< 1 Bitrus 3 >

1 Haka ma, ku matan aure, ku yi biyayya ga mazanku, domin in waɗansunsu ba su gaskata maganar ba, wataƙila a shawo kansu ba tare da magana ba
Enako, žene, pokorne bodite svojim možem, da, če tudi kateri niso poslušni besedi, pridobé se po vedenji žen brez besede,
2 sa’ad da suka ga rayuwarku mai tsabta da kuma na ladabi.
Ko so videli v strahu sveto vedenje vaše.
3 Kyanku bai kamata yă zama na adon jiki ba, kamar kitso da sa kayan ado na zinariya da kuma sa kaya masu tsada.
Dika vaša ne bodi vnanja, spletanje lâs, in navešanje zlatnine, ali oblačenje kril;
4 Maimakon haka, kyanku ya kamata yă zama ainihi na halinku na ciki, kyan da ba ya koɗewa na tawali’u da kuma na natsattsen ruhu, wanda yake mai daraja a gaban Allah.
Nego skriti človek srca, v neminljivosti krotkega in mirnega duha, kateri je drag pred Bogom.
5 Gama haka matan masu tsarki na dā waɗanda suka sa begensu ga Allah suka yi wa kansu ado. Sun yi wa mazansu biyayya,
Tako namreč so se nekdaj dičile tudi svete žene, katere so upale v Boga, podložne svojim možem;
6 kamar Saratu, wadda ta yi biyayya ga Ibrahim, har ta kira shi maigidanta. Ku’ya’yanta ne mata in kun aikata abin da yake daidai, ba ku kuma ba tsoro dama ba.
Kakor je bila Sara poslušna Abrahamu, imenujoč ga gospoda svojega. Katere otroci ste postale vé, če delate dobro in se ne bojite nobenega strahú.
7 Mazan aure, ku ma, ku yi zaman sanin ya kamata yayinda kuke zama da matanku, ku girmama su a matsayin abokan zama marasa ƙarfi da kuma a matsayin magādan kyautar rai na alheri tare da ku, don kada wani abu yă hana addu’o’inku.
Možjé, enako, živite z njimi po spoznanji, kakor slabšemu orodju ženskemu čast deleč, kakor tudi sodediči milosti življenja, da se ne ovirajo molitve vaše.
8 A ƙarshe, dukanku ku zauna lafiya da juna; ku zama masu juyayi, kuna ƙaunar juna kamar’yan’uwa, ku zama masu tausayi da kuma tawali’u.
Slednjič pa, vsi bodite enodušni, sočutni, bratoljubni, milosrčni, blagovoljni,
9 Kada ku rama mugunta da mugunta ko zagi da zagi, sai dai ku sa albarka, gama ga wannan ne aka kira ku, ku kuma gāji albarka.
Ne vračajoč hudega za hudo, ali psovanja za psovanje; a nasprotno "blagoslavljajoč, vedoč, da ste za to poklicani, da podedovate blagoslov.
10 Gama, “Duk wanda yake so yă ji daɗin rayuwa, yă kuma ga kwanaki masu kyau dole yă ƙame harshensa daga mugunta leɓunansa kuma daga maganar yaudara.
"Kajti kdor hoče življenje ljubiti in videti dobre dni, brzdá naj jezik svoj pred hudim, in ustne svoje, da ne govoré zvijače.
11 Dole yă juye daga mugunta, ya aikata nagarta; dole yă nemi salama yă kuma bi ta.
Ogiblje se naj hudega, in dela naj dobro; išče naj mirú in hodi za njim.
12 Gama idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kunnuwansa kuma suna jin addu’arsu, amma fuskar Ubangiji tana gāba da masu mugunta.”
Ker oči Gospodove so nad pravičnimi in ušesa njegova nad njih molitvami; obličje pa Gospodovo nad njimi, ki delajo hudo."
13 Wa zai yi muku lahani in kun himmantu ga yin nagarta?
In kdo je, da bi vam kaj hudega storil, če postanete posnemalci dobrega?
14 Amma ko da za ku sha wahala saboda abin da yake daidai, ku masu albarka ne. “Kada ku ji tsoron abin da suke tsoro; kada kuma ku firgita.”
Ali ko bi tudi trpeli za pravico, blagor vam! "Strahú pa njih ne bojte se, in ne begajte se;
15 Sai dai a cikin zukatanku ku keɓe Kiristi a matsayin Ubangiji. A kullum, ku kasance a shirye ku ba da amsa ga duk wanda yake neman ku ba da dalilin wannan begen da kuke da shi. Amma ku yi wannan cikin tawali’u da ladabi,
Gospoda pa Boga posvečujte v srcih svojih." Pripravljeni pa bodite vedno na zagovor vsakemu, kateri zahteva od vas odgovora za upanje v vas, s krotkostjo in strahom;
16 tare da lamiri mai kyau, saboda waɗanda suke maganganun banza a kan kyawawan ayyukanku cikin Kiristi su ji kunya da irin ɓata suna da suke yi.
In dobro vest imejte, da se v tem, za kar vas obrekujejo kakor hudodelnike, osramoté, kateri obrekujejo vaše lepo vedenje v Kristusu.
17 Ya fi kyau, in nufin Allah ne, a sha wahala don yin nagarta fiye da yin mugunta.
Kajti bolje, da dobro delajoč, če hoče volja Božja, trpite, nego hudo delajoč;
18 Gama Kiristi ya mutu domin zunubi sau ɗaya tak, mai adalci saboda marasa adalci, don yă kawo ku ga Allah. An kashe shi a cikin jiki, amma an rayar da shi a Ruhu,
Ker tudi Kristus je enkrat za grehe trpel, pravični za krivične, da nas pripelje Bogu; usmrten v mesu, oživljen pa v duhu,
19 ta wurin wanda kuma ya tafi ya yi wa ruhohin da suke a kurkuku wa’azi
V katerem je tudi šel in oznanjal duhovom v ječi,
20 waɗanda dā ba su yi biyayya ba sa’ad da Allah ya jira da haƙuri a kwanaki Nuhu yayinda ake sassaƙa jirgi. A cikinsa mutane kima ne kawai, su takwas, aka kuɓutar ta ruwa,
Kateri so bili nekdaj neposlušni, ko je enkrat potrpežljivost Božja čakala o dnevih Noeta, ko se je napravljala ladija, v katero se je rešilo malo, to je osem duš, po vodi;
21 ruwan nan kuwa kwatancin baftisma ne da yanzu ya cece ku ku ma, ba kawar da dauda daga jiki ba, sai dai yin alkawari na lamiri mai kyau ga Allah. Ya cece ku ta wurin tashin Yesu Kiristi daga matattu,
Čemur podoben tudi zdaj nas rešuje krst (ne mesne nesnage odloga, nego dobre vesti obljuba do Boga), po vstajenji Jezusa Kristusa,
22 wanda ya tafi sama, yana kuma a hannun dama na Allah, mala’iku, mulkoki da kuma masu iko suna masa biyayya.
Kateri je na desnici Božji, po vnebohodu, in podredjeni so mu angeli in oblasti in moči.

< 1 Bitrus 3 >