< 1 Sama’ila 1 >

1 Akwai wani mutum daga Ramatayim, mutumin Zuf daga ƙasar tuddan Efraim, sunansa Elkana, ɗan Yeroham, shi jikan Elihu ɗan Tohu, tattaɓa kunnen Zuf, mutumin Efraim.
There was a man named Elkanah who lived in Ramah [town] in the hilly area where [the tribe of] Ephraim lived. His father was Jeroham, his grandfather was Elihu, and his great-grandfather was Tohu. He belonged to the Zuph clan.
2 Yana da mata biyu, ɗaya sunanta Hannatu, ɗayan kuwa ana kiranta Feninna. Ita Feninna tana da’ya’ya, amma Hannatu ba ta da’ya’ya.
He had two wives: Hannah and Peninnah. Peninnah had several children, but Hannah had no children.
3 Shekara-shekara wannan mutum yakan haura daga garinsa zuwa Shilo domin yin sujada da miƙa hadayu ga Ubangiji Maɗaukaki. A can kuwa’ya’yan Eli maza biyu, Hofni da Finehas su ne firistoci na Ubangiji.
Once every year Elkanah went up [with his family] from Ramah to Shiloh [city]. He went there to worship Yahweh, [the commander] of the armies [of angels], and to offer sacrifices to him. The two sons of Eli, Hophni and Phinehas, [helped their father to do the work as] priests of Yahweh there.
4 Duk sa’ad da rana ta kewayo don Elkana yă miƙa hadaya, yakan ba da kashin nama ga matarsa Feninna da dukan’ya’yanta maza da mata.
Each time Elkanah offered sacrifices there, he gave some of the meat to Peninnah and some to each of her sons and daughters.
5 Amma Hannatu kuwa sai yă ba ta babban rabo gama yana ƙaunarta ko da yake Ubangiji ya kulle mahaifarta.
But even though he loved Hannah very much, he gave her only one special amount of meat because Yahweh had not permitted her to give birth to any children.
6 Saboda Ubangiji ya kulle mahaifarta, sai kishiyarta ta dinga tsokanarta don tă ba ta haushi.
And his other wife, Peninnah, would ridicule Hannah to make her feel miserable, because Yahweh had not allowed her to bear children.
7 Wannan ya ci gaba shekara da shekaru. Duk lokacin da Hannatu ta haura zuwa haikalin Ubangiji, sai kishiyarta tă tsokane ta har tă yi ta kuka tă kuma ƙi cin abinci.
This happened every year. When they went up to the temple of Yahweh [at Shiloh], Peninnah ridiculed Hannah so much that Hannah cried and would not eat.
8 Elkana mijinta kuwa yakan ce mata, “Hannatu don me kike kuka? Me ya sa ba za ki ci abinci ba? Don me kika karaya? Ashe, ban fi’ya’ya goma a gare ki ba?”
Then Elkanah would say to her, “Hannah, (why are you crying?/please quit crying!) [RHQ] (Why are you not eating?/Please eat something!) [RHQ] Why are you so upset/sad? You have me; is that not more important to you than if you had ten sons? (OR, I [love you] more than your sons [would love you], even if you had ten sons.)”
9 Wata rana sa’ad da suka gama ci da sha a Shilo, Hannatu ta miƙe tsaye. Eli firist kuwa yana zaune a kujera a bakin ƙofar haikalin Ubangiji.
One year, after they had finished eating and drinking at Shiloh, Hannah stood up [to pray]. Eli the priest was nearby, sitting on a chair by the doorway of the sacred tent of Yahweh.
10 A cikin baƙin ciki, Hannatu ta yi kuka mai zafi ta yi addu’a ga Ubangiji.
Hannah was very distressed, and she cried very sorrowfully as she prayed to Yahweh.
11 Ta yi ta cewa, “Ya Ubangiji Maɗaukaki. In har ka dubi baƙin cikin baiwarka, ka tuna da ni, ba ka kuma manta da baiwarka ba, amma ka ba ta ɗa, ni ma zan miƙa shi ga Ubangiji dukan rayuwarsa, aska kuwa ba za tă taɓa kansa ba.”
She made a vow saying, “O Almighty Commander of the armies of angels, if you will look at me and see how miserable I am, and think about me and allow me to give birth to a son, then I will dedicate him to you [to serve you] for the rest of his life. And [to show that he is dedicated to you], (no one will ever [be allowed to] cut his hair/his hair will never be cut).”
12 Yayinda take addu’a ga Ubangiji, Eli ya lura da bakinta.
As she was praying like that to Yahweh, Eli the priest saw Hannah’s lips [moving as she was praying].
13 Hannatu tana addu’a a zuci, ba a jin muryarta, sai leɓunanta ne kawai suna motsi. Eli kuwa ya yi tsammani ta bugu ne.
But Hannah was only praying silently; she was not making any sound. So Eli thought that she was drunk.
14 Sai ya ce mata, “Har yaushe za ki ci gaba da maye? Ki daina shan ruwan inabi.”
He said to her, “How long will you continue to get drunk [RHQ]? (Throw away your wine/Quit drinking wine)!”
15 Hannatu ta ce, “Ba haka ba ne, ranka yă daɗe, ni mace ce da take cikin matsala ƙwarai da gaske. Ban sha ruwan inabi ba, ko wani abu mai sa maye, ina dai faɗa wa Ubangiji abin da yake damuna ne.
Hannah replied, “Sir, I am not drunk! I have not been drinking wine or any other alcoholic drink. I feel very distressed and I have been telling Yahweh about how I feel.
16 Kada ka yi zato baiwarka’yar iska ce. Ina addu’a a nan saboda yawan azaba da baƙin cikin da nake ciki.”
Do not think that I am a worthless/wicked woman! I have been praying like this because I am very distressed [DOU].”
17 Eli ya ce, “In haka ne, to, ki sauka lafiya, Allah na Isra’ila kuma yă ba ki abin da kika roƙa daga gare shi.”
Eli replied, “I wish/desire that things will go well for you. I desire that God, the one we Israeli people [worship], will give you what you requested from him.”
18 Ta ce, bari baiwarka tă sami tagomashi a idonka. Sai ta yi tafiyarta ta je ta ci wani abu, fuskarta kuwa ba tă ƙara kasance da baƙin ciki ba.
She replied, “I want you to think highly/well about me.” Then she returned [to her family] and after she ate something, her face no longer looked sad.
19 Kashegari da sassafe suka tashi suka yi sujada a gaban Ubangiji, sai suka koma garinsu a Rama. Elkana kuwa ya kwana da matarsa Hannatu, Ubangiji kuma ya tuna da ita.
Early the next morning, Elkanah and his family got up and worshiped Yahweh [again], and then they returned to their home at Ramah. Elkanah (slept with/had sex with) Hannah. Then Yahweh answered her prayer,
20 Ana nan sai Hannatu ta yi ciki, ta kuma haifi ɗa. Ta ba shi suna Sama’ila; tana cewa, “Domin na roƙe shi daga wurin Ubangiji.”
and she became pregnant and gave birth to a son. She named him Samuel, [which sounds like the words in the Hebrew language that mean ‘heard by God’], because she said “Yahweh [heard me when] I requested from him [a son].”
21 Da shekara ta kewayo, sai Elkana da iyalinsa suka sāke tafi Shilo domin su yi hadaya ga Ubangiji, yă kuma cika alkawarin da ya yi.
The following year, Elkanah again went up [to Shiloh] with his family to make the kind of sacrifice he made each year, and also to give a special offering to God that he had promised [to give him previously].
22 Hannatu kuwa ba tă bi su ba. Ta gaya wa mijinta cewa, “Sai bayan na yaye yaron, zan kai shi in miƙa shi a gaban Ubangiji, yă kuma kasance a wurin koyaushe.”
But Hannah did not go [with them]. She said to her husband, “After I have weaned the baby, I will take him [to Shiloh and present him] to Yahweh, and he will stay there for the rest of his life.”
23 Elkana mijinta ya ce mata, “Ki yi abin da kika ga ya fi miki kyau. Ki jira har sai bayan kin yaye shi. Ubangiji dai ya cika maganarsa.” Saboda haka matar ta tsaya a gida, ta yi ta renon ɗanta har ta yaye shi.
Elkanah said, “Do what seems the best to you. Stay here until you have weaned him. What I desire is that Yahweh will [enable you to] do what you have promised.” So Hannah stayed at home and nursed her son until she weaned him.
24 Bayan ta yaye shi, sai ta ɗauki yaron tare da bijimi bana uku, da mudun gari, da salkan ruwan inabi, ta kawo su a gidan Ubangiji a Shilo.
After she weaned him, even though Samuel was very young, she took him to the temple/house of Yahweh at Shiloh. [To offer as a sacrifice], she took along a three-year-old bull, [a sack containing] (20 pounds/9 kg.) of flour, and a container of wine.
25 Bayan an yanka bijimin, sai suka kawo yaron wurin Eli.
After the priest had slaughtered the bull [and offered it to Yahweh on the altar], Hannah and Elkanah brought the boy to Eli.
26 Sai ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ba ka gane ni ba? Ai, ni ce matar da ta taɓa tsayawa a gabanka, tana addu’a ga Ubangiji.
Then Hannah said to him, “Sir, (Do you remember me?/I solemnly affirm), I am the woman who prayed as I stood here beside you [several years ago].
27 Wannan yaron ne na roƙa daga wurin Ubangiji, ya kuwa ba ni abin da na roƙa daga gare shi.
I prayed that Yahweh would enable me to give birth to a child, and this is the child whom I requested Yahweh to give me.
28 Saboda haka, na ba da shi ga Ubangiji muddin ransa, zai zama na Ubangiji.” A can kuwa ya yi wa Ubangiji sujada.
So now I am presenting him to Yahweh. He will belong to Yahweh as long as he lives.” Then Elkanah [and his family] worshiped Yahweh there.

< 1 Sama’ila 1 >