< 1 Sarakuna 1 >

1 Sa’ad da Sarki Dawuda ya tsufa ya kuma ƙara shekaru, ba ya iya jin ɗumi ko an rufe shi da abin rufuwa.
U A elemakule ae la o Davida ke alii, a ua nui kona mau makahiki, a uhi ae la lakou ia ia me na kapa, aole nae ia i mahana'e.
2 Saboda haka bayinsa suka ce masa, “Bari mu nemi wata budurwa wadda za tă yi wa ranka yă daɗe, sarki hidima, tă kuma kula da shi. Za tă dinga kwanta kusa da ranka yă daɗe, yă ji ɗumi.”
Nolaila, i olelo aku la kana mau kauwa ia ia, E imiia'ku kekahi wahine hou puupaa no kuu haku ke alii; a e ku oia ma ke alo o ke'lii, a e lilo ia i kahu nona, a e moe ia i kou poli, i mahana'e kuu haku ke alii.
3 Suka nemi kyakkyawar yarinya cikin fāɗin Isra’ila, sai suka sami Abishag, mutuniyar Shunam, suka kawo ta wa sarki.
Alaila imi hele ae la lakou i wahine hou maikai ma na aina a pau o ka Iseraela, a loaa ia lakou o Abisaga no Sunama, a alakai ae la lakou ia ia i ke alii.
4 Yarinyar kuwa kyakkyawa ce ƙwarai; ta kuwa lura da sarki, ta kuma yi masa hidima, amma sarki bai yi jima’i da ita ba.
He maikai loa hoi ua wahine la, a lilo ae la ia i kahu malama no ke alii, a lawelawe ae la oia nana, aole nae i ike ke alii ia ia.
5 Adoniya, wanda mahaifiyarsa ce Haggit, ya fito ya ce, “Zan zama sarki.” Saboda haka ya nemi kekunan yaƙi, ya kuma shirya dawakai, tare da mutane hamsin da za su sha gabansa.
Alaila o Adoniia ke keiki a Hagita i hookiekie ae ia ia iho, i iho la, E lilo au i alii: hoomakaukau ae la hoi ia i mau kaa me na kanaka hololio nona iho, a me na kanaka he kanalima e holo imua ona.
6 (A duk rayuwarsa mahaifinsa bai taɓa tsawata masa yă ce, “Me ya sa kake yin haka ba?” Shi kuwa mai kyan gani ne ƙwarai, shi ne aka haifa bayan Absalom.)
Aole hoi i hoonaukiuki ae kona makuakane ia ia i kekahi manawa, i ka ninau ana'e, No ke aha la oe i hana'i pela? a he maikai loa kona kino, a ua hanau ae la kona makuwahine ia ia mamuli iho o Abesaloma.
7 Adoniya ya haɗa baƙi da Yowab ɗan Zeruhiya da kuma Abiyatar firist, suka kuma ba shi goyon baya.
Kamailio ae la oia me Ioaba ke keiki a Zeruia, a me Abiatara ke kahuna, a kokua ae la laua mamuli o Adoniia.
8 Amma Zadok firist, Benahiya ɗan Yehohiyada, annabi Natan, Shimeyi, Reyi da kuma matsara na musamman na Dawuda ba su bi Adoniya ba.
Aka, o Zadoka, a me Benaia ke keiki a Iehoiada, a me Natana ke kaula, a me Simei, a me Rei, a me ka poe kanaka koa o Davida, aole lakou me Adoniia.
9 Wata rana Adoniya ya tafi Dutsen Zohelet kusa da En Rogel, inda ya yi hadayar tumaki, da shanun noma, da shanun da ake kiwo a gida. Ya kuma gayyaci’yan’uwansa, wato, sauran’ya’yan Sarki Dawuda, tare da dukan dattawan sarki da suka fito daga Yahuda,
Pepehi iho la o Adoniia i na hipa a me na bipi kauo, a me na bipi kupaluia, ma ka pohaku o Zoheleta, e pili ana i ka punawai Rogela, a kii aku la oia i kona mau hoahanau a pau, i na keiki a ke alii, a me na kanaka a pau o Iuda na kauwa a ke alii.
10 amma bai gayyaci annabi Natan, ko Benahiya, ko wani daga matsara na musamman, ko kuwa ɗan’uwansa Solomon ba.
Aka, o Natana ke kaula, a me Benaia, a me na kanaka koa, a me Solomona kona kaikaina, kana i kii ole aku ai.
11 Sai Natan ya ce wa Batsheba, mahaifiyar Solomon, “Ki san cewa Adoniya, ɗan Haggit, ya zama sarki ba tare da sanin ranka yă daɗe, sarkinmu Dawuda ba?
Nolaila olelo ae la o Natana ia Bateseba i ka makuwahine o Solomona, i ae la, aole anei oe i lohe e alii ana o Adoniia, ke keiki a Hagita, aole hoi i ike ke kakou haku o Davida.
12 Yanzu bari in ba ki shawara yadda za ki cece ranki da kuma ran ɗanki Solomon.
Ano hoi ea, e ao aku au ia oe, i hiki ia oe ke malama i kou ola nei, a me ke ola o kau keiki o Solomona.
13 Ki shiga wurin Sarki Dawuda ki ce masa, ‘Ranka yă daɗe sarki, ba ka rantse mini ni baiwarka cewa, “Tabbatacce Solomon ɗanka ne zai zama sarki bayana, yă kuma zauna a kujerar sarautar ba”? To, me ya sa Adoniya ya zama sarki?’
E hele oe a e komo aku i ke alii Davida, a e olelo aku ia ia, Aole anei oe i hoohiki up kau kauwawahine, e kuu haku ke alii, i ka i ana mai, Oiaio e alii ana o Solomona o kau keiki mahope iho o'u, a e noho oia maluna o ko'u nohoalii? No ke aha la hoi e alii nei o Adoniia?
14 Yayinda kike can kina magana da sarki, zan shiga in kuma tabbatar da abin da kika faɗa.”
Aia hoi, i kou kamailio ana malaila me ke alii, owau no kekahi e komo ae mamuli ou e hooiaio i kau mau olelo.
15 Saboda haka Batsheba ta je don tă ga sarki. A yanzu dai sarki ya tsufa, yana nan kuma a cikin ɗakinsa, inda Abishag mutuniya Shunam take masa hidima.
Alaila komo ae la o Bateseba i ke alii i kona keena, he elemakule loa ke alii; a malama ae la o Abisaga no Sunama i ke alii.
16 Batsheba ta rusuna ta kuma durƙusa a gaban sarki. Sai sarki ya tambaye ta ya ce, “Me kike so?”
Kulou iho la o Bateseba, me ka hoomaikai aku i ke alii. I mai la hoi ke alii, He aha kau?
17 Ta ce masa, “Ranka yă daɗe, kai kanka ka rantse mini ni baiwarka da sunan Ubangiji Allahnka cewa, ‘Solomon ɗanka zai zama sarki bayana, zai kuma zauna a kujerar sarautata.’
I aku la hoi oia ia ia, E kuu haku, ua hoohiki oe ma o Iehova la kou Akua no kau kauwawahine, Oiaio e alii no Solomona kau keiki mahope iho o'u, a e noho oia maluna o ko'u nohoalii.
18 Amma yanzu Adoniya ya zama sarki, kai kuwa ranka yă daɗe sarki, ba ka san wani abu game da shi ba.
Aia hoi, ano, e alii ana o Adoniia, eia hoi, e kuu Haku ke alii, aole oe i ike.
19 Ya miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa, ya kuma gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da Abiyatar firist, da Yowab shugaban mayaƙa, amma bai gayyaci Solomon bawanka ba.
Ua pepehi ae la oia i na bipi kauo, a me na bipi kupaluia, a me na hipa he nui, a ua kii ae hoi oia i na keiki a pau a ke alii a me Abiatara ke kahuna, a me Ioaba ka luna o ka poe koa, aka, o Solomona kau kauwa, kana i kii ole aku ai.
20 Ranka yă daɗe sarki, idanun dukan Isra’ila suna a kanka, domin su san wa zai zauna a kujerar ranka yă daɗe sarkina, a bayanka.
A o oe, e kuu haku ke alii, ke kau nei na maka o ka Iseraela a pau maluna ou, e hai aku oe ia lakou i ka mea e noho maluna o ka nohoalii o kuu haku ke alii, mahope iho ona.
21 In ba haka, bayan an binne ranka yă daɗe sarki, tare da kakanninsa, za a wulaƙance ni da Solomon ɗana, kamar masu laifi.”
A i ole ia, eia paha, aia hiamoe kuu haku ke alii me kona mau makua, alaila e kapaia auanei maua me ka'u keiki Solomona he mau mea hewa.
22 Yayinda take cikin magana tare da sarki, sai annabi Natan ya iso.
Aia hoi, i kona kamailio ana me ke alii, komo ae la o Natana ke kaula.
23 Sai aka faɗa wa sarki, “Ga annabi Natan.” Da Natan ya je gaban sarki, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
Hai aku la lakou i ke alii, i aku la, Eia'e, o Natana ke kaula. A komo ia imua i ke alo o ke alii, kulou iho la ia imua o ke alii ilalo kona alo i ka honua.
24 Natan ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki, ko ka furta cewa Adoniya ne zai zama sarki a bayanka, yă kuma zauna a kujerar sarautarka?
I aku la hoi o Natana, E kuu haku ke alii, ua olelo anei oe, E alii ana o Adoniia mahope iho o'u. a e noho oia maluna o ko'u nohoalii?
25 Yau ya gangara, ya kuma miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa. Ya gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da shugaban mayaƙa, da kuma Abiyatar firist. A yanzu haka suna ci, suna sha, tare da shi, suna cewa, ‘Ran Sarki Adoniya yă daɗe!’
No ka mea, ua iho aku oia i keia la a ua pepehi i na bipi kauo a me na bipi kupaluia, a me na hipa, he nui loa, a ua hea aku oia i na keiki a pau a ke alii, a me na luna o ka poe koa, a me Abiatara, ke kahuna, aia hoi, ke ai nei lakou ke inu nei hoi imua ona, me ka olelo aku, E ola ke alii, o Adoniia.
26 Amma bai gayyace ni bawanka, da Zadok firist, da Benahiya ɗan Yehohiyada, da kuma bawanka Solomon ba.
Aka, owau nei, owau o kau kauwa nei, a me Zadoka ke kahuna, a me Benaia ke keiki a Iehoiada, a me Solomona kau kauwa kana i kahea ole mai ai.
27 Ranka yă daɗe, sarki, ko ka tabbatar da haka, amma ba ka ko faɗa wa fadawanka, cewa ga wanda zai gāje Ranka yă daɗe, sarki ba?”
Ua hanaia anei keia mea e kuu haku ke alii, aole hoi oe i hoike mai i kau kauwa nei, i ka mea e noho maluna o ka nohoalii o kuu haku ke alii mahope iho ona?
28 Sai Dawuda ya ce, “Kira Batsheba tă shiga.” Sai ta zo gaban sarki ta kuma tsaya a gabansa.
Alaila olelo mai la ke alii Davida, i mai la, E kahea aku ia Bateseba io'u nei. A hele mai ia imua i ke alo o ke alii, a ku iho la ia imua o ke alii.
29 Sai sarki ya yi rantsuwa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya cece ni daga kowace damuwa,
Hoohiki iho la ke alii, i mai la, Ma ke ola o Iehova, ka mea nana kuu uhane i hoopakele ae mailoko ae o ka popilikia a pau,
30 tabbatacce a yau zan aikata abin da na yi miki rantsuwa da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila; Solomon ɗanki zai zama sarki bayana, kuma shi zai zauna a kan kujerar sarautata a maimakona.”
E like me ko'u hoohiki ana nou, ma o Iehova la ke Akua o Iseraela, peneia, Oiaio, e alii ana no o Solomona kau keiki, mahope iho o'u, a e noho oia maluna o ko'u nohoalii, ma ko'u hakahaka; pela io no wau e hana aku ai i keia la.
31 Sai Batsheba ta rusuna da fuskarta har ƙasa, ta kuma durƙusa a gaban sarki ta ce, “Bari ran Sarkina Dawuda yă daɗe, har abada!”
Alaila kulou iho la o Bateseba ilalo ke alo i ka honua, a hoomaikai aku la i ke alii, me ka olelo aku, E ola mau loa kuu haku ke alii Davida.
32 Sarki Dawuda ya ce, “Ku kira mini Zadok firist, annabi Natan, da Benahiya ɗan Yehohiyada.” Da suka zo gaban sarki,
I mai la hoi ke alii Davida, E kahea aku ia Zadoka io'u nei ke kahuna, a me Natana ke kaula, a me Benaia ke keiki a Iehoiada. A hele mai la lakou imua i ke alo o ke alii.
33 sai ya ce musu, “Ku ɗauki bayin sarki tare da ku, ku kuma sa ɗana Solomon a kan dokina, ku gangara da shi zuwa Gihon.
I mai la hoi ke alii ia lakou, E lawe pu me oukou i na kauwa a ko oukou haku, a e hooholo ia Solomona ka'u keiki maluna iho o kuu hoki, a e lawe ia ia i Gihona.
34 A can ku sa Zadok firist, da annabi Natan su shafe shi sarki a bisa Isra’ila. Ku busa ƙaho, ku kuma yi ihu, kuna cewa, ‘Ran Sarki Solomon yă daɗe!’
A na Zadoka ke kahuna, a me Natana ke kaula ia e poni i alii maluna o ka Iseraela: e hookani oukou i ka pu, a e olelo aku, E ola ke alii Solomona.
35 Sa’an nan ku haura tare da shi, zai kuwa zo yă zauna a kujera sarautata, yă yi mulki a maimakona. Na naɗa shi mai mulki a bisa Isra’ila da Yahuda.”
Alaila e hele mai oukou mamuli ona, i hele mai oia e noho maluna o ko'u nohoalii; no ka mea, e lilo oia i alii ma ko'u hakahaka, a ua hoomaopopo ae nei au ia ia i alii maluna o Iseraela a maluna hoi o Iuda.
36 Benahiya ɗan Yehohiyada ya amsa wa sarki, ya ce, “Amin! Bari Ubangiji Allah na ranka yă daɗe sarkina, yă tabbatar da haka.
Alaila olelo aku la o Benaia ke keiki a Iehoiada i ke alii, i aku la, Amene; a e olelo hoi pela Iehova ke Akua o kuu haku ke alii.
37 Kamar yadda Ubangiji ya kasance da ranka yă daɗe, sarki, haka ma bari yă kasance da Solomon, yă kuma mai da kujerar sarautarsa tă fi kujerar sarautar ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, girma!”
Me Iehova i noho pu ai me kuu haku ke alii, pela e noho pu ai oia me Solomona, a e hoonui ae i kona nohoalii i ka nohoalii o kuu haku ke alii Davida.
38 Sai Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa suka gangara, suka sa Solomon a kan dokin Sarki Dawuda, suka raka shi zuwa Gihon.
Alaila hele aku la Zadoka ke kahuna, a me Natana ke kaula, a me Benaia ke keiki a Iehoiada, a me na Kereta a me na Pelita a hooholo lakou ia Solomona maluna o ka hoki o ke alii o Davida, a lawe ae la lakou ia ia i Gihona.
39 Zadok firist ya ɗauki ƙahon mai daga tenti mai tsarki, ya shafe Solomon. Sa’an nan suka busa ƙaho, sai dukan mutane suka yi ihu, suna cewa “Ran Sarki Solomon yă daɗe!”
Lawe ae la o Zadoka ke kahuna i ka pepeiaohao aila mailoko ae o ka halelewa, a poni ae la ia Solomona. A hookani ae la lakou i ka pu; i ae la hoi na kanaka a pau, E ola ke alii Solomona.
40 Dukan mutane kuwa suka haura suka bi shi, suna busan sarewa, suna farin ciki sosai, har ƙasa ta girgiza saboda sowa.
A hoi mai la na kanaka a pau mamuli ona, hookiokio ae la na kanaka me na ohe, a hauoli ae la lakou me ka olioli nui, a haalulu ae la ka honua i ko lakou leo.
41 Adoniya tare da dukan baƙin da suke tare da shi kuwa suka ji wannan sa’ad da suke gama bikinsu. Da jin busan ƙaho, sai Yowab ya yi tambaya, ya ce, “Me ya jawo surutu haka a birni?”
Lohe ae la hoi o Adoniia a me na hoaai a pau me ia, i ka pau ana o ka lakou ahaaina. A lohe o Ioaba i ke kani ana o ka pu, i ae la ia, No ke aha la keia walaau ana o ke kulanakauhale haunaele?
42 Tun yana cikin magana, sai Yonatan ɗan Abiyatar ya iso. Adoniya ya ce, “Shigo! Ai, mutumin kirki irinka, lalle ka kawo labari mai daɗi ne.”
A i kana olelo ana, aia hoi, hiki ae la o Ionatana ke keiki a Abiatara, ke kahuna: i mai la o Adoniia ia ia, E komo mai oe, no ka mea, he kanaka ikaika no oe, a ke lawe mai nei oe i ka olelo maikai.
43 Yonatan ya ce wa Adoniya, “A ina! Ranka yă daɗe, Sarkinmu Dawuda ya naɗa Solomon sarki.
Alaila olelo ae la o Ionatana, i ae la ia Adoniia, Oiaio, ua hoolilo ae nei ko kakou haku ke alii o Davida ia Solomona i alii.
44 Sarki ya aika shi tare da Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa, suka sa shi a kan dokin sarki,
A ua hoouna ke alii me ia ia Zadoka ke kahuna, a me Natana ke kaula, a me Benaia ke keiki a Iehoiada, a me na Kereta, a me na Pelita, a ua hooholo lakou ia ia maluna o ka hoki a ke alii.
45 Zadok firist kuwa da annabi Natan sun shafe shi sarki a Gihon. Daga can suka haura suna kirari, birni kuwa ta ɓarke da sowa. Surutun da kake ji ke nan.
A ua poni ae la o Zadoka ke kahuna, a me Natana ke kaula ia ia i alii ma Gihona, a ua hoi mai lakou mailaila mai e hauoli ana, i halulu ai ke kulanakauhale. Oia ka walaau a oukou i lohe ai.
46 Ban da haka ma, Solomon ne sarki yanzu.
Ke noho nei no hoi o Solomona maluna o ka nohoalii o ke aupuni.
47 Yanzu haka, fadawa sun zo suna wa ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, sam barka, suna cewa, ‘Bari Allahnka yă sa sunan Solomon yă zama sananne fiye da naka, bari kuma sarautarsa tă fi taka girma!’ Sarki kuwa ya rusuna, ya yi sujada a kan gadonsa
A ua hele mai hoi na kauwa a ke alii e hoomaikai i ko kakou haku ke alii Davida, e i ana, E hoonui ke Akua i ka maikai o ka inoa o Solomona i kou inoa, a e hoopakela i kona nohoalii mamua o kou nohoalii. A kulou iho ke alii maluna iho o kona wahi moe.
48 ya ce, ‘Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bar idanuna suka ga magāji a kan kujerar sarautata a yau.’”
Peneia hoi i olelo mai ai ke alii, E hoomaikaiia o Iehova ke Akua o Iseraela ka mea nana i haawi mai i keia la e noho kekahi maluna o ko'u nohoalii, a e ike ana hoi kuu mau maka.
49 A nan fa, dukan baƙin Adoniya suka taso da rawar jiki suka watse.
Makau iho la na hoaai a pau na mea me Adoniia, ku ae la lakou a hele kela kanaka keia kanaka i kona wahi e hele ai.
50 Amma Adoniya, don tsoron Solomon, ya je ya kama ƙahon bagade ya riƙe.
Makau iho la hoi o Adoniia imua o Solomona, ku ae la ia, a hele aku, a lalau ae la i na pepeiaohao o ke kuahu.
51 Sa’ad da aka faɗa wa Solomon cewa, “Adoniya yana tsoron Sarki Solomon, kuma ya manne wa ƙahonin bagade. Yana cewa, ‘Bari Sarki Solomon yă rantse mini a yau cewa ba zai kashe bawansa da takobi ba.’”
Ua haiia mai ia Solomona peneia, Aia hoi, ke makau mai nei o Adoniia i ke alii ia Solomona, no ka mea, ea, ua lalau oia i na pepeiaohao o ke kuahu, e olelo ana, E hoohiki ke alii Solomona no'u i keia la, aole ia e pepehi mai i kana kauwa me ka pahikaua.
52 Solomon ya amsa ya ce, “In ya nuna kansa mai biyayya, ba gashin kansa da zai fāɗi ƙasa; amma in aka same mugunta a cikinsa, zai mutu.”
Olelo mai la hoi o Solomona, Ina e hoike oia ia ia iho he kanaka hoopono, aole e haule i ka honua kekahi oho ona, aka, ina i loaa ka hewa iloko ona, e make no ia.
53 Sai Sarki Solomon ya aiki mutane, suka kuma sauko da shi daga bagade. Adoniya kuwa ya zo, ya rusuna wa Sarki Solomon, sai Solomon ya ce, “Tafi gidanka.”
Alaila hoouna ae la ke alii Solomona, a lawe mai lakou ia ia mailuna mai o ke kuahu. Hele mai la ia a kulou iho la i ke alii ia Solomona, a olelo mai la Solomona ia ia, E hele oe i kou hale.

< 1 Sarakuna 1 >