< 1 Sarakuna 8 >
1 Sai Sarki Solomon ya tattara dattawan Urushalima a gabansa, da dukan shugabannin kabilu, da shugabannin iyalan Isra’ilawa, domin su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Sihiyona, Birnin Dawuda.
Då församlade Konung Salomo till sig de äldsta af Israel, alla öfverstar i slägterna, och Förstar för fäderna ibland Israels barn, till Jerusalem, till att föra Herrans förbunds ark upp utu Davids stad, det är Zion.
2 Dukan mutanen Isra’ila suka tattaru a gaban Sarki Solomon a lokacin biki, a watan Etanim, wato, wata na bakwai.
Och sig församlade till Konung Salomo alle män i Israel, uti den månaden Ethanim på högtidene, det är sjunde månaden.
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka iso, sai firistoci suka ɗauki akwatin alkawarin,
Och då alle äldste i Israel kommo, lyfte Presterna arken upp;
4 suka haura da akwatin alkawarin Ubangiji da kuma Tentin Sujada, da dukan kayayyaki masu tsarkin da suke cikinsa. Firistoci da Lawiyawa suka ɗauko su,
Och båro Herrans ark ditupp; dertill vittnesbördsens tabernakel, och all helgedomens tyg, som i tabernaklet var; det gjorde Presterna och Leviterna.
5 sai Sarki Solomon da dukan taron Isra’ila da suka tattaru kewaye da shi a gaban akwatin alkawari, suka yi ta miƙa hadayar tumaki da bijimai masu yawa da ba a iya lissaftawa, ko ƙirgawa.
Och Konung Salomo och hela Israels menighet, som sig till honom församlat hade, gingo med honom fram för arken, och offrade får, och fä, så mycket att man dem hvarken tälja eller räkna kunde.
6 Sa’an nan firistoci suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji inda aka shirya masa, can ciki cikin haikali, a Wuri Mafi Tsarki, aka kuma sa shi a ƙarƙashin fikafikan kerubobin.
Alltså båro Presterna Herrans förbunds ark uti sitt rum i husets chor, i det aldrahelgasta, under Cherubims vingar.
7 Kerubobin sun buɗe fikafikansu a bisa wurin da akwatin alkawarin yake, suka inuwartar da akwatin alkawarin da sandunan ɗaukansa.
Ty Cherubim räckte vingarna ut till det rum der arken stod, och öfverskylde arken och hans stänger.
8 Waɗannan sandunan sun yi tsawo har ana iya ganin bakinsu daga Wuri Mai Tsarki a gaban wuri mai tsarki na can ciki, amma ba a iya ganinsu daga waje na Wuri Mai Tsarki ba. Suna nan kuwa a can har wa yau.
Och så långa voro stängerna, att deras ändar syntes i helgedomenom för choren; men utantill vordo de intet sedde; och de blefvo der intill denna dag.
9 Ba kome a cikin akwatin alkawarin, sai dai alluna na dutse guda biyu waɗanda Musa ya ajiye a ciki tun a Horeb, inda Ubangiji ya yi alkawari da Isra’ilawa bayan sun fito Masar.
Och i arkenom var intet, utan allenast de två Mose stentaflor, som han lät deruti i Horeb, då Herren gjorde ett förbund med Israels barnom, då de utur Egypti land dragne voro.
10 Sa’ad da firistoci suka janye daga Wuri Mai Tsarki, sai girgije ya cika haikalin Ubangiji.
Då nu Presterna gingo utu helgedomenom, uppfyllde en molnsky Herrans hus,
11 Firistocin kuwa ba su iya yin hidimarsu ba saboda girgijen, gama ɗaukakar Ubangiji ta cika haikalinsa.
Så att Presterna icke kunde stå och sköta ämbetet för molnskyn; ty Herrans härlighet uppfyllde Herrans hus.
12 Sai Solomon ya ce, “Ubangiji ya ce zai zauna a gizagizai masu duhu;
Då sade Salomo: Herren hafver sagt, att han ville bo i mörkrena.
13 ga shi na gina haikali mai daraja dominka, inda za ka zauna har abada.”
Jag hafver byggt ett hus dig till boning; ett säte, att du skall bo der till evig tid.
14 Yayinda dukan taron Isra’ila suke tsattsaye a can, sai sarki ya juya ya albarkace su.
Och Konungen vände sitt ansigte, och välsignade hela menighetena Israel, och hela menigheten Israel stod;
15 Sa’an nan ya ce, “Ku yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda da hannunsa ya cika abin da ya yi alkawari da bakinsa ga mahaifina Dawuda. Gama ya ce,
Och han sade: Lofvad vare Herren Israels Gud, som med sin mun med minom fader David talat, och med sine hand fullbordat hafver, och sagt:
16 ‘Tun ran da na fitar da mutanena Isra’ila daga Masar, ban zaɓi wani birni a cikin wata kabilar Isra’ila a gina haikali domin Sunana yă kasance a can ba, amma na zaɓi Dawuda yă yi mulkin mutanena Isra’ila.’
Ifrå den dag, då jag förde mitt folk Israel utur Egypten, hafver jag ingen stad utvalt i några af Israels slägter, att mig skulle varda ett hus bygdt, så att mitt Namn skulle vara der; men David hafver jag utvalt, att han skall vara öfver mitt folk Israel.
17 “Mahaifina Dawuda ya yi niyya a cikin zuciyarsa yă gina haikali saboda Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Och min fader David hade väl i sinnet, att han skulle bygga Herrans Israels. Guds Namne ett hus.
18 Amma Ubangiji ya ce wa mahaifina Dawuda, ‘Saboda yana a zuciyarka ka gina haikali domin Sunana, ka yi daidai da ka yi niyyar wannan a zuciyarka.
Men Herren sade till min fader David: Att du hafver i sinnet bygga mino Namne ett hus, hafver du gjort väl, att du hade det i sinnet;
19 Duk da haka, ba kai ba ne za ka gina haikali, amma ɗanka, wanda yake namanka da jininka, shi ne wanda zai gina haikali domin Sunana.’
Dock skall icke du bygga det huset, utan din son, som utaf dina länder komma skall, han skall bygga mino Namne ett hus.
20 “Ubangiji ya kiyaye alkawarin da ya yi. Na gāje Dawuda mahaifina, yanzu kuma ga shi na zauna a kujerar sarautar Isra’ila, kamar dai yadda Ubangiji ya yi alkawari, na kuma gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Och Herren hafver gjort sitt ord fast, som han talat hafver; ty jag är uppkommen i mins faders Davids stad, och sitter på Israels stol, såsom Herren sagt, och hafver byggt Herrans Israels Guds Namne ett hus;
21 Na tanada wuri saboda akwatin alkawari, akwatin da ya ƙunshi alkawarin da Ubangiji ya yi da kakanninmu sa’ad da ya fitar da su daga Masar.”
Och hafver derutinnan tillpyntat ett rum till arken, som Herrans förbund uti är, det han gjort hafver med våra fäder, då han dem utur Egypti land förde.
22 Sai Solomon ya tsaya a gaban bagaden Ubangiji, a gaban dukan taron Isra’ila, ya ɗaga hannuwansa sama,
Och Salomo stod för Herrans altare emot hela Israels menighet, och räckte ut sina händer upp till himmelen;
23 ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, babu Allah kamar ka a sama can bisa, ko a ƙasa can ƙarƙashi, kai da kake kiyaye alkawarinka na ƙauna ga bayinka waɗanda suke cin gaba a hanyarka da dukan zuciyarsu.
Och sade: Herre Israels Gud, det är ingen Gud, antingen ofvantill i himmelen, eller nedre på jordene, din like; du som håller förbund och barmhertighet dinom tjenarom, som vandra för dig af allo hjerta;
24 Ka kiyaye alkawarinka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina. Da bakinka ka yi alkawari, da hannunka kuma ka cika shi, yadda yake a yau.
Du som hafver hållit dinom tjenare David, minom fader, allt det du honom sagt hafver; med dinom mun hafver du talat det, och med dine hand hafver du fullkomnat det, såsom det nu i denna dag tillgår.
25 “Yanzu, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bari ka cika wa bawanka Dawuda mahaifina alkawaran da ka yi masa sa’ad da ka ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani da zai zauna a gabana a kan kujerar sarautar Isra’ila ba, in kawai’ya’yanka maza sun yi hankali cikin dukan abubuwan da suke yi, don su yi tafiya a gabana kamar yadda ka yi.’
Nu, Herre Israels Gud, håll dinom tjenare David, minom fader, det du med honom talat hafver, och sagt: Dig skall icke fattas en man för mig, som sitta skall på Israels stol; såframt din barn förvara sina vägar, att de vandra såsom du för mig vandrat hafver.
26 Yanzu fa, ya Allah na Isra’ila, bari maganarka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina tă cika.
Nu, Israels Gud, låt din ord blifva sann, som du till din tjenare David, min fader, talat hafver.
27 “Amma anya, Allah, za ka zauna a duniya? Sammai, har ma da saman sammai ba za tă iya riƙe ka ba, balle wannan haikalin da na gina!
Ty menar du ock, att Gud bor på jordene? Si, himmelen och alla himlars himlar kunna icke begripa dig; huru skulle då detta huset göra det, som jag nu byggt hafver?
28 Duk da haka ka ji addu’ar bawanka da kuma roƙonsa don jinƙai, ya Ubangiji Allahna. Ka ji kuka da addu’ar da bawanka yake yi a gabanka a wannan rana.
Så vänd dig till dins tjenares bon, och till hans begär, Herre min Gud, så att du hörer det lof, och den bön, som din tjenare gör för dig i dag;
29 Bari idanunka su buɗe, su fuskanci wannan haikali dare da rana, wannan wurin da ka ce, ‘Sunana zai kasance a can,’ saboda ka ji addu’ar bawanka in yana fuskantar wannan wuri.
Att din ögon måga stå öppne öfver detta hus, natt och dag; öfver det rum, der du om sagt hafver: Mitt Namn skall vara der; att du ville höra den bön, som din tjenare gör på detta rum;
30 Ka ji roƙon bawanka da kuma na mutanenka Isra’ila sa’ad da suka yi addu’a, suka fuskanci wannan wuri. Ka ji daga sama, mazauninka, kuma sa’ad da ka ji, ka gafarta.
Och ville höra dins tjenares, och dins folks Israels bön, den de här görande varda i detta rum; och höra det der du bor i himmelen; och när du det hörer, vara nådelig.
31 “Sa’ad da mutum ya yi abin da ba daidai ba ga maƙwabcinsa, an kuma bukace shi yă yi rantsuwa, sai ya zo ya rantse a gaban bagade a cikin haikalin nan,
När nu någor syndar emot sin nästa, och tager dess en ed uppå sig, der han sig med förpligtar, och eden kommer inför ditt altare i desso huse;
32 sai ka ji daga sama, ka kuma yi wani abu. Ka shari’anta tsakanin bayinka, ka hukunta mai laifi, ka mai da laifinsa a kansa, mai gaskiya kuma ka nuna shi marar laifi ne bisa ga gaskiyarsa.
Att du ville då höra i himmelen, och skaffa dina tjenare rätt, att du fördömer den ogudaktiga, och låter hans väg komma öfver hans hufvud; och rättfärdigar den rätta, att du honom gör efter hans rättfärdighet.
33 “Sa’ad da abokan gāba suka ci mutanenka Isra’ila a yaƙi saboda sun yi maka zunubi, sa’ad da kuma suka dawo gare ka don su furta sunanka, suna addu’a suna roƙo gare ka a wannan haikali,
Om ditt folk Israel vorde slaget för sina fiendar, efter de emot dig syndat hafva; och vända sig till dig, och bekänna ditt Namn, och bedja, och begära af dig i desso huse;
34 ka ji daga sama, ka gafarta zunubin mutanenka, ka kuma dawo da su ƙasar da ka ba wa kakanninsu.
Att du ville då hörat i himmelen, och dins folks Israels syndom nådelig vara; och föra dem åter i det land, som du deras fäder gifvit hafver.
35 “Sa’ad da sammai sun kulle, babu kuma ruwan sama domin mutane sun yi maka zunubi, sa’ad da suka yi addu’a suna fuskantar wannan wuri, suka kuma furta sunanka, suka juye daga zunubinsu domin ka hore su,
Om himmelen igenlyckt varder, så att intet regnar, efter de emot dig syndat hafva; och varda bedjande på detta rum, och bekänna ditt Namn, och vända sig ifrå sina synder, efter du plågar dem;
36 ka ji daga sama, ka kuma gafarta zunubin bayinka, mutanenka Isra’ila. Ka koya musu hanyar da ta dace ta rayuwa, ka kuma aika da ruwan sama a ƙasar da ka ba wa mutanenka gādo.
Att du ville i himmelen höra dem, och vara dina tjenares, och dins folks Israels synder nådelig; att du visar dem den goda vägen, der de uti vandra skola, och låter regna på landet, som du dino folke till arfs gifvit hafver.
37 “Sa’ad da yunwa ko annoba ta fāɗo a ƙasar, ko burtuntuna, ko fumfuna, ko fāri, ko tsutsa, ko kuwa abokan gāba sun yi musu kwanto, a wani daga cikin biranensu, duk wata cuta, ko ciwon da ya zo,
Om en hård tid, eller pestilentie, eller torka, eller brand, eller gräshoppor, eller matkar på landet kommande varda; eller deras fiende belägger deras portar i landena, eller någor plåga eller krankhet;
38 in suka yi addu’a ko roƙo ta wurin wani daga cikin mutanenka Isra’ila, kowa ya san wahalar zuciyarsa, ya kuma buɗe hannuwansa yana fuskantar wannan haikali,
Den då beder eller begärar, ehvad de äro andra menniskor, eller ditt folk Israel, som förnimma sina plågo, hvar och en i sitt hjerta, och räcka sina händer ut till detta huset;
39 sai ka ji daga sama, mazauninka. Ka gafarta, ka kuma yi wani abu. Ka yi da kowane mutum bisa ga dukan abin da ya yi, tun da yake ka san zuciyarsa (gama kai kaɗai ka san zukatan dukan mutane),
Att du ville då höra i himmelen, i det säte der du bor, och vara nådelig; och fly det så, att du gifver hvarjom och enom såsom han vandrat hafver, såsom du hans hjerta känner; ty du allena känner alla menniskors barnas hjerta;
40 saboda su ji tsoronka a kowane lokacin da suke zaune a ƙasar da ka ba wa kakanninmu.
På det att de skola frukta dig alltid, så länge de lefva i landena, det du våra fäder gifvit hafver.
41 “Game da baƙo kuwa wanda shi ba na mutanenka Isra’ila ba, amma ya zo daga ƙasa mai nisa saboda sunanka,
Om ock en främmande, som icke är af ditt folk Israel, kommer af fjerran land för ditt Namns skull;
42 gama mutane za su ji game da girman sunanka, da ƙarfin hannunka, da kuma hannunka mai iko, sa’ad da ya zo, ya yi addu’a yana fuskantar wannan haikali,
Ty de varda hörande om ditt stora Namn, och om dina mägtiga hand, och om din uträckta arm; och kommer till att bedja i desso huse;
43 ka ji daga sama, mazauninka, ka kuma yi dukan abin da baƙon ya tambaye ka, saboda dukan mutanen duniya su san sunanka, su kuma ji tsoronka, kamar yadda mutanenka Isra’ila suke yi, bari kuma su san cewa wannan gidan da na gina, ya amsa Sunanka.
Att du då ville höra i himmelen, i det säte der du bor, och göra allt det den främmande dig om åkallar; på det all folk på jordene måga känna ditt Namn, att de ock frukta dig lika som ditt folk Israel, och förnimma, att detta huset efter ditt Namn nämndt är, det jag byggt hafver.
44 “Sa’ad da mutanenka suka tafi yaƙi da abokan gābansu, a duk inda ka aike su, sa’ad da kuma suka yi addu’a ga Ubangiji suna fuskantar birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka,
Om ditt folk utdrager i strid emot sina fiendar, den vägen som du dem sändandes varder, och de varda bedjande till Herran, emot vägen till den staden som du utvalt hafver, och emot huset som jag dino Namne byggt hafver;
45 ka ji addu’arsu da roƙonsu daga sama, ka kuma biya musu bukatansu.
Att du då ville höra deras bön och begär i himmelen, och skaffa dem rätt.
46 “Sa’ad da suka yi maka zunubi, gama babu wanda ba ya zunubi, ka kuwa yi fushi da su, ka kuma ba da su ga abokin gāba, wanda ya kwashe su kamammu zuwa ƙasarsa, nesa ko kusa;
Om de varda syndande emot dig; ty det är ingen menniska, som icke syndar; och du varder vred, och gifver dem för deras fiendar, så att de föra dem fångna i fiendaland, fjerran eller när;
47 in suka canja zuciyarsu a ƙasar da aka riƙe su kamammu, suka tuba, suka kuma roƙe ka a ƙasar waɗanda suka ci su da yaƙi, suka ce, ‘Mun yi zunubi, mun yi abin da ba daidai ba, mun yi mugunta’;
Och de besinna sig i sitt hjerta, uti landena der de fångne äro, och omvända sig, och bedja dig uti deras fängelses land, och säga: Vi hafve syndat, och gjort illa, och varit ogudaktige;
48 in sun juye gare ka da dukan zuciyarsu, da dukan ransu a ƙasar abokan gābansu waɗanda suka kwashe kamammu, suka yi addu’a gare ka, suka fuskanci wajen ƙasar da ka ba wa kakanninsu, waje birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka;
Och vända sig så till dig af allt hjerta, af allo själ, uti deras fiendars land, som dem bortfört hafva, och bedja till dig emot vägen till deras land, som du deras fäder gifvit hafver, emot den staden som du utvalt hafver, och emot det huset som jag dino Namne byggt hafver;
49 sai ka ji daga sama, mazauninka, ka ji addu’a da roƙonsu, ka kuma biya musu bukatansu.
Att du då ville höra deras bön och begär i himmelen, af det säte der du bor, och skaffa dem rätt,
50 Ka gafarta wa mutanenka, waɗanda suka yi maka zunubi; ka gafarta dukan laifofin da suka yi maka, ka kuma sa waɗanda suka ci su a yaƙi su ji tausayinsu.
Och vara dino folke nådelig, som emot dig syndat hafver, och all deras öfverträdelse, der de med hafva förbrutit sig emot dig; och gifva dem barmhertighet för dem som dem fångna hålla, att de förbarma sig öfver dem;
51 Gama su mutanenka ne, abin gādonka, waɗanda ka fitar daga Masar, daga tanderu mai narken ƙarfe.
Förty de äro ditt folk, och ditt arf, som du utur Egypten, utu jernugnenom fört hafver;
52 “Bari idanunka su buɗe ga roƙon bawanka, ga roƙon mutanenka Isra’ila, bari kuma ka saurare su sa’ad da suka yi kuka gare ka.
Att din ögon måga öppne vara till dins tjenares och dins folks Israels bön; att du ville höra dem i allt det, der de om åkalla dig;
53 Gama ka ware su daga dukan al’umman duniya su zama abin gādonka, kamar yadda aka furta ta wurin bawanka Musa sa’ad da kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka ka fitar da kakanninmu daga Masar.”
Ty du hafver dem dig af skiljt till ett arf utur all folk på jordene, såsom du sagt hafver genom din tjenare Mose, då du våra fäder utur Egypten förde, Herre, Herre.
54 Da Solomon ya gama dukan waɗannan addu’o’i da roƙe-roƙe ga Ubangiji, sai ya tashi daga gaban bagaden Ubangiji, inda ya durƙusa da hannuwansa a buɗe waje sama.
Och då Salomo hade all denna bön och begäran utbedit för Herranom, stod han upp ifrå Herrans altare, och höll upp att böja sin knä, och uträcka sina händer till himmelen;
55 Ya tashi ya kuma albarkaci dukan taron Isra’ila da babbar murya, yana cewa,
Och stod, och välsignade alla menighetena Israel, med höga, röst, och sade:
56 “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda ya ba wa mutanensa hutu kamar dai yadda ya yi alkawari. Babu magana guda da ta kāsa cika cikin dukan alkawaransa masu kyau da ya yi ta wurin bawansa Musa.
Lofvad vare Herren, som sino folke Israel ro gifvit hafver, såsom han sagt hafver; icke ett är förfallet af hans goda ord, som han genom sin tjenare Mose talat hafver.
57 Bari Ubangiji Allah yă kasance tare da mu kamar yadda ya kasance da kakanninmu; kada yă taɓa rabu da mu, ko yă yashe mu.
Herren vår Gud vare med oss, såsom han varit hafver med våra fäder. Han öfvergifve oss icke, och tage icke handena bort ifrån oss;
58 Bari yă juye zukatanmu gare shi, don mu yi tafiya a cikin dukan hanyoyinsa, mu kuma kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa, da kuma farillan da ya ba wa kakanninmu.
Till att böja vårt hjerta till sig, att vi måge vandra i alla hans vägar, och hålla hans bud, seder och rätter, som han våra fäder budit hafver;
59 Bari kuma waɗannan kalmomina, waɗanda na yi addu’a a gaban Ubangiji, su yi kusa da Ubangiji Allahnmu, dare da rana, don yă biya bukatan bawansa da na mutanensa Isra’ila, bisa ga bukatan kowa,
Och att desse orden, som jag för Herranom bedit hafver, måtte nalkas Herranom vårom Gud dag och natt, att han må skaffa sinom tjenare rätt, och sino folke Israel, hvarjom och enom i sinom tid;
60 saboda dukan mutanen duniya su san cewa Ubangiji, shi ne Allah, babu kuma wani.
På det att all folk på jordene måga känna, att Herren är Gud, och ingen annar.
61 Amma dole ku miƙa zukatanku ga Ubangiji Allahnmu, don ku rayu, ta wurin bin ƙa’idodinsa, ku kuma yi biyayya da umarnansa, kamar yadda kuke yi a wannan lokaci.”
Och edor hjerta vare rättsinnig med Herranom vårom Gud, till att vandra i hans seder, och till att hålla hans bud, såsom det tillgår i denna dag.
62 Sai sarki da dukan Isra’ila, suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
Och Konungen, samt med hela Israel, offrade offer för Herranom.
63 Solomon ya miƙa hadaya ta salama ga Ubangiji, shanu dubu ashirin da biyu, tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan Isra’ilawa suka keɓe haikalin Ubangiji.
Och Salomo offrade tackoffer, som han Herranom offrade, tu och tjugu tusend oxar, och hundradetusend och tjugutusend får. Alltså vigde de Herrans hus, Konungen och all Israels barn.
64 A wannan rana sarki ya tsarkake sashe na tsakiyar fili a gaban haikalin Ubangiji, a can kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa, hadaya ta gari, da kitsen hadaya ta salama, gama bagaden tagulla a gaban Ubangiji ya yi ƙanƙanta sosai da za a miƙa hadayun ƙonawa, hadayun hatsi, da kuma kitsen hadayun salama.
På samma dagen vigde Konungen medelgården, som var för Herrans hus, dermed att han der uträttade bränneoffer, spisoffer, och det feta af tackoffret; förty kopparaltaret, som för Herranom stod, var för litet till bränneoffer, spisoffer, och till det feta af tackoffer.
65 Ta haka Solomon da dukan Isra’ila, wato, babban taro, suka yi bikin a lokacin. Mutane suka zo, tun daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar. Suka yi biki a gaban Ubangiji Allahnmu, kwana bakwai. Suka kuma ƙara kwana bakwai, kwanaki goma sha huɗu gaba ɗaya.
Och Salomo gjorde på den tiden en högtid, och all Israel med honom en stor församling, ifrå den gränson Hamath, allt intill Egypti bäck, för Herranom vårom Gud i sju dagar, och åter i sju dagar; det voro fjorton dagar.
66 A rana ta biye sai ya sallame mutane. Suka sa wa sarki albarka, sa’an nan suka watse zuwa gida, da farin ciki, da murna a zukatansu saboda kyawawan abubuwan da Ubangiji ya yi domin bawansa Dawuda, da kuma mutanensa Isra’ila.
Och på åttonde dagen lät han folket gå; och de välsignade Konungen, och gingo sina färde i sina hyddor, glädjandes och fröjdandes sig öfver allt det goda, som Herren med sinom tjenare David, och med sitt folk Israel, gjort hade.