< 1 Bitrus 1 >

1 Bitrus, manzon Yesu Kiristi, Zuwa ga zaɓaɓɓu na Allah, baƙi a duniya, da suke a warwatse ko’ina a Fontus, Galatiya, Kaffadokiya, Asiya da kuma Bitiniya,
Petelo, Mitumi wang'wa Yesu Kilisto, kua kila nzila nia usambailo, kua iholanigwa, naiakoli ku Ponto ihii, Kugalatia, Kapadokia, Asia ni Bithinia.
2 waɗanda aka zaɓa bisa ga rigyasanin Allah Uba, ta wurin aikin tsarkakewar Ruhu, don biyayya ga Yesu Kiristi, su kuma sami yayyafan jininsa. Alheri da salama su zama naku a yalwace.
Kunsoko auhugu wang'wi Tunda. Tata, kua kogigwa nung'waung'welu, kikulyo lang'wa Yesu Kilisto, nuku sansangilwa Isakami akwe, Ukende utule kitalanyu, nupolo wanyu wongeeleke.
3 Yabo ya tabbata ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi! Cikin jinƙansa mai girma ya ba mu sabuwar haihuwa cikin bege mai rai ta wurin tashin Yesu Kiristi daga matattu,
Itunda Tata wa Mukulu witu Yesu Kilisto akembetwe Mukulu nuaupegwa wakwe nuanakanda, au kupee kutugwa upya, kuugimya nuusali kukiila uuki wang'wa Yesu Kilisto kuhega muashi,
4 da kuma cikin gādon da ba zai taɓa lalacewa, ɓacewa ko koɗewa ba, ajiyayye a sama dominku,
usali nishaukulimansila, shaukutula nikisoita hangi shaukukepa uikilwe kilunde kunsoko anyu.
5 ku waɗanda ta wurin bangaskiya ake kiyayewa ta wurin ikon Allah har yă zuwa ceton da yake a shirye da za a bayyana a ƙarshen lokaci.
Kuuhumi wang'wi Tunda mukusungigwa kukiila uhuili nuuguniki uo nunoneigwe kukunukulwa numatungo ampelo.
6 A kan wannan kuke cike da farin ciki ƙwarai, ko da yake yanzu na ɗan lokaci kuna fuskantar baƙin ciki daga gwaje-gwaje iri-iri.
Lumbiili kua ili, atizemulita kinyauwai itungili. Kitalanyu mumageng'wa aya.
7 Wannan kuwa domin a tabbatar da sahihancin bangaskiyarku ne, wadda ta fi zinariya daraja nesa, ita zinariya kuwa, ko da yake mai ƙarewa ce, akan gwada ta da wuta, domin bangaskiyan nan taku ta jawo muku yabo da girma da ɗaukaka a bayyanar Yesu Kiristi.
Iyi ngi kunsoko uhuili wanyu uhume kugeng'wa, uhuili uo nukite insao kukila idhahabu iyo niliimila mumoto nigema uhuili witu. Iyi ipumila kunsoko uhuili witu uhumi kutuga intendo ninza, ukulu nikulyo nila muuki nuang'wa Yesu Kilisto.
8 Ko da yake ba ku taɓa ganinsa ba, kuna ƙaunarsa; kuma ko da yake ba kwa ganinsa yanzu, kun gaskata shi, kun kuma cika da farin ciki ƙwarai, wanda ya fi gaban faɗi,
Shamumuine kunu mumuloilwe, shamumuine itungili kunu muhuie kutalakue hangi mukite ulumbi nukilinkie, nukua ulumbi nuizuig'we nuukulu nuakigulu.
9 gama kuna samun sakamakon bangaskiyarku, ceton rayukanku ke nan.
Itungili mukusingiilya impelo au huili wanyu, uguniki wa nkolo yanyu.
10 Game da ceton nan, annabawa, waɗanda suka yi maganar alherin da za tă zo gare ku, sun yi bincike mai zurfi, a natse,
Ianyakidagu akuduma, nukukolya uulya nua uguniki uwu, kuukende nauzetula kitalanyu.
11 suna ƙoƙari su san lokaci da kuma yanayin da Ruhun Kiristi da yake cikinsu yana nunawa sa’ad da ya yi faɗi a kan wahalolin Kiristi da kuma ɗaukaka da za tă bi.
Akaduma kulinga izezewiule uuguniki uu nauziziza. Akaduma hangi kulinga matungo ki ung'waung'welu wang'wa Kilisto nukoli mitalao aukuligitya ntuninienso. Ili ailupumila matungo naizawazeaila ung'wandyo kina uagigwi wang'wa Kilisto nuukulu nuuze mutyata.
12 Aka bayyana musu cewa ba kansu ne suke bauta wa ba sai ku, sa’ad da suka yi maganar abubuwan da aka faɗa muku ta wurin waɗanda suka yi muku wa’azin bishara, ta wurin Ruhu Mai Tsarki wanda aka aika daga sama. Ko mala’iku ma suna marmari su ga waɗannan abubuwa.
Ikakunukulwa kuanyakidagu kuza aitumila munkani zizi, hangi singa kunsoko itu, ao mahumo na nkani izi kukiila ao naialetile ulukani lang'wa Kilisto kitalanyu kunzila ang'wa ng'waung'welu nautumilwe kupuma kigulu, inkani izi ingi ataiamalaika akulowa kukunukulwa kitalakwe.
13 Saboda haka, ku shirya kanku don aiki; ku zama masu kamunkai; ku kafa begenku duka a kan alherin da za a ba ku sa’ad da aka bayyana Yesu Kiristi.
Kululo tungi ilino niamahala anyu, mutule miapolo mumasigo anyu, mutula nuugimya nuukendo uo nauletilwa kitalanyu imatungo nakukunukuilwa u Yesu Kilisto.
14 Kamar’ya’ya masu biyayya, kada ku bi mugayen sha’awace-sha’awacen da dā kuke da su sa’ad da kuke rayuwa a cikin jahilci.
Anga iang'enya niakete ikilyo, muleke kutungwa ni nsula izo nai mutyatile imatungo naimukili miagila imahala.
15 Amma kamar yadda wanda ya kira ku yake mai tsarki, haka ku ma sai ku kasance masu tsarki cikin dukan abubuwan da kuke yi;
Kululo anga naimilangilwe nuyu numuza, nunye, mutule miaza, ni ntendo yanyu yihi muikali.
16 gama a rubuce yake cewa, “Ku zama masu tsarki, domin ni mai tsarki ne.”
Kunsoko yandikilwe, mutule miaza, kunsoko unene ni muza.
17 Tun da yake kuna kira ga Uba wanda yake yin wa kowane mutum shari’a bisa ga ayyukansa ba bambanci, sai ku yi rayuwarku a nan kamar baƙi cikin tsoro mai bangirma.
Ang'wi mukitanga “Tata” uyu nuilamula itai kuitumi wa kila umuntu, itumile imatungo na muhinzo ako muuza.
18 Gama kun san cewa ba da abubuwa masu lalacewa kamar azurfa ko zinariya ce aka fanshe ku daga rayuwar banza da kuka karɓa daga kakanni-kakanninku ba,
Mulingile kina singa ai mpia ang'wi dhahabu, maintu nigazika ayo nimugunilwe kupuma muntendo yanyu nia upugu, izo naimimanyisilye kupuma kua tata anyu.
19 sai dai an fanshe ku da jini mai daraja na Kiristi, ɗan rago marar aibi ko lahani.
Kululo mugunilwe nasakami iyi ni kulyo lang'wa Kilisto, anga na nkolo ningila uwilu ni bado.
20 An zaɓe shi kafin halittar duniya, amma an bayyana shi a zamanin ƙarshe saboda ku.
Ukilisto aukoli ka nu ng'wandyo wa unkuloigulu aukili, ingi gwa itungili imahiku aya nampelo wakunukulwa kitalanyu.
21 Ta gare shi ne kuka gaskata da Allah, wanda ya tā da shi daga matattu, aka kuma ɗaukaka shi, ta haka bari bangaskiyarku da begenku su kasance ga Allah.
Mumuhuie Itunda kukiila ng'wenso, ni Tunda aumutyatile kupuma kuashi hangi naumupee ukulu kina uhuili wanyu nugimya wanyu utule kung'wi Tunda.
22 Yanzu da kuka tsarkake kanku ta wurin yin biyayya ga gaskiyan nan, don ku kasance da ƙauna mai gaskiya wa’yan’uwanku, sai ku ƙaunaci juna ƙwarai, daga zuciya.
Mitumile inkolo yanyu kutula nzelu kua ugombi nua tai iyo, kunsoko au lowi nuakinyandugu nuugoloki, kululo ilowi kungulu kupuma munkolo yanyu.
23 Gama an sāke haihuwarku, ba da iri da yake lalacewa ba, sai dai marar lalacewa, ta wurin rayayyiya da kuma madawwamiyar maganar Allah. (aiōn g165)
Malelwa kulukangala laka biili, singa kumbeu nigazika, ingi kupuma kumbeu nisinga igazika, kukiila upanga nulukani lang'wi Tunda nulusagiie. (aiōn g165)
24 Gama, “Dukan mutane kamar ciyawa suke, darajarsu kuma kamar furannin jeji ne; ciyawa takan yanƙwane furannin kuma su kakkaɓe,
Kunsoko, imiili ihi anga imatutu nuukulu wakwe anga iua niti tutu. Itutu linyala iua ligwiza.
25 amma maganar Ubangiji tana nan har abada.” Wannan kuwa ita ce kalmar da aka yi muku wa’azi. (aiōn g165)
Kululo ulukani la mukulu lisiga ikalinakali ulu ailukani nailutanantigwe kitalanyu. (aiōn g165)

< 1 Bitrus 1 >