< 1 Bitrus 4 >
1 Saboda haka, da yake Kiristi ya sha wahala a jikinsa, sai ku ma ku yi wa kanku ɗamara da irin wannan hali, gama wanda ya sha wahala a jikinsa ya gama da zunubi ke nan.
Therefore of Christ having suffered in flesh for us, arm ye yourselves also with the same mentality, because he who has suffered in flesh has ceased from sin,
2 Ta haka, ba ya sauran rayuwarsa a kan mugayen sha’awace-sha’awacen jiki, sai dai nufin Allah.
in order to live the remaining time in flesh, no longer by lusts of men, but by the will of God.
3 Gama kun ɓata lokaci sosai a dā kuna yin abubuwan da masu bauta gumaka suka zaɓa su yi, kuna rayuwa cikin lalata, sha’awace-sha’awace, buguwa, shashanci, shaye-shaye da kuma bautar gumaka masu banƙyama.
For enough time of life has past for you to accomplish the will of the Gentiles, having gone in debaucheries, lusts, excesses of wine, revelings, drinking parties, and lawless idolatries.
4 Sun yi mamaki da ba kwa haɗa kai da su a yanzu, da ba kwa kutsa kai tare da su cikin irin rayuwar banzan nan, har suna zaginku.
During which they think it strange of you not running together into the same pouring out of debauchery, while they slander.
5 Amma dole su ba da lissafi gare shi wanda yake a shirye yă shari’anta masu rai da matattu.
Men who will give back an accounting to him who fares readily to judge the living and the dead.
6 Dalilin ke nan da ya sa aka yi wa’azin bishara har ga waɗanda yanzu suke mutattu, don ko da yake an hukunta su a matsayin mutane a batun jiki, amma su rayu ga Allah a batun ruhu.
For good news was preached even to the dead for this, so that they might indeed be judged according to men in flesh, but live according to God in spirit.
7 Ƙarshen abubuwa duka ya yi kusa. Saboda haka ku kasance masu tunani mai kyau da masu kamunkai don ku iya yin addu’a.
But the end of all things has approached. Therefore be serious, and be sober for the prayers.
8 Fiye da kome, ku ƙaunaci juna sosai, domin ƙauna tana rufe zunubai masu ɗumbun yawa.
And above all having fervent love for yourselves, because love will cover a multitude of sins,
9 Ku riƙa karɓar juna ba da gunaguni ba.
stranger-loving toward each other without complaints.
10 Kowa yă yi amfani da kowace baiwar da ya samu don kyautata wa waɗansu, cikin aminci yana aikata alherin Allah a hanyoyi dabam-dabam.
As each has received a gift, serving it for yourselves, as good stewards of the manifold grace of God.
11 In wani ya yi magana, ya kamata yă yi ta a matsayin wanda yake magana ainihin kalmomin Allah. In wani yana yin hidima, ya kamata yă yi ta da ƙarfin da Allah ya tanadar, domin a cikin kome a yabi Allah ta wurin Yesu Kiristi. A gare shi ɗaukaka da iko sun tabbata har abada abadin. Amin. (aiōn )
If any man speaks, as oracles of God. If any man serves, as of ability as God supplies. So that God may be glorified in all things through Jesus Christ, to whom is the glory and the dominion into the ages of the ages. Truly. (aiōn )
12 Abokaina ƙaunatattu, kada ku yi mamakin gwaji mai tsananin da kuke sha, sai ka ce wani baƙon abu ne yake faruwa da ku.
Beloved, ye should not be surprised at the fieriness in you, which occurs for a trial to you, like a strange thing happening to you.
13 Sai dai ku yi murna cewa kuna tarayya cikin shan wahalolin Kiristi, domin ku kai ga farin ciki mai yawa sa’ad da aka bayyana ɗaukakarsa.
But rejoice in so far as ye are partakers in the sufferings of the Christ, so that also at the revealing of his glory ye may rejoice, having exceeding joy.
14 In an zage ku saboda sunan Kiristi, ku masu albarka ne, gama Ruhun ɗaukaka da kuma na Allah yana bisanku.
Blessed are ye if ye are reviled for the name of Christ, because the Spirit of glory and of God rests upon you. From them he is indeed blasphemed, but from you he is glorified.
15 In kuna shan wahala, kada yă zama don ku masu kisankai ne ko ɓarayi ko masu wani irin laifi ko kuma masu shisshigi.
For let not any man of you suffer as a murderer, or a thief, or an evildoer, or as a busybody.
16 Amma fa, in kuka sha wahala a matsayin ku Kirista ne, kada ku ji kunya, sai dai ku yabi Allah cewa kuna amsa wannan suna.
But if as a Christian, let him not be ashamed, but let him glorify God in this regard.
17 Gama lokaci ya yi da za a fara yi wa iyalin Allah shari’a; in kuwa ya fara da mu, to, me zai faru da waɗanda ba sa biyayya da bisharar Allah?
Because the time to begin judgment is from the house of God, and if first from us, what is the end of those who disobey the good news of God?
18 Kuma, “In da ƙyar masu adalci su kuɓuta, me zai faru da marasa tsoron Allah da kuma masu zunubi?”
And if the righteous man is scarcely saved, where will the irreverent and sinful man appear?
19 Saboda haka, waɗanda suke shan wahala bisa ga nufin Allah ya kamata su danƙa kansu ga Mahaliccinsu mai aminci, su kuma ci gaba da aikata abin da yake daidai.
Therefore also let those who suffer according to the will of God entrust their souls as to a faithful Creator by well-doing.