< 1 Sarakuna 9 >

1 Sa’ad da Solomon ya gama ginin haikalin Ubangiji da kuma fadan sarki, ya kuma yi dukan abin da yake so yă yi,
И бысть егда сконча Соломон зиждяй храм Господень и дом царев и всякое дело свое Соломон, елика восхоте сотворити,
2 sai Ubangiji ya bayyana gare shi sau na biyu, kamar yadda ya bayyana masa a Gibeyon.
и явися Господь Соломону вторицею, якоже явися ему в Гаваоне,
3 Ubangiji ya ce masa, “Na ji addu’arka da kuma roƙon da ka yi a gabana; na tsarkake wannan haikali wanda ka gina, ta wurinsa Sunana zai kasance a can har abada. Idanuna da zuciyata kullum za su kasance a can.
и рече к нему Господь: услышах глас молитвы твоея и моления твоего, имже молился еси предо Мною: сотворих ти по всей молитве твоей, и освятих храм сей, егоже создал еси, еже положити имя Мое тамо во веки, и будут очи Мои ту и сердце Мое во вся дни:
4 “Kai kuwa, in ka yi tafiya a gabana da mutunci a zuci da kuma gaskiya, kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, ka yi dukan abin da na umarta, ka kuma yi biyayya da ƙa’idodina da kuma dokokina,
и ты аще пойдеши предо Мною, якоже ходи Давид отец твой в преподобии сердца и в правоте, и еже творити по всем, яже заповедах ему, и повеления Моя и заповеди Моя сохраниши:
5 zan kafa kujerar sarautarka a bisa Isra’ila har abada, kamar yadda na alkawarta wa Dawuda mahaifinka sa’ad da na ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani a kan kujerar sarautar Isra’ila ba.’
и возставлю престол царствия твоего во Израили во веки, якоже глаголах к Давиду отцу твоему, глаголя: не оскудеет ти муж властелин во Израили:
6 “Amma in kai, ko’ya’yanka maza, suka juye daga gare ni, ba ku kuma kiyaye umarnai da ƙa’idodin da na ba ku ba, kuka yi gaba, kuka bauta wa waɗansu alloli, kuka kuma yi musu sujada,
аще же отвращающеся отвратитеся вы и чада ваша от Мене и не сохраните заповедий Моих и повелений Моих, яже даде Моисей пред вами, и пойдете и поработаете богом иным и поклонитеся им:
7 sai in yanke mutanen Isra’ila daga ƙasar da na ba su, in kuma ƙi wannan haikalin da na tsarkake domin Sunana. Isra’ila kuwa za tă zama abin gori da abin dariya a cikin dukan mutane.
и изрину Израиля из земли, юже дах им, и храм сей, егоже освятих имени Моему, отвергу от лица Моего: и будет Израиль в погубление и во глаголание всем людем:
8 Wannan haikali zai zama tarin juji. Duk wanda ya wuce ta hanyan nan kuwa zai ji tausayi, yă kuma yi tsaki yana cewa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka ga wannan ƙasa da kuma wannan haikali?’
и дом сей будет высокий, всяк преходяй сквозе его ужаснется, и возсвищет и речет: чесо ради сотвори Господь тако земли сей и храму сему?
9 Mutane za su amsa su ce, ‘Saboda sun yashe Ubangiji Allahnsu, wanda ya fitar da su daga Masar, suka rungumi waɗansu alloli, suna yin musu sujada, suna bauta musu ne, ya sa Ubangiji ya kawo dukan masifan nan a kansu.’”
И рекут: понеже оставиша Господа Бога своего, иже изведе отцы их из Египта, из дому работы, и прияша боги чуждыя, и поклонишася им, и поработаша им, сего ради наведе на ня Господь зло сие.
10 A ƙarshen shekaru ashirin da Solomon ya ɗauka yana gina haikalin Ubangiji da fadan sarki,
И бысть по двадесяти летех, в няже созда Соломон два домы, храм Господень и дом царев,
11 sai Sarki Solomon ya ba wa Hiram sarkin Taya garuruwa ashirin a yankin Galili, gama Hiram ya tanada masa da dukan katakai al’ul da na fir, da kuma zinariyar da ya bukaci domin aiki.
Хирам царь Тирский помогаше Соломону древы кедрскими и древы певговыми и златом и всем хотением его: тогда даде Соломон Хираму двадесять градов в земли Галилейстей.
12 Amma sa’ad da Hiram ya zo daga Taya don yă ga garuruwan da Solomon ya ba shi, sai bai ji daɗi ba.
И изыде Хирам из Тира и пойде в Галилею видети грады, яже даде ему Соломон: и не быша ему угодни,
13 Sai ya ce, “Wanda irin garuruwa ke nan ka ba ni, ɗan’uwana?” Saboda haka ya kira su Ƙasar Kabul, sunan da suke da shi har wa yau.
и рече: что гради сии, яже дал ми еси, брате? И нарече я предел (Хавуль), до днешняго дне.
14 Hiram kuwa ya aika wa sarki talenti 120 na zinariya.
И принесе Хирам Соломону сто и двадесять талант злата.
15 Ga lissafin ma’aikatan gandun da Sarki Solomon ya ɗauka don ginin haikalin Ubangiji, da fadarsa, da madogaran gini, da katangar Urushalima, da kuma Hazor Megiddo da Gezer.
Сие же есть число даяния еже принесе царь Соломон, да созиждет храм Господень и дом царев, и Мелон и стену Иерусалимску и Краеградие еже оградити стену града Давидова, и Асур и Магедо и Газер.
16 (Fir’auna sarkin Masar ya kai wa Gezer hari, ya kuma ci ta da yaƙi. Ya sa mata wuta, ya kashe Kan’aniyawanta mazaunan wurin, ya kuma ba da ita a matsayin kyautar aure ga’yarsa, matar Solomon.
Фараон царь Египетский взыде и взя Газер и сожже и огнем, и Ханаана живущаго во граде том погуби: и даде его в дар дщери своей, жене Соломони.
17 Solomon kuwa ya sāke gina Gezer.) Ya gina Bet-Horon ta Kwari,
И согради Соломон Газер и Вефорон нижний,
18 da Ba’alat, da Tadmor a hamada, na cikin ƙasarsa.
и Валааф и Фамор в пустыни.
19 Haka kuma ya gina dukan biranen ajiyarsa, da garuruwa domin kekunan yaƙinsa, da garuruwa domin dawakansa. Ya gina duk abin da ya so yă ginawa a Urushalima, da Lebanon, da kuma ko’ina a dukan yankin da ya yi mulki.
И вся грады крепкия, иже быша Соломону, и вся грады, идеже бяху колесницы, и вся грады, идеже бяху конницы его, и все еже бысть угодно царю Соломону, созда во Иерусалиме, и в Ливане и во всей земли царства своего.
20 Dukan Amoriyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa da Yebusiyawan da suka ragu a ƙasar (waɗanda ba Isra’ilawa ba ne),
Всех людий оставшихся от Аморреа и Хеттеа, и Ферезеа и Хананеа, и Евеа и Иевусеа и Гергесеа, не сущих от сынов Израилевых,
21 wato, waɗanda suka ragu a ƙasar, waɗanda Isra’ilawa ba su iya hallakawa ba, su ne Solomon ya ɗauka su zama bayinsa don aikin gandu, kamar yadda yake har wa yau.
сынов их оставшихся по них на земли, ихже не возмогоша сынове Израилевы потребити их, царь Соломон поработи их даяти дань даже до дне сего:
22 Amma Solomon bai mai da Isra’ilawa bayi ba; su ne mayaƙansa, shugabannin gwamnatinsa, dogarawansa, shugabannin sojojinsa, da shugabanninsa na kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙinsa.
от сынов же Израилевых не даде в работу Соломон, яко тии бяху мужие храбрии, и отроцы его, и князи его, и тристаты его, и воеводы колесниц его, и конницы его.
23 Su ne kuma manyan shugabanni masu lura da ayyukan Solomon, su ne shugabanni 550 masu lura da mutanen da suke aiki.
И бяху старейшины приставленным над делы царя Соломона, пять сот пятьдесят повелевающии людем делающым дело.
24 Bayan’yar Fir’auna ta haura daga Birnin Dawuda zuwa fadan da Solomon ya gina mata, sai ya gina madogaran gini.
Дщерь же фараона прейде из града Давидова в дом свой, егоже созда ей Соломон, тогда созда Мелон.
25 Sau uku a shekara Solomon kan miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama a kan bagaden da ya gina wa Ubangiji, yana ƙone turare a gaban Ubangiji haɗe da su, ta haka ya cika abin da ake bukata na haikali.
И приношаше Соломон трижды в год всесожжения и мирныя жертвы на олтарь, егоже созижде Господу, и кадяше фимиам пред Господем: и соверши храм.
26 Sarki Solomon ya kuma gina jiragen ruwa a Eziyon Geber, wadda take kusa da Elot a Edom, a bakin Jan Teku.
И сотвори царь Соломон корабль в Гасионе Гаверстем, иже при Елафе, при устии моря Последняго, в земли Едомстей.
27 Hiram kuwa ya aiki mutanensa, masu tuƙan jirgin ruwa waɗanda suka san teku, don su yi hidima a jerin jiragen ruwa tare da mutanen Solomon.
И посла Хирам на корабли от отрок своих мужы корабелники управляти ведущих море со отроки Соломони:
28 Suka tafi Ofir suka kuma dawo da talenti 420 na zinariya, wanda suka ba wa Sarki Solomon.
и приидоша в Софир, и взяша оттуду злата четыре ста и двадесять талант и принесоша царю Соломону.

< 1 Sarakuna 9 >