< 1 Sama’ila 1 >
1 Akwai wani mutum daga Ramatayim, mutumin Zuf daga ƙasar tuddan Efraim, sunansa Elkana, ɗan Yeroham, shi jikan Elihu ɗan Tohu, tattaɓa kunnen Zuf, mutumin Efraim.
`A man was of `Ramathym of Sophym, of the hil of Effraym, and his name was Elchana, the sone of Jeroboam, sone of Elyud, sone of Thau, sone of Suph, of Effraym.
2 Yana da mata biyu, ɗaya sunanta Hannatu, ɗayan kuwa ana kiranta Feninna. Ita Feninna tana da’ya’ya, amma Hannatu ba ta da’ya’ya.
And Helchana hadde twei wyues; the name `to oon was Anna, and the `name of the secounde was Fenenna; and sones weren to Feuenna; forsothe fre children `weren not to Anna.
3 Shekara-shekara wannan mutum yakan haura daga garinsa zuwa Shilo domin yin sujada da miƙa hadayu ga Ubangiji Maɗaukaki. A can kuwa’ya’yan Eli maza biyu, Hofni da Finehas su ne firistoci na Ubangiji.
And thilke man styede fro his citee in daies ordeyned, to worschipe and offre sacrifice to the Lord of oostis in Silo. Forsothe twei sones of Heli weren there, Ophym and Fynees, preestis of the Lord.
4 Duk sa’ad da rana ta kewayo don Elkana yă miƙa hadaya, yakan ba da kashin nama ga matarsa Feninna da dukan’ya’yanta maza da mata.
Therfor the dai cam, and Helcana offride, and yaf partis to Fenenna, his wijf, and to alle hise sones and douytris;
5 Amma Hannatu kuwa sai yă ba ta babban rabo gama yana ƙaunarta ko da yake Ubangiji ya kulle mahaifarta.
forsothe he yaf soreufuly o part to Anna, for he louyde Anna; forsothe the Lord hadde closid hir wombe.
6 Saboda Ubangiji ya kulle mahaifarta, sai kishiyarta ta dinga tsokanarta don tă ba ta haushi.
And hir enemy turmentide `hir, and angwischide greetly, in so myche that sche vpbreidide, that the Lord hadde closid hir wombe.
7 Wannan ya ci gaba shekara da shekaru. Duk lokacin da Hannatu ta haura zuwa haikalin Ubangiji, sai kishiyarta tă tsokane ta har tă yi ta kuka tă kuma ƙi cin abinci.
And so sche dide `bi alle yeeris, whanne `in tyme comynge ayen, thei stieden in to the hows of the Lord; and so sche terride Anna. Forsothe Anna wepte, and took not mete.
8 Elkana mijinta kuwa yakan ce mata, “Hannatu don me kike kuka? Me ya sa ba za ki ci abinci ba? Don me kika karaya? Ashe, ban fi’ya’ya goma a gare ki ba?”
Therfor Helcana, hir hosebonde, seide to hir, Anna, whi wepist thou, and whi etist thou not, and whi is thin herte turmentid? Whether Y am not betere to thee than ben ten sones?
9 Wata rana sa’ad da suka gama ci da sha a Shilo, Hannatu ta miƙe tsaye. Eli firist kuwa yana zaune a kujera a bakin ƙofar haikalin Ubangiji.
`Sotheli Anna roos, aftir that sche hadde ete and drunke in Silo. `And the while Hely was on his greet seete, bifor the postis of the `hows of the Lord,
10 A cikin baƙin ciki, Hannatu ta yi kuka mai zafi ta yi addu’a ga Ubangiji.
whanne Anna was in bittere soule, sche preyede the Lord, and wepte largeli;
11 Ta yi ta cewa, “Ya Ubangiji Maɗaukaki. In har ka dubi baƙin cikin baiwarka, ka tuna da ni, ba ka kuma manta da baiwarka ba, amma ka ba ta ɗa, ni ma zan miƙa shi ga Ubangiji dukan rayuwarsa, aska kuwa ba za tă taɓa kansa ba.”
and made a vow, and seide, Lord God of oostis, if thou biholdist, and seest the turment of thi seruauntesse, and hast mynde of me, and foryetis not thin handmayde, and yyuest to thi seruauntesse `a male kynde, Y schal yyue hym to the Lord in alle daies of his lijf, and a rasour schal not stie on his heed.
12 Yayinda take addu’a ga Ubangiji, Eli ya lura da bakinta.
Forsothe it was doon, whanne sche multipliede preieris bifor the Lord, that Ely aspiede hir mouth.
13 Hannatu tana addu’a a zuci, ba a jin muryarta, sai leɓunanta ne kawai suna motsi. Eli kuwa ya yi tsammani ta bugu ne.
Forsothe Anna spak in hir herte, and oneli hir lippis weren mouyd, and outerly hir vois was not herd. Therfor Hely gesside hir drunkun,
14 Sai ya ce mata, “Har yaushe za ki ci gaba da maye? Ki daina shan ruwan inabi.”
and he seide to hyr, Hou longe schalt thou be drunkun? Difye thou a litil the wyn, `bi which thou art moist.
15 Hannatu ta ce, “Ba haka ba ne, ranka yă daɗe, ni mace ce da take cikin matsala ƙwarai da gaske. Ban sha ruwan inabi ba, ko wani abu mai sa maye, ina dai faɗa wa Ubangiji abin da yake damuna ne.
Anna answeride, and seide, Nay, my lord, for Y am `a wretchid womman greetli; Y `drank not wyn `and al thing that may make drunkun, but Y schedde out my soule in the `siyt of the Lord;
16 Kada ka yi zato baiwarka’yar iska ce. Ina addu’a a nan saboda yawan azaba da baƙin cikin da nake ciki.”
gesse thou not thin handmaide as oon of the douytris of Belyal, for of the multitude of my sorewe and morenyng Y spak `til in to present tyme.
17 Eli ya ce, “In haka ne, to, ki sauka lafiya, Allah na Isra’ila kuma yă ba ki abin da kika roƙa daga gare shi.”
Thanne Hely seide to hir, Go thou in pees, and God of Israel yyue to thee the axyng which thou preiedist hym.
18 Ta ce, bari baiwarka tă sami tagomashi a idonka. Sai ta yi tafiyarta ta je ta ci wani abu, fuskarta kuwa ba tă ƙara kasance da baƙin ciki ba.
And sche seide, `Y wolde that thin hondmayde fynde grace in thin iyen. And the womman yede in to hir weie, and eet; and hir cheris weren no more chaungid dyuersly.
19 Kashegari da sassafe suka tashi suka yi sujada a gaban Ubangiji, sai suka koma garinsu a Rama. Elkana kuwa ya kwana da matarsa Hannatu, Ubangiji kuma ya tuna da ita.
And `thei ryseden eerly, and worschipiden bifore the Lord; and thei turneden ayen, and camen in to hir hows in Ramatha. Forsothe Helchana knew fleischli Anna, his wijf; and the Lord thouyte on hir.
20 Ana nan sai Hannatu ta yi ciki, ta kuma haifi ɗa. Ta ba shi suna Sama’ila; tana cewa, “Domin na roƙe shi daga wurin Ubangiji.”
And it was doon after the cumpas of daies, Anna conseyuede, and childide a sone, and sche clepide his name Samuel; for sche hadde axid hym of the Lord.
21 Da shekara ta kewayo, sai Elkana da iyalinsa suka sāke tafi Shilo domin su yi hadaya ga Ubangiji, yă kuma cika alkawarin da ya yi.
Forsothe hir hosebonde Helcana stiede, and al his hows, to offre a solempne sacrifice, and his avow to the Lord.
22 Hannatu kuwa ba tă bi su ba. Ta gaya wa mijinta cewa, “Sai bayan na yaye yaron, zan kai shi in miƙa shi a gaban Ubangiji, yă kuma kasance a wurin koyaushe.”
And Anna stiede not, for sche hadde seid to hir hosebonde, Y schal not go, til the yonge child be wenyd, and til Y lede hym, and he appere bifor the `siyt of the Lord, and dwelle there contynueli.
23 Elkana mijinta ya ce mata, “Ki yi abin da kika ga ya fi miki kyau. Ki jira har sai bayan kin yaye shi. Ubangiji dai ya cika maganarsa.” Saboda haka matar ta tsaya a gida, ta yi ta renon ɗanta har ta yaye shi.
And Helcana, hir hosebonde, seide to hir, Do thou that that semeth good to thee, and dwelle thou til thou wene hym; and Y biseche, that the Lord fille his word. Therfor the womman dwellide, and yaf mylk to hir sone, til sche remouyde hym fro mylk.
24 Bayan ta yaye shi, sai ta ɗauki yaron tare da bijimi bana uku, da mudun gari, da salkan ruwan inabi, ta kawo su a gidan Ubangiji a Shilo.
And sche brouyte hym with hir, aftir that sche hadde wened hym, with thre caluys, and thre buyschelis of mele, and amfore, `ether a pot, of wyn; and sche brouyte hym to the hows of the Lord in Silo. Forsothe the child was yit ful yonge.
25 Bayan an yanka bijimin, sai suka kawo yaron wurin Eli.
And thei sacrifieden a calf, and thei offriden the child to Hely.
26 Sai ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ba ka gane ni ba? Ai, ni ce matar da ta taɓa tsayawa a gabanka, tana addu’a ga Ubangiji.
And Anna seide, My lord, Y biseche, that is, that this child be thi `disciple and seruaunt, thi soule lyueth; Y am that womman, that stood bifor thee here, and preiede the Lord;
27 Wannan yaron ne na roƙa daga wurin Ubangiji, ya kuwa ba ni abin da na roƙa daga gare shi.
for this child Y preiede, and the Lord yaf to me myn axyng which Y axide hym;
28 Saboda haka, na ba da shi ga Ubangiji muddin ransa, zai zama na Ubangiji.” A can kuwa ya yi wa Ubangiji sujada.
therfor Y haue youe hym to the Lord `in alle daies, in whiche he is youun to the Lord. And thei worschypiden there the Lord.