisse sa parole. » La femme attendit et allaita son fils jusqu'à ce qu'elle le sevrât.
24 Bayan ta yaye shi, sai ta ɗauki yaron tare da bijimi bana uku, da mudun gari, da salkan ruwan inabi, ta kawo su a gidan Ubangiji a Shilo.
Lorsqu'elle l'eut sevré, elle l'emporta avec elle, avec trois taureaux, un épha de farine et un récipient de vin, et elle l'amena dans la maison de l'Éternel à Silo. L'enfant était jeune.
25 Bayan an yanka bijimin, sai suka kawo yaron wurin Eli.
Ils tuèrent le taureau et amenèrent l'enfant à Eli.
26 Sai ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ba ka gane ni ba? Ai, ni ce matar da ta taɓa tsayawa a gabanka, tana addu’a ga Ubangiji.
Elle dit: « Oh, mon seigneur, aussi vrai que ton âme est vivante, mon seigneur, je suis la femme qui s'est tenue ici près de toi, en priant l'Éternel.
27 Wannan yaron ne na roƙa daga wurin Ubangiji, ya kuwa ba ni abin da na roƙa daga gare shi.
J'ai prié pour cet enfant, et Yahvé m'a accordé la demande que je lui ai adressée.
28 Saboda haka, na ba da shi ga Ubangiji muddin ransa, zai zama na Ubangiji.” A can kuwa ya yi wa Ubangiji sujada.
C'est pourquoi je l'ai aussi remis à Yahvé. Aussi longtemps qu'il vivra, il sera donné à Yahvé. » Il y a adoré Yahvé.

< 1 Sama’ila 1 >