< 1 Sarakuna 9 >

1 Sa’ad da Solomon ya gama ginin haikalin Ubangiji da kuma fadan sarki, ya kuma yi dukan abin da yake so yă yi,
And it came to pass when Solomon had finished the building of the house of the Lord, and the king’s house, and all that he desired, and was pleased to do,
2 sai Ubangiji ya bayyana gare shi sau na biyu, kamar yadda ya bayyana masa a Gibeyon.
That the Lord appeared to him the second time, as he had appeared to him in Gabaon.
3 Ubangiji ya ce masa, “Na ji addu’arka da kuma roƙon da ka yi a gabana; na tsarkake wannan haikali wanda ka gina, ta wurinsa Sunana zai kasance a can har abada. Idanuna da zuciyata kullum za su kasance a can.
And the Lord said to him: I have heard thy prayer and thy supplication, which thou hast made before me: I have sanctified this house, which thou hast built, to put my name there for ever, and my eyes and my heart shall be there always.
4 “Kai kuwa, in ka yi tafiya a gabana da mutunci a zuci da kuma gaskiya, kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, ka yi dukan abin da na umarta, ka kuma yi biyayya da ƙa’idodina da kuma dokokina,
And if thou wilt walk before me, as thy father walked, in simplicity of heart, and in uprightness: and wilt do all that I have commanded thee, and wilt keep my ordinances and my judgments,
5 zan kafa kujerar sarautarka a bisa Isra’ila har abada, kamar yadda na alkawarta wa Dawuda mahaifinka sa’ad da na ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani a kan kujerar sarautar Isra’ila ba.’
I will establish the throne of thy kingdom over Israel for ever, as I promised David thy father, saying: There shall not fail a man of thy race upon the throne of Israel.
6 “Amma in kai, ko’ya’yanka maza, suka juye daga gare ni, ba ku kuma kiyaye umarnai da ƙa’idodin da na ba ku ba, kuka yi gaba, kuka bauta wa waɗansu alloli, kuka kuma yi musu sujada,
But if you and your children revolting shall turn away from following me, and will not keep my commandments, and my ceremonies, which I have set before you, but will go and worship strange gods, and adore them:
7 sai in yanke mutanen Isra’ila daga ƙasar da na ba su, in kuma ƙi wannan haikalin da na tsarkake domin Sunana. Isra’ila kuwa za tă zama abin gori da abin dariya a cikin dukan mutane.
I will take away Israel from the face of the land which I have given them; and the temple which I have sanctified to my name, I will cast out of my sight; and Israel shall be a proverb, and a byword among all people.
8 Wannan haikali zai zama tarin juji. Duk wanda ya wuce ta hanyan nan kuwa zai ji tausayi, yă kuma yi tsaki yana cewa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka ga wannan ƙasa da kuma wannan haikali?’
And this house shall be made an example of: every one that shall pass by it, shall be astonished, and shall hiss, and say: Why hath the Lord done thus to this land, and to this house:
9 Mutane za su amsa su ce, ‘Saboda sun yashe Ubangiji Allahnsu, wanda ya fitar da su daga Masar, suka rungumi waɗansu alloli, suna yin musu sujada, suna bauta musu ne, ya sa Ubangiji ya kawo dukan masifan nan a kansu.’”
And they shall answer: Because they forsook the Lord their God, who brought their fathers out of the land of Egypt, and followed strange gods, and adored them, and worshipped them: therefore hath the Lord brought upon them all this evil.
10 A ƙarshen shekaru ashirin da Solomon ya ɗauka yana gina haikalin Ubangiji da fadan sarki,
And when twenty years were ended after Solomon had built the two houses, that is, the house of the Lord, and the house of the king,
11 sai Sarki Solomon ya ba wa Hiram sarkin Taya garuruwa ashirin a yankin Galili, gama Hiram ya tanada masa da dukan katakai al’ul da na fir, da kuma zinariyar da ya bukaci domin aiki.
(Hiram the king of Tyre furnishing Solomon with cedar trees and fir trees, and gold according to all he had need of.) then Solomon gave Hiram twenty cities in the land of Galilee.
12 Amma sa’ad da Hiram ya zo daga Taya don yă ga garuruwan da Solomon ya ba shi, sai bai ji daɗi ba.
And Hiram came out of Tyre, to see the towns which Solomon had given him, and they pleased him not,
13 Sai ya ce, “Wanda irin garuruwa ke nan ka ba ni, ɗan’uwana?” Saboda haka ya kira su Ƙasar Kabul, sunan da suke da shi har wa yau.
And he said: Are these the cities which thou hast given me, brother? And he called them the land of Chabul, unto this day.
14 Hiram kuwa ya aika wa sarki talenti 120 na zinariya.
And Hiram sent to king Solomon a hundred and twenty talents of gold.
15 Ga lissafin ma’aikatan gandun da Sarki Solomon ya ɗauka don ginin haikalin Ubangiji, da fadarsa, da madogaran gini, da katangar Urushalima, da kuma Hazor Megiddo da Gezer.
This is the sum of the expenses, which king Solomon offered to build the house of the Lord, and his own house, and Mello, and the wall of Jerusalem, and Heser, and Mageddo, and Gazer.
16 (Fir’auna sarkin Masar ya kai wa Gezer hari, ya kuma ci ta da yaƙi. Ya sa mata wuta, ya kashe Kan’aniyawanta mazaunan wurin, ya kuma ba da ita a matsayin kyautar aure ga’yarsa, matar Solomon.
Pharao the king of Egypt came up and took Gazer, and burnt it with fire: and slew the Chanaanite that dwelt in the city, and gave it for a dowry to his daughter, Solomon’s wife.
17 Solomon kuwa ya sāke gina Gezer.) Ya gina Bet-Horon ta Kwari,
So Solomon built: Gazer, and Beth-horon the nether,
18 da Ba’alat, da Tadmor a hamada, na cikin ƙasarsa.
And Baalath, and Palmira in the land of the wilderness.
19 Haka kuma ya gina dukan biranen ajiyarsa, da garuruwa domin kekunan yaƙinsa, da garuruwa domin dawakansa. Ya gina duk abin da ya so yă ginawa a Urushalima, da Lebanon, da kuma ko’ina a dukan yankin da ya yi mulki.
And all the towns that belonged to himself, and were not walled, he fortified, the cities also of the chariots, and the cities of the horsemen, and whatsoever he had a mind to build in Jerusalem, and in Libanus, and in all the land of his dominion.
20 Dukan Amoriyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa da Yebusiyawan da suka ragu a ƙasar (waɗanda ba Isra’ilawa ba ne),
All the people that were left of the Amorrhites, and Hethites, and Pherezites, and Hevites, and Jebusites, that are not of the children of Israel:
21 wato, waɗanda suka ragu a ƙasar, waɗanda Isra’ilawa ba su iya hallakawa ba, su ne Solomon ya ɗauka su zama bayinsa don aikin gandu, kamar yadda yake har wa yau.
Their children, that were left in the land, to wit, such as the children of Israel had not been able to destroy, Solomon made tributary unto this day.
22 Amma Solomon bai mai da Isra’ilawa bayi ba; su ne mayaƙansa, shugabannin gwamnatinsa, dogarawansa, shugabannin sojojinsa, da shugabanninsa na kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙinsa.
But of the children of Israel Solomon made not any to be bondmen, but they were men of war, and his servants, and his princes, and captains, and overseers of the chariots and horses.
23 Su ne kuma manyan shugabanni masu lura da ayyukan Solomon, su ne shugabanni 550 masu lura da mutanen da suke aiki.
And there were five hundred and fifty chief officers set over all the works of Solomon, and they had people under them, and had charge over the appointed works.
24 Bayan’yar Fir’auna ta haura daga Birnin Dawuda zuwa fadan da Solomon ya gina mata, sai ya gina madogaran gini.
And the daughter of Pharao came up out of the city of David to her house, which Solomon had built for her: then did he build Mello.
25 Sau uku a shekara Solomon kan miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama a kan bagaden da ya gina wa Ubangiji, yana ƙone turare a gaban Ubangiji haɗe da su, ta haka ya cika abin da ake bukata na haikali.
Solomon also offered three times every year holocausts, and victims of peace offerings upon the altar which he had built to the Lord, and he burnt incense before the Lord: and the temple was finished.
26 Sarki Solomon ya kuma gina jiragen ruwa a Eziyon Geber, wadda take kusa da Elot a Edom, a bakin Jan Teku.
And king Solomon made a fleet in Asiongaber, which is by Ailath on the shore of the Red Sea in the land of Edom.
27 Hiram kuwa ya aiki mutanensa, masu tuƙan jirgin ruwa waɗanda suka san teku, don su yi hidima a jerin jiragen ruwa tare da mutanen Solomon.
And Hiram sent his servants in the fleet, sailors that had knowledge of the sea, with the servants of Solomon.
28 Suka tafi Ofir suka kuma dawo da talenti 420 na zinariya, wanda suka ba wa Sarki Solomon.
And they came to Ophir, and they brought from thence to king Solomon four hundred and twenty talents of gold.

< 1 Sarakuna 9 >