< 1 Bitrus 4 >
1 Saboda haka, da yake Kiristi ya sha wahala a jikinsa, sai ku ma ku yi wa kanku ɗamara da irin wannan hali, gama wanda ya sha wahala a jikinsa ya gama da zunubi ke nan.
Seeing therefore Christ hath suffered for us in the flesh, arm yourselves likewise with the same thought, that he, who hath mortified the flesh, hath ceased from sin;
2 Ta haka, ba ya sauran rayuwarsa a kan mugayen sha’awace-sha’awacen jiki, sai dai nufin Allah.
that he should no longer live the rest of his time in the flesh according to the lusts of men, but after the will of God.
3 Gama kun ɓata lokaci sosai a dā kuna yin abubuwan da masu bauta gumaka suka zaɓa su yi, kuna rayuwa cikin lalata, sha’awace-sha’awace, buguwa, shashanci, shaye-shaye da kuma bautar gumaka masu banƙyama.
For the time past of our life is sufficient for us to have wrought the will of the Gentiles, walking in lasciviousness, inordinate desires, excess of wine, revellings, drunkenness, and abominable idolatries:
4 Sun yi mamaki da ba kwa haɗa kai da su a yanzu, da ba kwa kutsa kai tare da su cikin irin rayuwar banzan nan, har suna zaginku.
in which they think it strange that ye run not with them into the same excess of riot, and therefore speak evil of you:
5 Amma dole su ba da lissafi gare shi wanda yake a shirye yă shari’anta masu rai da matattu.
who shall give an account to Him, who is ready to judge the living and the dead.
6 Dalilin ke nan da ya sa aka yi wa’azin bishara har ga waɗanda yanzu suke mutattu, don ko da yake an hukunta su a matsayin mutane a batun jiki, amma su rayu ga Allah a batun ruhu.
For to this end was the gospel preached also to them that are dead, that they might be judged indeed according to men in the flesh, but might live according to God in the spirit.
7 Ƙarshen abubuwa duka ya yi kusa. Saboda haka ku kasance masu tunani mai kyau da masu kamunkai don ku iya yin addu’a.
But the end of all things draws nigh: be ye therefore sober, and watch unto prayer:
8 Fiye da kome, ku ƙaunaci juna sosai, domin ƙauna tana rufe zunubai masu ɗumbun yawa.
having above all things fervent love to each other; for love will cover a multitude of sins.
9 Ku riƙa karɓar juna ba da gunaguni ba.
Be hospitable one to another, without grudging;
10 Kowa yă yi amfani da kowace baiwar da ya samu don kyautata wa waɗansu, cikin aminci yana aikata alherin Allah a hanyoyi dabam-dabam.
as every one hath received a gift, imparting it to each other, as good stewards of the manifold grace of God.
11 In wani ya yi magana, ya kamata yă yi ta a matsayin wanda yake magana ainihin kalmomin Allah. In wani yana yin hidima, ya kamata yă yi ta da ƙarfin da Allah ya tanadar, domin a cikin kome a yabi Allah ta wurin Yesu Kiristi. A gare shi ɗaukaka da iko sun tabbata har abada abadin. Amin. (aiōn )
If any one speak, let it be as declaring the oracles of God: if any one minister, let it be as from the power which God affordeth him: that in all things God may be glorified through Jesus Christ, to whom be the glory and dominion for ever and ever. Amen. (aiōn )
12 Abokaina ƙaunatattu, kada ku yi mamakin gwaji mai tsananin da kuke sha, sai ka ce wani baƙon abu ne yake faruwa da ku.
Beloved, be not surprised at the fiery trial coming upon you, which is to try you, as if some strange thing befel you:
13 Sai dai ku yi murna cewa kuna tarayya cikin shan wahalolin Kiristi, domin ku kai ga farin ciki mai yawa sa’ad da aka bayyana ɗaukakarsa.
but rejoice in that ye are partakers in the sufferings of Christ; that, when his glory shall be revealed, ye may also rejoice with exceeding joy.
14 In an zage ku saboda sunan Kiristi, ku masu albarka ne, gama Ruhun ɗaukaka da kuma na Allah yana bisanku.
If ye be reproached for the name of Christ, happy are ye; for the Spirit of glory and of God resteth upon you: and though as to them He is blasphemed, yet as to you He is glorified.
15 In kuna shan wahala, kada yă zama don ku masu kisankai ne ko ɓarayi ko masu wani irin laifi ko kuma masu shisshigi.
But let none of you suffer as a murderer, or as a thief, or as a malefactor, or as an intermeddler with other people's affairs.
16 Amma fa, in kuka sha wahala a matsayin ku Kirista ne, kada ku ji kunya, sai dai ku yabi Allah cewa kuna amsa wannan suna.
But if any suffer as a Christian, let him not be ashamed; but let him glorify God herein.
17 Gama lokaci ya yi da za a fara yi wa iyalin Allah shari’a; in kuwa ya fara da mu, to, me zai faru da waɗanda ba sa biyayya da bisharar Allah?
For the time is coming when judgement is to begin at the house of God: and if at us first, what will be the end of those that obey not the gospel of God?
18 Kuma, “In da ƙyar masu adalci su kuɓuta, me zai faru da marasa tsoron Allah da kuma masu zunubi?”
And if the righteous be saved with difficulty, where shall the ungodly and the sinner appear?
19 Saboda haka, waɗanda suke shan wahala bisa ga nufin Allah ya kamata su danƙa kansu ga Mahaliccinsu mai aminci, su kuma ci gaba da aikata abin da yake daidai.
Wherefore let them, that suffer according to the will of God, commit their souls in well-doing to Him as to a faithful Creator.