< 1 Bitrus 3 >
1 Haka ma, ku matan aure, ku yi biyayya ga mazanku, domin in waɗansunsu ba su gaskata maganar ba, wataƙila a shawo kansu ba tare da magana ba
Likewise, ye wives, be submissive to your own husbands; in order that, if any do not believe the word, they shall be gained through the deportment of their wives, without the word;
2 sa’ad da suka ga rayuwarku mai tsabta da kuma na ladabi.
beholding your chaste deportment which is with reverence:
3 Kyanku bai kamata yă zama na adon jiki ba, kamar kitso da sa kayan ado na zinariya da kuma sa kaya masu tsada.
whose beauty, let it not be the external beauty of braiding the hairs, and wearing golds, or putting on of outer garments;
4 Maimakon haka, kyanku ya kamata yă zama ainihi na halinku na ciki, kyan da ba ya koɗewa na tawali’u da kuma na natsattsen ruhu, wanda yake mai daraja a gaban Allah.
but let their beauty be the hidden man of the heart, in the purity of the meek and quiet spirit, which in the sight of God is perfection complete.
5 Gama haka matan masu tsarki na dā waɗanda suka sa begensu ga Allah suka yi wa kansu ado. Sun yi wa mazansu biyayya,
For in this way in olden times the holy wives, the ones having hope toward God, were indeed accustomed to beautify themselves, submissive to their own husbands:
6 kamar Saratu, wadda ta yi biyayya ga Ibrahim, har ta kira shi maigidanta. Ku’ya’yanta ne mata in kun aikata abin da yake daidai, ba ku kuma ba tsoro dama ba.
as Sarah submitted to Abraham, calling him Lord: whose children you have become, doing good, and not fearing any calamity.
7 Mazan aure, ku ma, ku yi zaman sanin ya kamata yayinda kuke zama da matanku, ku girmama su a matsayin abokan zama marasa ƙarfi da kuma a matsayin magādan kyautar rai na alheri tare da ku, don kada wani abu yă hana addu’o’inku.
Likewise, ye husbands, dwelling with the wife according to knowledge, as the weaker vessel, extending to them honor, as indeed the equal heirs of the grace of life; that your prayers should not be hindered.
8 A ƙarshe, dukanku ku zauna lafiya da juna; ku zama masu juyayi, kuna ƙaunar juna kamar’yan’uwa, ku zama masu tausayi da kuma tawali’u.
And finally, all being like-minded, sympathetic, loving the brethren, merciful, humble:
9 Kada ku rama mugunta da mugunta ko zagi da zagi, sai dai ku sa albarka, gama ga wannan ne aka kira ku, ku kuma gāji albarka.
not giving evil for evil, or railing for railing: but on the contrary blessing; because unto this you have been called, that you may inherit the blessing.
10 Gama, “Duk wanda yake so yă ji daɗin rayuwa, yă kuma ga kwanaki masu kyau dole yă ƙame harshensa daga mugunta leɓunansa kuma daga maganar yaudara.
For let the one wishing to love life, and to see good days, cease his tongue from evil, and his lips from speaking guile:
11 Dole yă juye daga mugunta, ya aikata nagarta; dole yă nemi salama yă kuma bi ta.
let him depart from evil, and do good; let him seek peace, and pursue it:
12 Gama idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kunnuwansa kuma suna jin addu’arsu, amma fuskar Ubangiji tana gāba da masu mugunta.”
because the eyes of the Lord are upon the righteous, and his ears are open to their cry: but the face of the Lord is against those doing evil.
13 Wa zai yi muku lahani in kun himmantu ga yin nagarta?
Who is the one about to harm you, if you may be zealots of the good?
14 Amma ko da za ku sha wahala saboda abin da yake daidai, ku masu albarka ne. “Kada ku ji tsoron abin da suke tsoro; kada kuma ku firgita.”
But if indeed you suffer for righteousness' sake, you are happy. Fear not their fear, neither be troubled;
15 Sai dai a cikin zukatanku ku keɓe Kiristi a matsayin Ubangiji. A kullum, ku kasance a shirye ku ba da amsa ga duk wanda yake neman ku ba da dalilin wannan begen da kuke da shi. Amma ku yi wannan cikin tawali’u da ladabi,
but sanctify the Lord Christ in your hearts: being always ready for an answer to every one asking you a reason for the hope which is in you, but with meekness and fear:
16 tare da lamiri mai kyau, saboda waɗanda suke maganganun banza a kan kyawawan ayyukanku cikin Kiristi su ji kunya da irin ɓata suna da suke yi.
having a good conscience, in order that, in whatsoever you are calumniated, those traducing your good deportment in Christ may be ashamed.
17 Ya fi kyau, in nufin Allah ne, a sha wahala don yin nagarta fiye da yin mugunta.
For it is better, doing good, if the will of the Lord should will it, to suffer, rather than doing evil.
18 Gama Kiristi ya mutu domin zunubi sau ɗaya tak, mai adalci saboda marasa adalci, don yă kawo ku ga Allah. An kashe shi a cikin jiki, amma an rayar da shi a Ruhu,
Because Christ indeed once died for our sins, the just for the unjust, that he might bring us to God, indeed being put to death in the flesh, but quickened in spirit:
19 ta wurin wanda kuma ya tafi ya yi wa ruhohin da suke a kurkuku wa’azi
by which also having gone he proclaimed to the spirits in prison;
20 waɗanda dā ba su yi biyayya ba sa’ad da Allah ya jira da haƙuri a kwanaki Nuhu yayinda ake sassaƙa jirgi. A cikinsa mutane kima ne kawai, su takwas, aka kuɓutar ta ruwa,
who at one time were disobedient, when the longsuffering of God waited in the days of Noah, the ark being prepared, in which a few, that is, eight souls were saved through the water.
21 ruwan nan kuwa kwatancin baftisma ne da yanzu ya cece ku ku ma, ba kawar da dauda daga jiki ba, sai dai yin alkawari na lamiri mai kyau ga Allah. Ya cece ku ta wurin tashin Yesu Kiristi daga matattu,
Which antitype baptism does even now save you, not the removal of the filth of the flesh, but the seeking after a good conscience toward God, through the resurrection of Jesus Christ:
22 wanda ya tafi sama, yana kuma a hannun dama na Allah, mala’iku, mulkoki da kuma masu iko suna masa biyayya.
who is on the right hand of God, having gone up into heaven; angels and authorities and powers being subordinated unto him.