< 1 Sama’ila 1 >

1 Akwai wani mutum daga Ramatayim, mutumin Zuf daga ƙasar tuddan Efraim, sunansa Elkana, ɗan Yeroham, shi jikan Elihu ɗan Tohu, tattaɓa kunnen Zuf, mutumin Efraim.
And he was a man one from Ramathaim Zophim from [the] hill country of Ephraim and name his [was] Elkanah [the] son of Jeroham [the] son of Elihu [the] son of Tohu [the] son of Zuph an Ephrathite.
2 Yana da mata biyu, ɗaya sunanta Hannatu, ɗayan kuwa ana kiranta Feninna. Ita Feninna tana da’ya’ya, amma Hannatu ba ta da’ya’ya.
And [belonged] to him two wives [the] name of one [was] Hannah and [the] name of the second [was] Peninnah and it belonged to Peninnah children and [belonged] to Hannah not children.
3 Shekara-shekara wannan mutum yakan haura daga garinsa zuwa Shilo domin yin sujada da miƙa hadayu ga Ubangiji Maɗaukaki. A can kuwa’ya’yan Eli maza biyu, Hofni da Finehas su ne firistoci na Ubangiji.
And he went up the man that from city his from days - days towards to bow down and to sacrifice to Yahweh of hosts at Shiloh and there [the] two [the] sons of Eli Hophni and Phinehas [were] priests of Yahweh.
4 Duk sa’ad da rana ta kewayo don Elkana yă miƙa hadaya, yakan ba da kashin nama ga matarsa Feninna da dukan’ya’yanta maza da mata.
And it was the day and he sacrificed Elkanah and he gave to Peninnah wife his and to all sons her and daughters her portions.
5 Amma Hannatu kuwa sai yă ba ta babban rabo gama yana ƙaunarta ko da yake Ubangiji ya kulle mahaifarta.
And to Hannah he gave a portion one double for Hannah he loved and Yahweh he had closed womb her.
6 Saboda Ubangiji ya kulle mahaifarta, sai kishiyarta ta dinga tsokanarta don tă ba ta haushi.
And she provoked her rival her also provocation in order to disconcert her for he had closed Yahweh behind womb her.
7 Wannan ya ci gaba shekara da shekaru. Duk lokacin da Hannatu ta haura zuwa haikalin Ubangiji, sai kishiyarta tă tsokane ta har tă yi ta kuka tă kuma ƙi cin abinci.
And thus he did a year in a year as often as went up she in [the] house of Yahweh thus she provoked her and she wept and not she ate.
8 Elkana mijinta kuwa yakan ce mata, “Hannatu don me kike kuka? Me ya sa ba za ki ci abinci ba? Don me kika karaya? Ashe, ban fi’ya’ya goma a gare ki ba?”
And he said to her Elkanah husband her O Hannah why? do you weep and why? not are you eating and why? is sad heart your ¿ not [am] I good to you more than ten sons.
9 Wata rana sa’ad da suka gama ci da sha a Shilo, Hannatu ta miƙe tsaye. Eli firist kuwa yana zaune a kujera a bakin ƙofar haikalin Ubangiji.
And she arose Hannah after had eaten in Shiloh and after had drunk and Eli the priest [was] sitting on the seat at [the] doorpost of [the] temple of Yahweh.
10 A cikin baƙin ciki, Hannatu ta yi kuka mai zafi ta yi addu’a ga Ubangiji.
And she [was] bitter of soul and she prayed to Yahweh and utterly she wept.
11 Ta yi ta cewa, “Ya Ubangiji Maɗaukaki. In har ka dubi baƙin cikin baiwarka, ka tuna da ni, ba ka kuma manta da baiwarka ba, amma ka ba ta ɗa, ni ma zan miƙa shi ga Ubangiji dukan rayuwarsa, aska kuwa ba za tă taɓa kansa ba.”
And she vowed a vow and she said O Yahweh of hosts certainly [if] you will look - on [the] affliction of maidservant your and you will remember me and not you will forget maidservant your and you will give to maidservant of your spring of men and I will give him to Yahweh all [the] days of life his and a razor not it will go up on head his.
12 Yayinda take addu’a ga Ubangiji, Eli ya lura da bakinta.
And it was that she had increased to pray before Yahweh and Eli [was] watching mouth her.
13 Hannatu tana addu’a a zuci, ba a jin muryarta, sai leɓunanta ne kawai suna motsi. Eli kuwa ya yi tsammani ta bugu ne.
And Hannah she [was] speaking to heart her only lips her [were] quivering and voice her not it was heard and he considered her Eli to a drunken [woman].
14 Sai ya ce mata, “Har yaushe za ki ci gaba da maye? Ki daina shan ruwan inabi.”
And he said to her Eli until when? will you be drunk! remove wine your from with you.
15 Hannatu ta ce, “Ba haka ba ne, ranka yă daɗe, ni mace ce da take cikin matsala ƙwarai da gaske. Ban sha ruwan inabi ba, ko wani abu mai sa maye, ina dai faɗa wa Ubangiji abin da yake damuna ne.
And she answered Hannah and she said no O lord my [am] a woman hard of spirit I and wine and strong drink not I have drunk and I have poured out soul my before Yahweh.
16 Kada ka yi zato baiwarka’yar iska ce. Ina addu’a a nan saboda yawan azaba da baƙin cikin da nake ciki.”
May not you give maidservant your before a daughter of worthlessness for from [the] greatness of complaint my and provocation my I have spoken until now.
17 Eli ya ce, “In haka ne, to, ki sauka lafiya, Allah na Isra’ila kuma yă ba ki abin da kika roƙa daga gare shi.”
And he answered Eli and he said go to peace and [the] God of Israel may he grant petition your which you have asked from with him.
18 Ta ce, bari baiwarka tă sami tagomashi a idonka. Sai ta yi tafiyarta ta je ta ci wani abu, fuskarta kuwa ba tă ƙara kasance da baƙin ciki ba.
And she said may she find maidservant your favor in view your and she went the woman to way her and she ate and face her not they were to her still.
19 Kashegari da sassafe suka tashi suka yi sujada a gaban Ubangiji, sai suka koma garinsu a Rama. Elkana kuwa ya kwana da matarsa Hannatu, Ubangiji kuma ya tuna da ita.
And they rose early in the morning and they bowed down before Yahweh and they returned and they went to house their Ramah towards and he knew Elkanah Hannah wife his and he remembered her Yahweh.
20 Ana nan sai Hannatu ta yi ciki, ta kuma haifi ɗa. Ta ba shi suna Sama’ila; tana cewa, “Domin na roƙe shi daga wurin Ubangiji.”
And it was to [the] circuit of the days and she conceived Hannah and she bore a son and she called name his Samuel for from Yahweh I asked for him.
21 Da shekara ta kewayo, sai Elkana da iyalinsa suka sāke tafi Shilo domin su yi hadaya ga Ubangiji, yă kuma cika alkawarin da ya yi.
And he went up the man Elkanah and all household his to sacrifice to Yahweh [the] sacrifice of the days and vow his.
22 Hannatu kuwa ba tă bi su ba. Ta gaya wa mijinta cewa, “Sai bayan na yaye yaron, zan kai shi in miƙa shi a gaban Ubangiji, yă kuma kasance a wurin koyaushe.”
And Hannah not she went up for she said to husband her until he will be weaned the lad and I will take him and he will appear with [the] presence of Yahweh and he will dwell there until perpetuity.
23 Elkana mijinta ya ce mata, “Ki yi abin da kika ga ya fi miki kyau. Ki jira har sai bayan kin yaye shi. Ubangiji dai ya cika maganarsa.” Saboda haka matar ta tsaya a gida, ta yi ta renon ɗanta har ta yaye shi.
And he said to her Elkanah husband her do the good in view your remain until wean you him only may he carry out Yahweh word his and she remained the woman and she suckled son her until (had weaned she *LAH(b)*) him.
24 Bayan ta yaye shi, sai ta ɗauki yaron tare da bijimi bana uku, da mudun gari, da salkan ruwan inabi, ta kawo su a gidan Ubangiji a Shilo.
And she brought up him with her just when she had weaned him with young bulls three and an ephah one of flour and a skin of wine and she took him [the] house of Yahweh Shiloh and the lad [was] a lad.
25 Bayan an yanka bijimin, sai suka kawo yaron wurin Eli.
And they slaughtered the young bull and they brought the lad to Eli.
26 Sai ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ba ka gane ni ba? Ai, ni ce matar da ta taɓa tsayawa a gabanka, tana addu’a ga Ubangiji.
And she said pardon me O lord my [by] [the] life of self your O lord my I [am] the woman who stood with you in this [place] to pray to Yahweh.
27 Wannan yaron ne na roƙa daga wurin Ubangiji, ya kuwa ba ni abin da na roƙa daga gare shi.
Concerning the lad this I prayed and he has granted Yahweh to me petition my which I asked from with him.
28 Saboda haka, na ba da shi ga Ubangiji muddin ransa, zai zama na Ubangiji.” A can kuwa ya yi wa Ubangiji sujada.
And also I I entrust him to Yahweh all the days which he has been he [is] asked by Yahweh and he bowed down there to Yahweh.

< 1 Sama’ila 1 >