< 1 Bitrus 1 >

1 Bitrus, manzon Yesu Kiristi, Zuwa ga zaɓaɓɓu na Allah, baƙi a duniya, da suke a warwatse ko’ina a Fontus, Galatiya, Kaffadokiya, Asiya da kuma Bitiniya,
panta-gālātiyā-kappadakiyā-āśiyā-bithuniyādeśeṣu pravāsino ye vikīrṇalokāḥ
2 waɗanda aka zaɓa bisa ga rigyasanin Allah Uba, ta wurin aikin tsarkakewar Ruhu, don biyayya ga Yesu Kiristi, su kuma sami yayyafan jininsa. Alheri da salama su zama naku a yalwace.
piturīśvarasya pūrvvanirṇayād ātmanaḥ pāvanena yīśukhrīṣṭasyājñāgrahaṇāya śoṇitaprokṣaṇāya cābhirucitāstān prati yīśukhrīṣṭasya preritaḥ pitaraḥ patraṁ likhati| yuṣmān prati bāhulyena śāntiranugrahaśca bhūyāstāṁ|
3 Yabo ya tabbata ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi! Cikin jinƙansa mai girma ya ba mu sabuwar haihuwa cikin bege mai rai ta wurin tashin Yesu Kiristi daga matattu,
asmākaṁ prabho ryīśukhrīṣṭasya tāta īśvaro dhanyaḥ, yataḥ sa svakīyabahukṛpāto mṛtagaṇamadhyād yīśukhrīṣṭasyotthānena jīvanapratyāśārtham arthato
4 da kuma cikin gādon da ba zai taɓa lalacewa, ɓacewa ko koɗewa ba, ajiyayye a sama dominku,
'kṣayaniṣkalaṅkāmlānasampattiprāptyartham asmān puna rjanayāmāsa| sā sampattiḥ svarge 'smākaṁ kṛte sañcitā tiṣṭhati,
5 ku waɗanda ta wurin bangaskiya ake kiyayewa ta wurin ikon Allah har yă zuwa ceton da yake a shirye da za a bayyana a ƙarshen lokaci.
yūyañceśvarasya śaktitaḥ śeṣakāle prakāśyaparitrāṇārthaṁ viśvāsena rakṣyadhve|
6 A kan wannan kuke cike da farin ciki ƙwarai, ko da yake yanzu na ɗan lokaci kuna fuskantar baƙin ciki daga gwaje-gwaje iri-iri.
tasmād yūyaṁ yadyapyānandena praphullā bhavatha tathāpi sāmprataṁ prayojanahetoḥ kiyatkālaparyyantaṁ nānāvidhaparīkṣābhiḥ kliśyadhve|
7 Wannan kuwa domin a tabbatar da sahihancin bangaskiyarku ne, wadda ta fi zinariya daraja nesa, ita zinariya kuwa, ko da yake mai ƙarewa ce, akan gwada ta da wuta, domin bangaskiyan nan taku ta jawo muku yabo da girma da ɗaukaka a bayyanar Yesu Kiristi.
yato vahninā yasya parīkṣā bhavati tasmāt naśvarasuvarṇādapi bahumūlyaṁ yuṣmākaṁ viśvāsarūpaṁ yat parīkṣitaṁ svarṇaṁ tena yīśukhrīṣṭasyāgamanasamaye praśaṁsāyāḥ samādarasya gauravasya ca yogyatā prāptavyā|
8 Ko da yake ba ku taɓa ganinsa ba, kuna ƙaunarsa; kuma ko da yake ba kwa ganinsa yanzu, kun gaskata shi, kun kuma cika da farin ciki ƙwarai, wanda ya fi gaban faɗi,
yūyaṁ taṁ khrīṣṭam adṛṣṭvāpi tasmin prīyadhve sāmprataṁ taṁ na paśyanto'pi tasmin viśvasanto 'nirvvacanīyena prabhāvayuktena cānandena praphullā bhavatha,
9 gama kuna samun sakamakon bangaskiyarku, ceton rayukanku ke nan.
svaviśvāsasya pariṇāmarūpam ātmanāṁ paritrāṇaṁ labhadhve ca|
10 Game da ceton nan, annabawa, waɗanda suka yi maganar alherin da za tă zo gare ku, sun yi bincike mai zurfi, a natse,
yuṣmāsu yo 'nugraho varttate tadviṣaye ya īśvarīyavākyaṁ kathitavantaste bhaviṣyadvādinastasya paritrāṇasyānveṣaṇam anusandhānañca kṛtavantaḥ|
11 suna ƙoƙari su san lokaci da kuma yanayin da Ruhun Kiristi da yake cikinsu yana nunawa sa’ad da ya yi faɗi a kan wahalolin Kiristi da kuma ɗaukaka da za tă bi.
viśeṣatasteṣāmantarvvāsī yaḥ khrīṣṭasyātmā khrīṣṭe varttiṣyamāṇāni duḥkhāni tadanugāmiprabhāvañca pūrvvaṁ prākāśayat tena kaḥ kīdṛśo vā samayo niradiśyataitasyānusandhānaṁ kṛtavantaḥ|
12 Aka bayyana musu cewa ba kansu ne suke bauta wa ba sai ku, sa’ad da suka yi maganar abubuwan da aka faɗa muku ta wurin waɗanda suka yi muku wa’azin bishara, ta wurin Ruhu Mai Tsarki wanda aka aika daga sama. Ko mala’iku ma suna marmari su ga waɗannan abubuwa.
tatastai rviṣayaiste yanna svān kintvasmān upakurvvantyetat teṣāṁ nikaṭe prākāśyata| yāṁśca tān viṣayān divyadūtā apyavanataśiraso nirīkṣitum abhilaṣanti te viṣayāḥ sāmprataṁ svargāt preṣitasya pavitrasyātmanaḥ sahāyyād yuṣmatsamīpe susaṁvādapracārayitṛbhiḥ prākāśyanta|
13 Saboda haka, ku shirya kanku don aiki; ku zama masu kamunkai; ku kafa begenku duka a kan alherin da za a ba ku sa’ad da aka bayyana Yesu Kiristi.
ataeva yūyaṁ manaḥkaṭibandhanaṁ kṛtvā prabuddhāḥ santo yīśukhrīṣṭasya prakāśasamaye yuṣmāsu varttiṣyamānasyānugrahasya sampūrṇāṁ pratyāśāṁ kuruta|
14 Kamar’ya’ya masu biyayya, kada ku bi mugayen sha’awace-sha’awacen da dā kuke da su sa’ad da kuke rayuwa a cikin jahilci.
aparaṁ pūrvvīyājñānatāvasthāyāḥ kutsitābhilāṣāṇāṁ yogyam ācāraṁ na kurvvanto yuṣmadāhvānakārī yathā pavitro 'sti
15 Amma kamar yadda wanda ya kira ku yake mai tsarki, haka ku ma sai ku kasance masu tsarki cikin dukan abubuwan da kuke yi;
yūyamapyājñāgrāhisantānā iva sarvvasmin ācāre tādṛk pavitrā bhavata|
16 gama a rubuce yake cewa, “Ku zama masu tsarki, domin ni mai tsarki ne.”
yato likhitam āste, yūyaṁ pavitrāstiṣṭhata yasmādahaṁ pavitraḥ|
17 Tun da yake kuna kira ga Uba wanda yake yin wa kowane mutum shari’a bisa ga ayyukansa ba bambanci, sai ku yi rayuwarku a nan kamar baƙi cikin tsoro mai bangirma.
aparañca yo vināpakṣapātam ekaikamānuṣasya karmmānusārād vicāraṁ karoti sa yadi yuṣmābhistāta ākhyāyate tarhi svapravāsasya kālo yuṣmābhi rbhītyā yāpyatāṁ|
18 Gama kun san cewa ba da abubuwa masu lalacewa kamar azurfa ko zinariya ce aka fanshe ku daga rayuwar banza da kuka karɓa daga kakanni-kakanninku ba,
yūyaṁ nirarthakāt paitṛkācārāt kṣayaṇīyai rūpyasuvarṇādibhi rmuktiṁ na prāpya
19 sai dai an fanshe ku da jini mai daraja na Kiristi, ɗan rago marar aibi ko lahani.
niṣkalaṅkanirmmalameṣaśāvakasyeva khrīṣṭasya bahumūlyena rudhireṇa muktiṁ prāptavanta iti jānītha|
20 An zaɓe shi kafin halittar duniya, amma an bayyana shi a zamanin ƙarshe saboda ku.
sa jagato bhittimūlasthāpanāt pūrvvaṁ niyuktaḥ kintu caramadineṣu yuṣmadarthaṁ prakāśito 'bhavat|
21 Ta gare shi ne kuka gaskata da Allah, wanda ya tā da shi daga matattu, aka kuma ɗaukaka shi, ta haka bari bangaskiyarku da begenku su kasance ga Allah.
yatastenaiva mṛtagaṇāt tasyotthāpayitari tasmai gauravadātari ceśvare viśvasitha tasmād īśvare yuṣmākaṁ viśvāsaḥ pratyāśā cāste|
22 Yanzu da kuka tsarkake kanku ta wurin yin biyayya ga gaskiyan nan, don ku kasance da ƙauna mai gaskiya wa’yan’uwanku, sai ku ƙaunaci juna ƙwarai, daga zuciya.
yūyam ātmanā satyamatasyājñāgrahaṇadvārā niṣkapaṭāya bhrātṛpremne pāvitamanaso bhūtvā nirmmalāntaḥkaraṇaiḥ parasparaṁ gāḍhaṁ prema kuruta|
23 Gama an sāke haihuwarku, ba da iri da yake lalacewa ba, sai dai marar lalacewa, ta wurin rayayyiya da kuma madawwamiyar maganar Allah. (aiōn g165)
yasmād yūyaṁ kṣayaṇīyavīryyāt nahi kintvakṣayaṇīyavīryyād īśvarasya jīvanadāyakena nityasthāyinā vākyena punarjanma gṛhītavantaḥ| (aiōn g165)
24 Gama, “Dukan mutane kamar ciyawa suke, darajarsu kuma kamar furannin jeji ne; ciyawa takan yanƙwane furannin kuma su kakkaɓe,
sarvvaprāṇī tṛṇaistulyastattejastṛṇapuṣpavat| tṛṇāni pariśuṣyati puṣpāṇi nipatanti ca|
25 amma maganar Ubangiji tana nan har abada.” Wannan kuwa ita ce kalmar da aka yi muku wa’azi. (aiōn g165)
kintu vākyaṁ pareśasyānantakālaṁ vitiṣṭhate| tadeva ca vākyaṁ susaṁvādena yuṣmākam antike prakāśitaṁ| (aiōn g165)

< 1 Bitrus 1 >