< 1 Sama’ila 1 >

1 Akwai wani mutum daga Ramatayim, mutumin Zuf daga ƙasar tuddan Efraim, sunansa Elkana, ɗan Yeroham, shi jikan Elihu ɗan Tohu, tattaɓa kunnen Zuf, mutumin Efraim.
Der var en Mand fra Ramatajim, en Zufit fra Efraims Bjerge ved Navn Elkana, en Søn af Jerobam, en Søn af Elihu, en Søn af Tohu, en Søn af Zuf, en Efraimit.
2 Yana da mata biyu, ɗaya sunanta Hannatu, ɗayan kuwa ana kiranta Feninna. Ita Feninna tana da’ya’ya, amma Hannatu ba ta da’ya’ya.
Han havde to Hustruer; den ene hed Hanna, den anden Peninna; Peninna havde Børn, men Hanna ikke.
3 Shekara-shekara wannan mutum yakan haura daga garinsa zuwa Shilo domin yin sujada da miƙa hadayu ga Ubangiji Maɗaukaki. A can kuwa’ya’yan Eli maza biyu, Hofni da Finehas su ne firistoci na Ubangiji.
Denne Mand drog hvert Aar op fra sin By for at tilbede Hærskarers HERRE og ofre til ham i Silo, hvor Elis to Sønner Hofni og Pinehas Var Præster for HERREN.
4 Duk sa’ad da rana ta kewayo don Elkana yă miƙa hadaya, yakan ba da kashin nama ga matarsa Feninna da dukan’ya’yanta maza da mata.
En Dag ofrede nu Elkana — han plejede at give sin Hustru Peninna og alle hendes Sønner og Døtre flere Dele,
5 Amma Hannatu kuwa sai yă ba ta babban rabo gama yana ƙaunarta ko da yake Ubangiji ya kulle mahaifarta.
men skønt han elskede Hanna, gav han hende kun een Del, fordi HERREN havde tillukket hendes Moderliv;
6 Saboda Ubangiji ya kulle mahaifarta, sai kishiyarta ta dinga tsokanarta don tă ba ta haushi.
hendes Medbejlerske tilføjede hende ogsaa grove Krænkelser for den Skam, at HERREN havde tillukket hendes Moderliv.
7 Wannan ya ci gaba shekara da shekaru. Duk lokacin da Hannatu ta haura zuwa haikalin Ubangiji, sai kishiyarta tă tsokane ta har tă yi ta kuka tă kuma ƙi cin abinci.
Saaledes gik det Aar efter Aar: hver Gang de drog op til HERRENS Hus, krænkede hun hende saaledes — saa skete det, at hun græd og ikke vilde spise.
8 Elkana mijinta kuwa yakan ce mata, “Hannatu don me kike kuka? Me ya sa ba za ki ci abinci ba? Don me kika karaya? Ashe, ban fi’ya’ya goma a gare ki ba?”
Da sagde hendes Mand Elkana til hende: »Hanna, hvorfor græder du, og hvorfor spiser du ikke? Hvorfor er du mismodig? Er jeg dig ikke mere værd end ti Sønner?«
9 Wata rana sa’ad da suka gama ci da sha a Shilo, Hannatu ta miƙe tsaye. Eli firist kuwa yana zaune a kujera a bakin ƙofar haikalin Ubangiji.
Men da de havde holdt Maaltid i Silo, stod Hanna op og traadte hen for HERRENS Aasyn, medens Præsten Eli sad paa sin Stol ved en af Dørstolperne i HERRENS Hus;
10 A cikin baƙin ciki, Hannatu ta yi kuka mai zafi ta yi addu’a ga Ubangiji.
og i sin Vaande bad hun under heftig Graad til HERREN
11 Ta yi ta cewa, “Ya Ubangiji Maɗaukaki. In har ka dubi baƙin cikin baiwarka, ka tuna da ni, ba ka kuma manta da baiwarka ba, amma ka ba ta ɗa, ni ma zan miƙa shi ga Ubangiji dukan rayuwarsa, aska kuwa ba za tă taɓa kansa ba.”
og aflagde det Løfte: »Hærskarers HERRE! Hvis du vil se til din Tjenerindes Nød og komme mig i Hu og ikke glemme din Tjenerinde, men give din Tjenerinde en Søn, saa vil jeg give ham til HERREN alle hans Levedage, og ingen Ragekniv skal komme paa hans Hoved!«
12 Yayinda take addu’a ga Ubangiji, Eli ya lura da bakinta.
Saaledes bad hun længe for HERRENS Aasyn, og Eli iagttog hendes Mund;
13 Hannatu tana addu’a a zuci, ba a jin muryarta, sai leɓunanta ne kawai suna motsi. Eli kuwa ya yi tsammani ta bugu ne.
men da Hanna talte ved sig selv, saa kun hendes Læber bevægede sig, og hendes Stemme ikke kunde høres, troede Eli, at hun var beruset,
14 Sai ya ce mata, “Har yaushe za ki ci gaba da maye? Ki daina shan ruwan inabi.”
og sagde til hende: »Hvor længe vil du gaa og være drukken? Se at komme af med din Rus!«
15 Hannatu ta ce, “Ba haka ba ne, ranka yă daɗe, ni mace ce da take cikin matsala ƙwarai da gaske. Ban sha ruwan inabi ba, ko wani abu mai sa maye, ina dai faɗa wa Ubangiji abin da yake damuna ne.
Men Hanna svarede: »Nej, Herre! Jeg er en haardt prøvet Kvinde; Vin og stærk Drik har jeg ikke drukket; jeg udøste kun min Sjæl for HERRENS Aasyn.
16 Kada ka yi zato baiwarka’yar iska ce. Ina addu’a a nan saboda yawan azaba da baƙin cikin da nake ciki.”
Regn ikke din Trælkvinde for en daarlig Kvinde! Nej, hele Tiden har jeg talt ud af min dybe Kummer og Kvide!«
17 Eli ya ce, “In haka ne, to, ki sauka lafiya, Allah na Isra’ila kuma yă ba ki abin da kika roƙa daga gare shi.”
Eli svarede: »Gaa bort i Fred! Israels Gud vil give dig, hvad du har bedt ham om!«
18 Ta ce, bari baiwarka tă sami tagomashi a idonka. Sai ta yi tafiyarta ta je ta ci wani abu, fuskarta kuwa ba tă ƙara kasance da baƙin ciki ba.
Da sagde hun: »Maatte din Trælkvinde finde Naade for dine Øjne!« Saa gik Kvinden sin Vej, og hun spiste og saa ikke længer forgræmmet ud.
19 Kashegari da sassafe suka tashi suka yi sujada a gaban Ubangiji, sai suka koma garinsu a Rama. Elkana kuwa ya kwana da matarsa Hannatu, Ubangiji kuma ya tuna da ita.
Næste Morgen stod de tidligt op og kastede sig ned for HERRENS Aasyn; og saa vendte de tilbage og kom hjem til deres Hus i Rama. Og Elkana kendte sin Hustru Hanna, og HERREN kom hende i Hu;
20 Ana nan sai Hannatu ta yi ciki, ta kuma haifi ɗa. Ta ba shi suna Sama’ila; tana cewa, “Domin na roƙe shi daga wurin Ubangiji.”
og hun blev frugtsommelig og fødte en Søn Aaret efter og gav ham Navnet Samuel; »thi, « sagde hun, »jeg har bedt mig ham til hos HERREN!«
21 Da shekara ta kewayo, sai Elkana da iyalinsa suka sāke tafi Shilo domin su yi hadaya ga Ubangiji, yă kuma cika alkawarin da ya yi.
Da Elkana nu med hele sit Hus drog op for at bringe HERREN det aarlige Offer og sit Løfteoffer,
22 Hannatu kuwa ba tă bi su ba. Ta gaya wa mijinta cewa, “Sai bayan na yaye yaron, zan kai shi in miƙa shi a gaban Ubangiji, yă kuma kasance a wurin koyaushe.”
drog Hanna ikke med; thi hun sagde til sin Mand: »Jeg vil vente, til Drengen er vænnet fra, saa vil jeg bringe ham derhen, for at han kan stedes for HERRENS Aasyn og blive der for stedse!«
23 Elkana mijinta ya ce mata, “Ki yi abin da kika ga ya fi miki kyau. Ki jira har sai bayan kin yaye shi. Ubangiji dai ya cika maganarsa.” Saboda haka matar ta tsaya a gida, ta yi ta renon ɗanta har ta yaye shi.
Da sagde hendes Mand Elkana til hende: »Gør, som du synes! Bliv her, indtil du har vænnet ham fra! Maatte HERREN kun gøre dit Ord til Virkelighed!« Saa blev Kvinden hjemme og ammede sin Søn, indtil hun vænnede ham fra.
24 Bayan ta yaye shi, sai ta ɗauki yaron tare da bijimi bana uku, da mudun gari, da salkan ruwan inabi, ta kawo su a gidan Ubangiji a Shilo.
Men da hun havde vænnet ham fra, tog hun ham med, desuden en treaars Tyr, en Efa Mel og en Dunk Vin, og hun kom til HERRENS Hus i Silo og havde Drengen med.
25 Bayan an yanka bijimin, sai suka kawo yaron wurin Eli.
Da nu Tyren var slagtet, kom Drengens Moder til Eli
26 Sai ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ba ka gane ni ba? Ai, ni ce matar da ta taɓa tsayawa a gabanka, tana addu’a ga Ubangiji.
og sagde: »Hør mig, Herre! Saa sandt du lever, Herre, jeg er den Kvinde, som stod her ved din Side og bad til HERREN.
27 Wannan yaron ne na roƙa daga wurin Ubangiji, ya kuwa ba ni abin da na roƙa daga gare shi.
Om denne Dreng bad jeg, og HERREN gav mig, hvad jeg bad ham om.
28 Saboda haka, na ba da shi ga Ubangiji muddin ransa, zai zama na Ubangiji.” A can kuwa ya yi wa Ubangiji sujada.
Derfor vil jeg ogsaa overlade ham til HERREN; hele sit Liv skal han være overladt til HERREN!« Og hun lod ham blive der for HERRENS Aasyn.

< 1 Sama’ila 1 >