< 1 Sama’ila 1 >
1 Akwai wani mutum daga Ramatayim, mutumin Zuf daga ƙasar tuddan Efraim, sunansa Elkana, ɗan Yeroham, shi jikan Elihu ɗan Tohu, tattaɓa kunnen Zuf, mutumin Efraim.
Ephraim mon, Ramathaim kho dawk tami buet touh ao. A min teh Elkanah, Ephraim kho e Zuph capa, Tohu capa, Elihu capa, Jeroham capa doeh.
2 Yana da mata biyu, ɗaya sunanta Hannatu, ɗayan kuwa ana kiranta Feninna. Ita Feninna tana da’ya’ya, amma Hannatu ba ta da’ya’ya.
Ahni teh a yu kahni touh a tawn, buet touh e min teh Hannah, buet touh e teh Peninnah, Peninnah teh a ca a tawn, Hannah teh ca tawn hoeh.
3 Shekara-shekara wannan mutum yakan haura daga garinsa zuwa Shilo domin yin sujada da miƙa hadayu ga Ubangiji Maɗaukaki. A can kuwa’ya’yan Eli maza biyu, Hofni da Finehas su ne firistoci na Ubangiji.
Elkanah teh ransahu BAWIPA bawk hane hoi thueng hanelah amae kho hoi Shiloh kho kumtangkuem ouk a cei. Hote kho dawk Eli e capa roi Hophni hoi Phinehas teh Bawipa e vaihma lah ao roi.
4 Duk sa’ad da rana ta kewayo don Elkana yă miƙa hadaya, yakan ba da kashin nama ga matarsa Feninna da dukan’ya’yanta maza da mata.
Thuengnae tueng a pha navah Elkanah ni a yu Peninnah hoi a canaw e ham a rei.
5 Amma Hannatu kuwa sai yă ba ta babban rabo gama yana ƙaunarta ko da yake Ubangiji ya kulle mahaifarta.
Hatei Hannah teh coe hane let hni touh a poe. Bawipa ni Hannah ca khe hane kâ poe hoeh ei Hannah a pahren dawk a poe.
6 Saboda Ubangiji ya kulle mahaifarta, sai kishiyarta ta dinga tsokanarta don tă ba ta haushi.
Bawipa ni Hannah hah ca khenae a poe hoeh dawkvah, Hannah hoi kâpo hoeh e napui ni, Hannah a lungmathoe nahanelah voutsout a sak.
7 Wannan ya ci gaba shekara da shekaru. Duk lokacin da Hannatu ta haura zuwa haikalin Ubangiji, sai kishiyarta tă tsokane ta har tă yi ta kuka tă kuma ƙi cin abinci.
Hottelah kumtangkuem, Bawipa im a cei navah, lungmathoenae a poe, a khuika teh bu hai cat laipalah Hannah teh ao.
8 Elkana mijinta kuwa yakan ce mata, “Hannatu don me kike kuka? Me ya sa ba za ki ci abinci ba? Don me kika karaya? Ashe, ban fi’ya’ya goma a gare ki ba?”
A vâ Elkanah ni Hannah bangkongmaw bu na ca hoeh. Bangkongmaw na lung a mathoe. Capa hra touh hlak nang hanelah kahawi nahoehmaw telah atipouh.
9 Wata rana sa’ad da suka gama ci da sha a Shilo, Hannatu ta miƙe tsaye. Eli firist kuwa yana zaune a kujera a bakin ƙofar haikalin Ubangiji.
Shiloh kho vah a canei awh hnukkhu vaihma teh BAWIPA e bawkim longkha koe a tahung navah,
10 A cikin baƙin ciki, Hannatu ta yi kuka mai zafi ta yi addu’a ga Ubangiji.
Hannah a thaw teh, lungthin ka rek lah khuika laihoi BAWIPA koe a ratoum.
11 Ta yi ta cewa, “Ya Ubangiji Maɗaukaki. In har ka dubi baƙin cikin baiwarka, ka tuna da ni, ba ka kuma manta da baiwarka ba, amma ka ba ta ɗa, ni ma zan miƙa shi ga Ubangiji dukan rayuwarsa, aska kuwa ba za tă taɓa kansa ba.”
Hannah ni ransahu BAWIPA, nange sannu e rucatnae na hmu teh kai na pahnim hanh. Na sannu pou na pouk lah, capa na poe pawiteh hote capa teh a hring nathung BAWIPA koe ka poe han. A sam hai ka ngaw pouh mahoeh telah lawkkamnae a sak.
12 Yayinda take addu’a ga Ubangiji, Eli ya lura da bakinta.
Hannah teh, BAWIPA hmalah pou a ratoum nah Eli ni apâhni a khet pouh.
13 Hannatu tana addu’a a zuci, ba a jin muryarta, sai leɓunanta ne kawai suna motsi. Eli kuwa ya yi tsammani ta bugu ne.
Hannah ni a lungthung hoi a ratoum. A pahni dueng a kâroe teh a lawk a thai hoeh dawkvah, yamu a parui telah Eli ni a pouk.
14 Sai ya ce mata, “Har yaushe za ki ci gaba da maye? Ki daina shan ruwan inabi.”
Nâsittouh maw na parui lahoi na o han. Misurtui hah takhoe leih telah atipouh.
15 Hannatu ta ce, “Ba haka ba ne, ranka yă daɗe, ni mace ce da take cikin matsala ƙwarai da gaske. Ban sha ruwan inabi ba, ko wani abu mai sa maye, ina dai faɗa wa Ubangiji abin da yake damuna ne.
Hannah ni nahoeh bawipa, lungmathoenae hoi kaawm e doeh. Misur thoseh, yamu thoseh ka net hoeh. BAWIPA hmalah kahringnae ka rabawk e doeh.
16 Kada ka yi zato baiwarka’yar iska ce. Ina addu’a a nan saboda yawan azaba da baƙin cikin da nake ciki.”
Na sannu tami kahawihoehe lah pouk hanh. Ka phuenang laihoi atu sittouh ka hei telah bout a dei navah,
17 Eli ya ce, “In haka ne, to, ki sauka lafiya, Allah na Isra’ila kuma yă ba ki abin da kika roƙa daga gare shi.”
Eli ni karoumcalah cet haw, BAWIPA koe na hei e teh, Isarel miphun e Cathut ni na poe lawiseh telah atipouh.
18 Ta ce, bari baiwarka tă sami tagomashi a idonka. Sai ta yi tafiyarta ta je ta ci wani abu, fuskarta kuwa ba tă ƙara kasance da baƙin ciki ba.
Hannah ni hai na sannu kai teh, na minhmai kahawi kahmawt naseh telah a dei hnukkhu, a minhmai kapan lahoi a cei teh bu a ca toe.
19 Kashegari da sassafe suka tashi suka yi sujada a gaban Ubangiji, sai suka koma garinsu a Rama. Elkana kuwa ya kwana da matarsa Hannatu, Ubangiji kuma ya tuna da ita.
Ahnimouh teh amom a thaw awh teh, BAWIPA a bawk awh teh Ramah kho amamouh im vah a pha awh. ELkanah teh a yu Hannah hoi a kâpanue roi teh BAWIPA ni Hannah teh pahnim hoeh.
20 Ana nan sai Hannatu ta yi ciki, ta kuma haifi ɗa. Ta ba shi suna Sama’ila; tana cewa, “Domin na roƙe shi daga wurin Ubangiji.”
Hannah ni camo a von teh atueng akuep navah ca tongpa a khe. Hete ca teh BAWIPA koe ratoum lahoi hmu e lah ao dawkvah, Samuel telah a min a phung.
21 Da shekara ta kewayo, sai Elkana da iyalinsa suka sāke tafi Shilo domin su yi hadaya ga Ubangiji, yă kuma cika alkawarin da ya yi.
Elkanah hoi a imthungnaw teh BAWIPA koe kumtangkuem ouk a sak awh e thueng hanelah lawk a kam e kuep sak hanelah a cei.
22 Hannatu kuwa ba tă bi su ba. Ta gaya wa mijinta cewa, “Sai bayan na yaye yaron, zan kai shi in miƙa shi a gaban Ubangiji, yă kuma kasance a wurin koyaushe.”
Hannah ni a vâ koe, camo sanu a kamphei torei doeh BAWIPA hmalah, ka ceikhai vaiteh BAWIPA koe pou ao han toe telah atipouh.
23 Elkana mijinta ya ce mata, “Ki yi abin da kika ga ya fi miki kyau. Ki jira har sai bayan kin yaye shi. Ubangiji dai ya cika maganarsa.” Saboda haka matar ta tsaya a gida, ta yi ta renon ɗanta har ta yaye shi.
A vâ Elkanah ni ahawi na tie patetlah sak lawih. Camo sanu na pâphei totouh awm lawih. BAWIPA e lawkkam mah kuep sak telah atipouh. Hatdawkvah Hannah ni a ca sanu a pânei teh sanu pâphei totouh a im vah ao.
24 Bayan ta yaye shi, sai ta ɗauki yaron tare da bijimi bana uku, da mudun gari, da salkan ruwan inabi, ta kawo su a gidan Ubangiji a Shilo.
A ca sanu a pâphei hnukkhu kum thum touh e maitotan buet touh, tavai kawlung buet touh, misurtui um touh hoi a ca hah a ceikhai, camo a nawca rah eiteh, Shiloh e BAWIPA e im dawk a ceikhai.
25 Bayan an yanka bijimin, sai suka kawo yaron wurin Eli.
Maito a thei hnukkhu camo hah Eli koe a thokhai.
26 Sai ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ba ka gane ni ba? Ai, ni ce matar da ta taɓa tsayawa a gabanka, tana addu’a ga Ubangiji.
Hannah ni oe ka bawipa nang na hring e patetlah kai teh yampa vah hete hmuen koe nang koevah, ka kangdue lahoi BAWIPA koe ouk ka ratoum e napui kai hah doeh.
27 Wannan yaron ne na roƙa daga wurin Ubangiji, ya kuwa ba ni abin da na roƙa daga gare shi.
Hete camo ka hmu thai nahan ka ratoum teh ka hei e patetlah Bawipa ni na poe toe.
28 Saboda haka, na ba da shi ga Ubangiji muddin ransa, zai zama na Ubangiji.” A can kuwa ya yi wa Ubangiji sujada.
Hatdawkvah, kai ni BAWIPA koe ka hnawng toe a hring nathung BAWIPA koe hnawng e lah ao toe, a titeh hote hmuen koe BAWIPA hah a bawk.