< 1 Sarakuna 9 >

1 Sa’ad da Solomon ya gama ginin haikalin Ubangiji da kuma fadan sarki, ya kuma yi dukan abin da yake so yă yi,
Forsothe it was doon, whanne Salomon had perfourmed the bildyng of the hows of the Lord, and the bildyng of the kyng, and al thing that he coueitide, and wolde make,
2 sai Ubangiji ya bayyana gare shi sau na biyu, kamar yadda ya bayyana masa a Gibeyon.
the Lord apperide to Salomon the secunde tyme, as he apperide to hym in Gabaon.
3 Ubangiji ya ce masa, “Na ji addu’arka da kuma roƙon da ka yi a gabana; na tsarkake wannan haikali wanda ka gina, ta wurinsa Sunana zai kasance a can har abada. Idanuna da zuciyata kullum za su kasance a can.
And the Lord seide to hym, Y haue herd thi preier, and thi bisechyng, which thou bisouytist bifor me; Y haue halewid this hows, which thou bildidist, that Y schulde sette there my name with outen ende; and myn iyen and myn herte schulen be there in alle daies.
4 “Kai kuwa, in ka yi tafiya a gabana da mutunci a zuci da kuma gaskiya, kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, ka yi dukan abin da na umarta, ka kuma yi biyayya da ƙa’idodina da kuma dokokina,
Also if thou goist bifore me, as thi fadir yede, in simplenesse of herte, and in equite, and doist alle thingis whiche Y comaundide to thee, and kepist my domes, and my lawful thingis,
5 zan kafa kujerar sarautarka a bisa Isra’ila har abada, kamar yadda na alkawarta wa Dawuda mahaifinka sa’ad da na ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani a kan kujerar sarautar Isra’ila ba.’
Y schal sette the trone of thi rewme on Israel with outen ende, as Y spak to Dauid, thi fadir, and seide, A man of thi kyn schal not be takun awei fro the trone of Israel.
6 “Amma in kai, ko’ya’yanka maza, suka juye daga gare ni, ba ku kuma kiyaye umarnai da ƙa’idodin da na ba ku ba, kuka yi gaba, kuka bauta wa waɗansu alloli, kuka kuma yi musu sujada,
Forsothe if bi turnyng awei ye and youre sones turnen awey, and suen not me, and kepen not myn hestis and cerymonyes, whiche Y settide forth to you, but ye goen, and worschipen alien goddis, and onouren hem `bi outward reuerence,
7 sai in yanke mutanen Isra’ila daga ƙasar da na ba su, in kuma ƙi wannan haikalin da na tsarkake domin Sunana. Isra’ila kuwa za tă zama abin gori da abin dariya a cikin dukan mutane.
Y schal do awei Israel fro the face of the lond which Y yaue to hem; and Y schal caste awei fro my siyt the temple, which Y halewid to my name; and Israel schal be in to a prouerbe and in to a fable, to alle puplis.
8 Wannan haikali zai zama tarin juji. Duk wanda ya wuce ta hanyan nan kuwa zai ji tausayi, yă kuma yi tsaki yana cewa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka ga wannan ƙasa da kuma wannan haikali?’
And this hows schal be in to ensaumple of Goddis offence; ech man that schal passe bi it, schal wondre, and schal hisse, and schal seye, Whi hath the Lord do thus to this lond, and to this hows?
9 Mutane za su amsa su ce, ‘Saboda sun yashe Ubangiji Allahnsu, wanda ya fitar da su daga Masar, suka rungumi waɗansu alloli, suna yin musu sujada, suna bauta musu ne, ya sa Ubangiji ya kawo dukan masifan nan a kansu.’”
And thei schulen answere, For thei forsoken her Lord God, that ladde the fadris of hem out of Egipt; and thei sueden alien goddis, and worschipiden hem, and onouriden hem; therfor the Lord brouyte in on hem al this yuel.
10 A ƙarshen shekaru ashirin da Solomon ya ɗauka yana gina haikalin Ubangiji da fadan sarki,
Sotheli whanne twenti yeer weren fillid, aftir that Salomon hadde bildid tweyne housis, that is, the hows of the Lord, and the hows of the kyng, while Hiram,
11 sai Sarki Solomon ya ba wa Hiram sarkin Taya garuruwa ashirin a yankin Galili, gama Hiram ya tanada masa da dukan katakai al’ul da na fir, da kuma zinariyar da ya bukaci domin aiki.
kyng of Tire, yaf to Salomon trees of cedre, and of beech, and gold, bi al thing that he hadde nedeful; thanne Salomon yaf to Hiram twenti citees in the lond of Galile.
12 Amma sa’ad da Hiram ya zo daga Taya don yă ga garuruwan da Solomon ya ba shi, sai bai ji daɗi ba.
And Hiram yede out of Tyre that he schulde se the citees, whiche Salomon hadde youe to hym, and tho plesiden not hym;
13 Sai ya ce, “Wanda irin garuruwa ke nan ka ba ni, ɗan’uwana?” Saboda haka ya kira su Ƙasar Kabul, sunan da suke da shi har wa yau.
and he seide, Whethir thes ben the citees, whiche thou, brother, hast youe to me? And he clepide tho citees the lond of Chabul, `til in to this dai.
14 Hiram kuwa ya aika wa sarki talenti 120 na zinariya.
Also Hiram sente to king Salomon sixe score talentis of gold.
15 Ga lissafin ma’aikatan gandun da Sarki Solomon ya ɗauka don ginin haikalin Ubangiji, da fadarsa, da madogaran gini, da katangar Urushalima, da kuma Hazor Megiddo da Gezer.
This is the summe of `costis, which summe Salomon the kyng yaf to bilde the hows of the Lord, and his house Mello, and the wal of Jerusalem, and Ezer, and Maggeddo, and Gazer.
16 (Fir’auna sarkin Masar ya kai wa Gezer hari, ya kuma ci ta da yaƙi. Ya sa mata wuta, ya kashe Kan’aniyawanta mazaunan wurin, ya kuma ba da ita a matsayin kyautar aure ga’yarsa, matar Solomon.
Farao, kyng of Egipt, stiede, and took Gazer, and brente it bi fier; and he killide Chananei, that dwellide in the citee, and yaf it in to dower to his douytir, the wijf of Salomon.
17 Solomon kuwa ya sāke gina Gezer.) Ya gina Bet-Horon ta Kwari,
Therfor Salomon bildide Gazer, and the lower Bethoron,
18 da Ba’alat, da Tadmor a hamada, na cikin ƙasarsa.
and Balaath, and Palmyra in the lond of wildirnesse;
19 Haka kuma ya gina dukan biranen ajiyarsa, da garuruwa domin kekunan yaƙinsa, da garuruwa domin dawakansa. Ya gina duk abin da ya so yă ginawa a Urushalima, da Lebanon, da kuma ko’ina a dukan yankin da ya yi mulki.
and he made strong alle the townes, that perteyneden to hym, and weren with out wal, and the citees of chaaris, and the citees of knyytis, and what euer thing pleside hym to bilde in Jerusalem, and in the Liban, and in al the lond of his power.
20 Dukan Amoriyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa da Yebusiyawan da suka ragu a ƙasar (waɗanda ba Isra’ilawa ba ne),
Salomon made tributaries `til to this dai al the puple, that lefte of Ammorreis, Etheis, and Fereseis, and Eueys, and Jebuseys, that ben not of the sones of Israel,
21 wato, waɗanda suka ragu a ƙasar, waɗanda Isra’ilawa ba su iya hallakawa ba, su ne Solomon ya ɗauka su zama bayinsa don aikin gandu, kamar yadda yake har wa yau.
the sones of these hethen men, that dwelliden in the lond, that is, whiche the sones of Israel myyten not distrye.
22 Amma Solomon bai mai da Isra’ilawa bayi ba; su ne mayaƙansa, shugabannin gwamnatinsa, dogarawansa, shugabannin sojojinsa, da shugabanninsa na kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙinsa.
Sotheli kyng Salomon ordeynede not ony man of the sones of Israel to serue, but thei weren men werriours, and mynystris of him, and princes, and dukis, and prefectis of his chares and horsis.
23 Su ne kuma manyan shugabanni masu lura da ayyukan Solomon, su ne shugabanni 550 masu lura da mutanen da suke aiki.
Sotheli fyue hundrid and fifti `souereynes weren princes ouer alle the werkis of Salomon, whiche princes hadden the puple suget, and comaundiden to werkis ordeyned.
24 Bayan’yar Fir’auna ta haura daga Birnin Dawuda zuwa fadan da Solomon ya gina mata, sai ya gina madogaran gini.
Sotheli the douyter of Farao stiede fro the citee of Dauid in to hir hows, `which hows Salomon hadde bildid to hir; thanne he bildide Mello.
25 Sau uku a shekara Solomon kan miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama a kan bagaden da ya gina wa Ubangiji, yana ƙone turare a gaban Ubangiji haɗe da su, ta haka ya cika abin da ake bukata na haikali.
Also Salomon offride in thre tymes bi alle yeeris brent sacrifices and pesible sacrifices, on the auter which he hadde bildid to the Lord; and he brente encense bifor the Lord, and the temple was performed.
26 Sarki Solomon ya kuma gina jiragen ruwa a Eziyon Geber, wadda take kusa da Elot a Edom, a bakin Jan Teku.
Also king Salomon made `o schip in Asiongaber, which is bisidis Haila, in the brenke of the Reed sea, and in the lond of Idumee.
27 Hiram kuwa ya aiki mutanensa, masu tuƙan jirgin ruwa waɗanda suka san teku, don su yi hidima a jerin jiragen ruwa tare da mutanen Solomon.
And Iram sente in that schip hise seruauntis, schipmen, and kunnynge of the see, with the seruauntis of Salomon;
28 Suka tafi Ofir suka kuma dawo da talenti 420 na zinariya, wanda suka ba wa Sarki Solomon.
and whanne thei hadden come in to Ophir, thei brouyten fro thennus gold of foure hundrid and twenti talentis to kyng Salomon.

< 1 Sarakuna 9 >