< 1 Bitrus 2 >
1 Saboda haka, ku rabu da kowace ƙeta da dukan ruɗu, munafunci, kishi, da kuma kowace irin ɓata suna.
Отже, відкиньте всяке зло, усяке лукавство, лицемірство, заздрощі й усякі наклепи.
2 Kamar sababbin jarirai, ku yi marmarin madara zalla ta ruhaniya, domin ta wurinta za ku yi girma cikin cetonku,
Як новонароджені немовлята, прагніть чистого духовного молока, щоб через нього ви зросли в спасінні,
3 yanzu da kuka ɗanɗana alherin Ubangiji.
якщо ви [дійсно] пізнали, що Господь добрий.
4 Da kuka zo gare shi, rayayyen Dutse, da mutane suka ƙi amma Allah ya zaɓa, kuma mai daraja a gare shi
Підходьте до Нього, живого Каменя, відкинутого людьми, але обраного та дорогоцінного перед Богом.
5 ku ma, a matsayinku na duwatsu masu rai, ana gina ku ga zama gidan ruhaniya don ku zama tsattsarkar ƙungiyar firistoci, kuna miƙa hadayun ruhaniya, abin karɓa ga Allah ta wurin Yesu Kiristi.
І ви, як живе каміння, будуйте з себе духовний дім, щоб [бути] святим священством і через Ісуса Христа приносити духовні жертви, приємні Богові.
6 Gama a cikin Nassi an ce, “Ga shi, na kafa dutse a Sihiyona, zaɓaɓɓen dutse na kusurwar gini mai daraja, wanda kuma ya dogara gare shi ba zai taɓa kunyata ba.”
Бо в Писанні сказано: «Ось Я кладу на Сіоні наріжний Камінь, обраний і коштовний. І хто вірить у Нього, ніколи не буде осоромлений».
7 A gare ku da kuka gaskata, wannan dutse mai daraja ne. Amma ga waɗanda ba su gaskata ba, “Dutsen da magina suka ƙi ya zama dutsen kusurwar gini,
Отже, для вас Він дорогоцінний, бо ви вірите, а для тих, хто не вірить, «Камінь, який відкинули будівничі, став наріжним Каменем»
8 kuma, “Dutse ne da yake sa mutane tuntuɓe kuma fā ne da yake sa su fāɗi.” Sun yi tuntuɓe domin sun ƙi su yi biyayya da saƙon, wanda kuma yake abin da aka ƙaddara musu.
і «Каменем спотикання і Скелею падіння». Вони спотикаються, бо не вірять Слову. Саме для цього вони й призначені.
9 Amma ku zaɓaɓɓu ne, ƙungiyar firistocin babban Sarki, al’umma mai tsarki, jama’a mallakar Allah, domin ku shaida yabon shi wanda ya kira ku daga cikin duhu zuwa haskensa mai banmamaki.
Але ви – рід обраний, царське священство, святий народ, люди, які належать Богові, щоб звіщати величні діла Того, Хто покликав вас із темряви до Свого дивовижного світла.
10 Dā ku ba mutane ba ne, amma yanzu ku mutanen Allah ne; Dā ba ku karɓi jinƙai ba, amma yanzu kun karɓi jinƙai.
Колись ви не [були] народом, але тепер ви Божий народ. Колись ви не [були] помилувані, але тепер помилувані.
11 Abokaina ƙaunatattu, ina roƙonku, a matsayin bare da kuma baƙi a duniya, ku rabu da sha’awace-sha’awacen zunubin da suke yaƙi da ranku.
Любі, закликаю вас як чужинців і мандрівників, стримуватися від плотських лихих бажань, які воюють проти душі.
12 Ku yi irin rayuwa mai kyau a cikin masu bautar gumaka, yadda ko da sun zarge ku da yin laifi, za su iya ganin ayyukanku nagari, su ɗaukaka Allah a ranar da zai ziyarce mu.
Поводьтеся добре серед язичників, щоб ті, хто обмовляє вас, як злочинців, побачивши [ваші] добрі діла, прославили Бога в День приходу.
13 Saboda Ubangiji, ku yi biyayya ga kowace hukumar da aka kafa cikin mutane, ko ga sarki, a matsayi wanda ya fi iko,
Підкоряйтеся всякій людській владі заради Господа – чи цареві, як володарю,
14 ko ga gwamnoni, waɗanda ya aika domin su hukunta masu laifi su kuma yabi masu aikata abin da yake daidai.
чи намісникам, як посланим від Нього, щоб карати злочинців та хвалити тих, хто робить добро.
15 Gama nufin Allah ne cewa ta wurin yin nagarta za ku toshe jahilcin marasa azanci.
Бо така Божа воля, щоб, роблячи добро, ви приборкували неуцтво нерозумних людей.
16 Ku yi rayuwa kamar mutanen da aka’yantar, sai dai kada ku yi amfani da’yancinku a matsayin hujjar aikata mugunta; ku yi rayuwa kamar bayin Allah.
[Живіть] як вільні [люди], не як ті, що використовують свободу для прикриття зла, але як раби Бога.
17 Ku nuna ladabin da ya dace ga kowa. Ku ƙaunaci’yan’uwantakar masu bi, ku ji tsoron Allah, ku girmama sarki.
Шануйте всіх, любіть братерство, бійтеся Бога, шануйте царя.
18 Bayi, ku yi biyayya ga iyayengijinku da matuƙar ladabi, ba kawai ga waɗanda suke da kirki da masu sauƙinkai ba, amma har ga masu zafin rai ma.
Слуги, у повному страху підкоряйтеся не лише добрим і лагідним володарям, але й нечесним.
19 Gama abin yabo ne in mutum ya yi haƙuri cikin zafin wahalar rashin adalci saboda yana sane da Allah.
Тому що це достойне похвали, коли хтось через своє сумління [перед] Богом зносить скорботи, страждаючи несправедливо.
20 Amma ina abin taƙama in kuka sha duka saboda kun yi laifi kuka kuma jimre? Sai dai in kuka sha wahala saboda yin nagari kuka kuma jimre, abin yabo ne a gaban Allah.
Адже яка честь терпіти, коли вас б’ють за провини? Коли ж ви терпите й страждаєте, роблячи добро, – це благодать перед Богом.
21 Ga wannan ne aka kira ku, domin Kiristi ya sha wahala dominku, ya bar muku gurbin da ya kamata ku bi.
До цього ви були покликані, бо і Христос страждав за вас, залишивши вам приклад, щоб ви йшли Його слідами.
22 “Bai taɓa yin laifi ba sam, ba a kuma sami ƙarya a bakinsa ba.”
«Він не вчинив гріха, і в Його устах не було знайдено підступу».
23 Sa’ad da suka zazzage shi, bai rama ba; sa’ad da ya sha wahala, bai yi barazana ba. A maimakon haka, ya miƙa kansa ga wanda yake shari’ar adalci.
Коли Його ображали, Він не ображав; страждаючи, Він не погрожував, але передав [Себе] Тому, Хто судить справедливо.
24 Shi kansa ya ɗauki zunubanmu a jikinsa a kan itace, domin mu mutu ga zunubai mu kuma rayu ga adalci; ta wurin raunukansa ne kuka sami warkarwa.
«Він у Своєму тілі підняв наші гріхи» на хрест, щоб ми, померши для гріхів, жили для праведності; «Його ранами ви зцілені».
25 Gama dā kuna kama da tumakin da suka ɓace, amma yanzu kun dawo ga Makiyayi da kuma Mai lura da rayukanku.
Адже ви були як заблудлі вівці, але тепер повернулися до Пастиря й Єпископа ваших душ.