< 1 Bitrus 2 >

1 Saboda haka, ku rabu da kowace ƙeta da dukan ruɗu, munafunci, kishi, da kuma kowace irin ɓata suna.
Wherefore, laying aside all malice, and all guile and hypocrisies, and envyings, and all evil speaking;
2 Kamar sababbin jarirai, ku yi marmarin madara zalla ta ruhaniya, domin ta wurinta za ku yi girma cikin cetonku,
as newborn babes, earnestly desire the unadulterated milk of the word, that you may grow by it.
3 yanzu da kuka ɗanɗana alherin Ubangiji.
Because, indeed, you have tasted that the Lord is good;
4 Da kuka zo gare shi, rayayyen Dutse, da mutane suka ƙi amma Allah ya zaɓa, kuma mai daraja a gare shi
to whom coming, as to a living stone, rejected indeed by men, but chosen by God, and precious;
5 ku ma, a matsayinku na duwatsu masu rai, ana gina ku ga zama gidan ruhaniya don ku zama tsattsarkar ƙungiyar firistoci, kuna miƙa hadayun ruhaniya, abin karɓa ga Allah ta wurin Yesu Kiristi.
you, also, as living stones, are built up a spiritual temple, a holy priesthood, to offer spiritual sacrifices, most acceptable to God, through Jesus Christ.
6 Gama a cikin Nassi an ce, “Ga shi, na kafa dutse a Sihiyona, zaɓaɓɓen dutse na kusurwar gini mai daraja, wanda kuma ya dogara gare shi ba zai taɓa kunyata ba.”
Wherefore, it is contained in the scripture, "Behold I lay in Zion a chief corner stone, elect, precious: whoever trusts in it, shall not be ashamed."
7 A gare ku da kuka gaskata, wannan dutse mai daraja ne. Amma ga waɗanda ba su gaskata ba, “Dutsen da magina suka ƙi ya zama dutsen kusurwar gini,
To you, then, who trust, it is precious; but to unbelieving-- a stone which the builders rejected, which has become the head of the corner--
8 kuma, “Dutse ne da yake sa mutane tuntuɓe kuma fā ne da yake sa su fāɗi.” Sun yi tuntuɓe domin sun ƙi su yi biyayya da saƙon, wanda kuma yake abin da aka ƙaddara musu.
a stone of stumbling, and a rock of offense. Those who stumble at the word, are disobedient unbelievers, to which, therefore, they were appointed:
9 Amma ku zaɓaɓɓu ne, ƙungiyar firistocin babban Sarki, al’umma mai tsarki, jama’a mallakar Allah, domin ku shaida yabon shi wanda ya kira ku daga cikin duhu zuwa haskensa mai banmamaki.
but you are an elect race, a royal priesthood, a holy nation, a purchased people; that you should declare the perfections of him who has called you from darkness into his marvelous light:
10 Dā ku ba mutane ba ne, amma yanzu ku mutanen Allah ne; Dā ba ku karɓi jinƙai ba, amma yanzu kun karɓi jinƙai.
who formerly were not a people, but now are a people of God; who had not obtained mercy, but now have obtained mercy.
11 Abokaina ƙaunatattu, ina roƙonku, a matsayin bare da kuma baƙi a duniya, ku rabu da sha’awace-sha’awacen zunubin da suke yaƙi da ranku.
Beloved, I beseech you, as sojourners and travelers, abstain from fleshly lusts, which war against the soul.
12 Ku yi irin rayuwa mai kyau a cikin masu bautar gumaka, yadda ko da sun zarge ku da yin laifi, za su iya ganin ayyukanku nagari, su ɗaukaka Allah a ranar da zai ziyarce mu.
Have your behavior comely, among the Gentiles, that, whereas, they speak against you, as evil doers, having beheld your good works, they may glorify God, in the day of visitation.
13 Saboda Ubangiji, ku yi biyayya ga kowace hukumar da aka kafa cikin mutane, ko ga sarki, a matsayi wanda ya fi iko,
Be subject, therefore, to every human establishment for the Lord's sake; whether to the king, as supreme;
14 ko ga gwamnoni, waɗanda ya aika domin su hukunta masu laifi su kuma yabi masu aikata abin da yake daidai.
or to governor, as those sent by him for the punishment, indeed, of evil doers; but for the praise of them who do good.
15 Gama nufin Allah ne cewa ta wurin yin nagarta za ku toshe jahilcin marasa azanci.
For so is the will of God, that, by doing good, you put to silence the ignorance of foolish men.
16 Ku yi rayuwa kamar mutanen da aka’yantar, sai dai kada ku yi amfani da’yancinku a matsayin hujjar aikata mugunta; ku yi rayuwa kamar bayin Allah.
Live as freemen, yet do not use your freedom as a covering of wickedness; but as the servants of God.
17 Ku nuna ladabin da ya dace ga kowa. Ku ƙaunaci’yan’uwantakar masu bi, ku ji tsoron Allah, ku girmama sarki.
Treat all men with respect: love the brotherhood: fear God: honor the king.
18 Bayi, ku yi biyayya ga iyayengijinku da matuƙar ladabi, ba kawai ga waɗanda suke da kirki da masu sauƙinkai ba, amma har ga masu zafin rai ma.
Let household servants be subject to their masters, with all reverence; not only to the good and gentle, but also to the froward.
19 Gama abin yabo ne in mutum ya yi haƙuri cikin zafin wahalar rashin adalci saboda yana sane da Allah.
For this is acceptable, if any one, from conscience of God, sustain sorrows, suffering unjustly.
20 Amma ina abin taƙama in kuka sha duka saboda kun yi laifi kuka kuma jimre? Sai dai in kuka sha wahala saboda yin nagari kuka kuma jimre, abin yabo ne a gaban Allah.
But what praise is due, if, when you commit faults and are buffeted, you bear it patiently? Yet if, when you do well, and suffer, you bear it patiently, this is acceptable with God.
21 Ga wannan ne aka kira ku, domin Kiristi ya sha wahala dominku, ya bar muku gurbin da ya kamata ku bi.
Besides, to this you were called; for even Christ suffered for us, leaving us a pattern, that you should follow his footsteps;
22 “Bai taɓa yin laifi ba sam, ba a kuma sami ƙarya a bakinsa ba.”
who did not sin, neither was guile found in his mouth;
23 Sa’ad da suka zazzage shi, bai rama ba; sa’ad da ya sha wahala, bai yi barazana ba. A maimakon haka, ya miƙa kansa ga wanda yake shari’ar adalci.
who, when he was reviled, did not revile in return; when he suffered he did not threaten, but committed his cause to him who judges righteously--
24 Shi kansa ya ɗauki zunubanmu a jikinsa a kan itace, domin mu mutu ga zunubai mu kuma rayu ga adalci; ta wurin raunukansa ne kuka sami warkarwa.
who himself bore away our sins in his own body, on the tree; that we, being freed from sins, should live to righteousness; by whose stripes you are healed.
25 Gama dā kuna kama da tumakin da suka ɓace, amma yanzu kun dawo ga Makiyayi da kuma Mai lura da rayukanku.
For you were as sheep going astray, but are now returned to the Shepherd, and Overseer of your souls.

< 1 Bitrus 2 >