< 1 Bitrus 4 >

1 Saboda haka, da yake Kiristi ya sha wahala a jikinsa, sai ku ma ku yi wa kanku ɗamara da irin wannan hali, gama wanda ya sha wahala a jikinsa ya gama da zunubi ke nan.
Christ, then, having suffered for us in the flesh, do you also warm yourselves with the same mind: for he who has suffered in the flesh, has ceased from sin;
2 Ta haka, ba ya sauran rayuwarsa a kan mugayen sha’awace-sha’awacen jiki, sai dai nufin Allah.
so that he no longer lives his remaining time in the flesh, to the lusts of men, but to the will of God.
3 Gama kun ɓata lokaci sosai a dā kuna yin abubuwan da masu bauta gumaka suka zaɓa su yi, kuna rayuwa cikin lalata, sha’awace-sha’awace, buguwa, shashanci, shaye-shaye da kuma bautar gumaka masu banƙyama.
For the time which has passed of life, is sufficient to have wrought the will of the Gentiles, having walked in lasciviousness, lusts, excesses in wine, revelings, carousals, and abominable idolatries.
4 Sun yi mamaki da ba kwa haɗa kai da su a yanzu, da ba kwa kutsa kai tare da su cikin irin rayuwar banzan nan, har suna zaginku.
On which account they wonder that you do not run with them, into the same sink of debauchery, reviling you, --
5 Amma dole su ba da lissafi gare shi wanda yake a shirye yă shari’anta masu rai da matattu.
who shall give account to him who is prepared to judge the living and the dead.
6 Dalilin ke nan da ya sa aka yi wa’azin bishara har ga waɗanda yanzu suke mutattu, don ko da yake an hukunta su a matsayin mutane a batun jiki, amma su rayu ga Allah a batun ruhu.
For, to this end of the gospel was preached to the dead, that they might, indeed, be judged according to men in the flesh, but live according to God in the spirit.
7 Ƙarshen abubuwa duka ya yi kusa. Saboda haka ku kasance masu tunani mai kyau da masu kamunkai don ku iya yin addu’a.
Now the end of all things has approached; be, therefore, sober, and watch to prayer.
8 Fiye da kome, ku ƙaunaci juna sosai, domin ƙauna tana rufe zunubai masu ɗumbun yawa.
And above all things, have fervent love to one another; for love will cover a multitude of sins.
9 Ku riƙa karɓar juna ba da gunaguni ba.
Be hospitable to one another, without murmurings.
10 Kowa yă yi amfani da kowace baiwar da ya samu don kyautata wa waɗansu, cikin aminci yana aikata alherin Allah a hanyoyi dabam-dabam.
Let every one, according as he has received a gift, minister it to the others, as good stewards of the manifold favor of God.
11 In wani ya yi magana, ya kamata yă yi ta a matsayin wanda yake magana ainihin kalmomin Allah. In wani yana yin hidima, ya kamata yă yi ta da ƙarfin da Allah ya tanadar, domin a cikin kome a yabi Allah ta wurin Yesu Kiristi. A gare shi ɗaukaka da iko sun tabbata har abada abadin. Amin. (aiōn g165)
If any one speak, let him speak as the oracles of God: if any one minister, let him do it as from the strength which God supplies; that in all things God may be glorified through Jesus Christ, to whom be the glory and the power for ever and ever. Amen. (aiōn g165)
12 Abokaina ƙaunatattu, kada ku yi mamakin gwaji mai tsananin da kuke sha, sai ka ce wani baƙon abu ne yake faruwa da ku.
Beloved, wonder not at the fiery trial among you, which is come upon you for a trial, as if some strange thing happened to you;
13 Sai dai ku yi murna cewa kuna tarayya cikin shan wahalolin Kiristi, domin ku kai ga farin ciki mai yawa sa’ad da aka bayyana ɗaukakarsa.
but, seeing you partake of the sufferings of Christ, rejoice: that, also, at the revelation of his glory you may rejoice, with exceeding great joy.
14 In an zage ku saboda sunan Kiristi, ku masu albarka ne, gama Ruhun ɗaukaka da kuma na Allah yana bisanku.
If you be reproached for the name of Christ, you are happy; because the Spirit of glory and of God rests upon you.
15 In kuna shan wahala, kada yă zama don ku masu kisankai ne ko ɓarayi ko masu wani irin laifi ko kuma masu shisshigi.
By them, indeed, he is evil spoken of, but by you he is glorified. Wherefore, let none of you suffer as a murderer, or a thief, or a malefactor, or as a meddling person.
16 Amma fa, in kuka sha wahala a matsayin ku Kirista ne, kada ku ji kunya, sai dai ku yabi Allah cewa kuna amsa wannan suna.
However, if any one suffer as a Christian, let him not be ashamed, but let him even glorify God on that account.
17 Gama lokaci ya yi da za a fara yi wa iyalin Allah shari’a; in kuwa ya fara da mu, to, me zai faru da waɗanda ba sa biyayya da bisharar Allah?
Indeed, the time is come that punishment must begin at the house of God; and if it begin first at us, what the end of them who do not obey the gospel of God?
18 Kuma, “In da ƙyar masu adalci su kuɓuta, me zai faru da marasa tsoron Allah da kuma masu zunubi?”
And, if the righteous with difficulty escape, where will the ungodly and the sinner appear!
19 Saboda haka, waɗanda suke shan wahala bisa ga nufin Allah ya kamata su danƙa kansu ga Mahaliccinsu mai aminci, su kuma ci gaba da aikata abin da yake daidai.
Wherefore, then, let those who suffer by the will of God, commit their own lives to him in well doing, as a faithful Creator.

< 1 Bitrus 4 >