< 1 Bitrus 4 >
1 Saboda haka, da yake Kiristi ya sha wahala a jikinsa, sai ku ma ku yi wa kanku ɗamara da irin wannan hali, gama wanda ya sha wahala a jikinsa ya gama da zunubi ke nan.
Therefore, since Christ suffered on our behalf in flesh, arm yourselves also with the same mentality (for the one who has ‘suffered in flesh’ has been made to cease from sin)
2 Ta haka, ba ya sauran rayuwarsa a kan mugayen sha’awace-sha’awacen jiki, sai dai nufin Allah.
so as not to live your remaining time in flesh for human lusts any longer, but for the will of God.
3 Gama kun ɓata lokaci sosai a dā kuna yin abubuwan da masu bauta gumaka suka zaɓa su yi, kuna rayuwa cikin lalata, sha’awace-sha’awace, buguwa, shashanci, shaye-shaye da kuma bautar gumaka masu banƙyama.
Because the time that has passed is plenty for you to have performed the will of the pagans—having walked in lewdness, lusts, drunkenness, revelries, carousings and disgusting idolatries—
4 Sun yi mamaki da ba kwa haɗa kai da su a yanzu, da ba kwa kutsa kai tare da su cikin irin rayuwar banzan nan, har suna zaginku.
in regard to which they are disagreeably surprised at your not running with them into the same flood of debauchery, reviling you;
5 Amma dole su ba da lissafi gare shi wanda yake a shirye yă shari’anta masu rai da matattu.
they will give an account to Him who is ready to judge living and dead
6 Dalilin ke nan da ya sa aka yi wa’azin bishara har ga waɗanda yanzu suke mutattu, don ko da yake an hukunta su a matsayin mutane a batun jiki, amma su rayu ga Allah a batun ruhu.
(which is precisely why dead ones were once evangelized, that they should be judged as men in flesh, to be sure, but that they should live according to God in spirit).
7 Ƙarshen abubuwa duka ya yi kusa. Saboda haka ku kasance masu tunani mai kyau da masu kamunkai don ku iya yin addu’a.
The end of all things has approached; therefore be serious and self-controlled in your praying.
8 Fiye da kome, ku ƙaunaci juna sosai, domin ƙauna tana rufe zunubai masu ɗumbun yawa.
Above all things your love for one another should be constant, because love covers a multitude of sins.
9 Ku riƙa karɓar juna ba da gunaguni ba.
Be hospitable to one another without grumbling.
10 Kowa yă yi amfani da kowace baiwar da ya samu don kyautata wa waɗansu, cikin aminci yana aikata alherin Allah a hanyoyi dabam-dabam.
As each has received a gift, minister it to one another as good administrators of God's varied grace.
11 In wani ya yi magana, ya kamata yă yi ta a matsayin wanda yake magana ainihin kalmomin Allah. In wani yana yin hidima, ya kamata yă yi ta da ƙarfin da Allah ya tanadar, domin a cikin kome a yabi Allah ta wurin Yesu Kiristi. A gare shi ɗaukaka da iko sun tabbata har abada abadin. Amin. (aiōn )
If anyone speaks, let it be as utterances of God. If anyone serves, let it be as from strength as God supplies, so that in all things God may be glorified through Jesus Christ, to whom belong the glory and the dominion throughout the ages. Amen. (aiōn )
12 Abokaina ƙaunatattu, kada ku yi mamakin gwaji mai tsananin da kuke sha, sai ka ce wani baƙon abu ne yake faruwa da ku.
Dear ones, do not be surprised at the fiery trial that has come upon you as a test, as though something strange was happening to you,
13 Sai dai ku yi murna cewa kuna tarayya cikin shan wahalolin Kiristi, domin ku kai ga farin ciki mai yawa sa’ad da aka bayyana ɗaukakarsa.
but to the extent that you share in Christ's sufferings, rejoice, so that at the revelation of His glory you also may rejoice a great deal more.
14 In an zage ku saboda sunan Kiristi, ku masu albarka ne, gama Ruhun ɗaukaka da kuma na Allah yana bisanku.
If you are insulted for the name of Christ, you are blessed, because the Spirit of the glory and of God has come to rest upon you. On their part He is blasphemed, but on your part He is glorified.
15 In kuna shan wahala, kada yă zama don ku masu kisankai ne ko ɓarayi ko masu wani irin laifi ko kuma masu shisshigi.
Now do not any of you suffer as a murderer, or a thief, or an evildoer, or as a meddler in others' affairs;
16 Amma fa, in kuka sha wahala a matsayin ku Kirista ne, kada ku ji kunya, sai dai ku yabi Allah cewa kuna amsa wannan suna.
but if anyone suffers as a Christian, let him not be ashamed, but let him glorify God in this matter.
17 Gama lokaci ya yi da za a fara yi wa iyalin Allah shari’a; in kuwa ya fara da mu, to, me zai faru da waɗanda ba sa biyayya da bisharar Allah?
Because the time has come for judgment to begin at God's house; now if it starts with us, what will be the end of those who keep disobeying the Gospel of God?
18 Kuma, “In da ƙyar masu adalci su kuɓuta, me zai faru da marasa tsoron Allah da kuma masu zunubi?”
Also, ‘If the righteous one is saved with difficulty, where will the godless and sinful person appear?’
19 Saboda haka, waɗanda suke shan wahala bisa ga nufin Allah ya kamata su danƙa kansu ga Mahaliccinsu mai aminci, su kuma ci gaba da aikata abin da yake daidai.
And so let those who suffer according to the will of God entrust their souls to Him in doing good, as to a faithful Creator.