< 1 Sarakuna 8 >

1 Sai Sarki Solomon ya tattara dattawan Urushalima a gabansa, da dukan shugabannin kabilu, da shugabannin iyalan Isra’ilawa, domin su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Sihiyona, Birnin Dawuda.
Potem je Salomon zbral Izraelove starešine in vse poglavarje rodov, vodilne izmed očetov Izraelovih otrok, h kralju Salomonu v Jeruzalem, da bi lahko prinesli gor skrinjo Gospodove zaveze iz Davidovega mesta, ki je Sion.
2 Dukan mutanen Isra’ila suka tattaru a gaban Sarki Solomon a lokacin biki, a watan Etanim, wato, wata na bakwai.
Vsi možje iz Izraela so se na praznik zbrali h kralju Salomonu, v mesecu etanímu, ki je sedmi mesec.
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka iso, sai firistoci suka ɗauki akwatin alkawarin,
Prišli so vsi Izraelovi starešine in duhovniki so dvignili skrinjo.
4 suka haura da akwatin alkawarin Ubangiji da kuma Tentin Sujada, da dukan kayayyaki masu tsarkin da suke cikinsa. Firistoci da Lawiyawa suka ɗauko su,
Gor so prinesli Gospodovo skrinjo, šotorsko svetišče skupnosti shoda in vse svete posode, ki so bile v šotorskem svetišču, celo te so duhovniki in Lévijevci prinesli gor.
5 sai Sarki Solomon da dukan taron Isra’ila da suka tattaru kewaye da shi a gaban akwatin alkawari, suka yi ta miƙa hadayar tumaki da bijimai masu yawa da ba a iya lissaftawa, ko ƙirgawa.
Kralj Salomon in vsa Izraelova skupnost, ki je bila zbrana k njemu, so bili z njim pred skrinjo. Žrtvovali so ovce in vole, ki se jih zaradi množice ni dalo ne povedati ne prešteti.
6 Sa’an nan firistoci suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji inda aka shirya masa, can ciki cikin haikali, a Wuri Mafi Tsarki, aka kuma sa shi a ƙarƙashin fikafikan kerubobin.
Duhovniki so skrinjo Gospodove zaveze prinesli na njeno mesto, v hišni orakelj, k najsvetejšemu kraju, celo pod peruti kerubov.
7 Kerubobin sun buɗe fikafikansu a bisa wurin da akwatin alkawarin yake, suka inuwartar da akwatin alkawarin da sandunan ɗaukansa.
Kajti keruba sta svoji dve peruti razprostirala nad prostorom skrinje in keruba sta od zgoraj pokrivala skrinjo in njena drogova.
8 Waɗannan sandunan sun yi tsawo har ana iya ganin bakinsu daga Wuri Mai Tsarki a gaban wuri mai tsarki na can ciki, amma ba a iya ganinsu daga waje na Wuri Mai Tsarki ba. Suna nan kuwa a can har wa yau.
Drogova so izvlekli, da sta se konca drogov videla iz svetega kraja pred orakljem, odzunaj pa nista bila vidna in tam sta do današnjega dne.
9 Ba kome a cikin akwatin alkawarin, sai dai alluna na dutse guda biyu waɗanda Musa ya ajiye a ciki tun a Horeb, inda Ubangiji ya yi alkawari da Isra’ilawa bayan sun fito Masar.
V skrinji ni bilo ničesar razen dveh kamnitih plošč, ki ju je Mojzes položil tja pri Horebu, ko je Gospod sklenil zavezo z Izraelovi otroci, ko so prišli iz egiptovske dežele.
10 Sa’ad da firistoci suka janye daga Wuri Mai Tsarki, sai girgije ya cika haikalin Ubangiji.
Pripetilo se je, ko so duhovniki prišli ven iz svetega kraja, da je oblak napolnil Gospodovo hišo,
11 Firistocin kuwa ba su iya yin hidimarsu ba saboda girgijen, gama ɗaukakar Ubangiji ta cika haikalinsa.
tako da duhovniki zaradi oblaka niso mogli stati, da bi služili, kajti Gospodova slava je napolnila Gospodovo hišo.
12 Sai Solomon ya ce, “Ubangiji ya ce zai zauna a gizagizai masu duhu;
Potem je spregovoril Salomon: » Gospod je rekel, da bo prebival v gosti temi.
13 ga shi na gina haikali mai daraja dominka, inda za ka zauna har abada.”
Zagotovo sem ti zgradil hišo, da prebivaš v njej, ustaljen kraj zate, da v njem prebivaš na veke.«
14 Yayinda dukan taron Isra’ila suke tsattsaye a can, sai sarki ya juya ya albarkace su.
Kralj je obrnil svoj obraz naokrog in blagoslovil vso Izraelovo skupnost (in vsa Izraelova skupnost je stala)
15 Sa’an nan ya ce, “Ku yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda da hannunsa ya cika abin da ya yi alkawari da bakinsa ga mahaifina Dawuda. Gama ya ce,
in rekel je: »Blagoslovljen bodi Gospod, Izraelov Bog, ki je s svojimi usti spregovoril mojemu očetu Davidu in je to izpolnil s svojo roko, rekoč:
16 ‘Tun ran da na fitar da mutanena Isra’ila daga Masar, ban zaɓi wani birni a cikin wata kabilar Isra’ila a gina haikali domin Sunana yă kasance a can ba, amma na zaɓi Dawuda yă yi mulkin mutanena Isra’ila.’
›Od dneva, ko sem svoje ljudstvo Izraela privedel ven iz Egipta, nisem izbral nobenega mesta izmed vseh Izraelovih rodov, da bi zgradil hišo, da bi bilo v njej lahko moje ime, temveč sem izbral Davida, da bo nad mojim ljudstvom Izraelom.‹
17 “Mahaifina Dawuda ya yi niyya a cikin zuciyarsa yă gina haikali saboda Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
To je bilo na srcu mojega očeta Davida, da zgradi hišo za ime Gospoda, Izraelovega Boga.
18 Amma Ubangiji ya ce wa mahaifina Dawuda, ‘Saboda yana a zuciyarka ka gina haikali domin Sunana, ka yi daidai da ka yi niyyar wannan a zuciyarka.
Gospod je rekel mojemu očetu Davidu: ›Medtem ko je bilo to v tvojem srcu, da zgradiš hišo mojemu imenu, si storil dobro, da je bilo to v tvojem srcu.
19 Duk da haka, ba kai ba ne za ka gina haikali, amma ɗanka, wanda yake namanka da jininka, shi ne wanda zai gina haikali domin Sunana.’
Vendar pa hiše ne boš gradil ti, temveč tvoj sin, ki bo izšel iz tvojih ledij, on bo zgradil hišo mojemu imenu.‹
20 “Ubangiji ya kiyaye alkawarin da ya yi. Na gāje Dawuda mahaifina, yanzu kuma ga shi na zauna a kujerar sarautar Isra’ila, kamar dai yadda Ubangiji ya yi alkawari, na kuma gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Gospod je izpolnil svojo besedo, ki jo je govoril in dvignjen sem bil na položaj svojega očeta Davida in sedim na Izraelovem prestolu, kakor je obljubil Gospod in zgradil sem hišo za ime Gospoda, Izraelovega Boga.
21 Na tanada wuri saboda akwatin alkawari, akwatin da ya ƙunshi alkawarin da Ubangiji ya yi da kakanninmu sa’ad da ya fitar da su daga Masar.”
Tam sem pripravil prostor za skrinjo, v kateri je Gospodova zaveza, ki jo je on sklenil z našimi očeti, ko jih je privedel ven iz egiptovske dežele.«
22 Sai Solomon ya tsaya a gaban bagaden Ubangiji, a gaban dukan taron Isra’ila, ya ɗaga hannuwansa sama,
Salomon je stal pred Gospodovim oltarjem v prisotnosti vse Izraelove skupnosti in svoji roki razširil proti nebu
23 ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, babu Allah kamar ka a sama can bisa, ko a ƙasa can ƙarƙashi, kai da kake kiyaye alkawarinka na ƙauna ga bayinka waɗanda suke cin gaba a hanyarka da dukan zuciyarsu.
in rekel: » Gospod, Izraelov Bog, ni Boga, podobnega tebi, na nebu zgoraj ali na zemlji spodaj, ki ohranjaš zavezo in usmiljenje s svojimi služabniki, ki z vsem svojim srcem hodijo pred teboj,
24 Ka kiyaye alkawarinka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina. Da bakinka ka yi alkawari, da hannunka kuma ka cika shi, yadda yake a yau.
ki si svojemu služabniku Davidu, mojemu očetu, ohranil to, kar si mu obljubil. Govoril si s svojimi usti in si to tudi izpolnil s svojo roko, kakor je to ta dan.
25 “Yanzu, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bari ka cika wa bawanka Dawuda mahaifina alkawaran da ka yi masa sa’ad da ka ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani da zai zauna a gabana a kan kujerar sarautar Isra’ila ba, in kawai’ya’yanka maza sun yi hankali cikin dukan abubuwan da suke yi, don su yi tafiya a gabana kamar yadda ka yi.’
Zato zdaj Gospod, Izraelov Bog, ohrani s svojim služabnikom Davidom, mojim očetom, to, kar si mu obljubil, rekoč: ›Ne bo ti zmanjkalo moža v mojem pogledu, da bi sedel na Izraelovem prestolu; samo da tvoji otroci pazijo na svojo pot, da hodijo pred menoj, kakor si ti hodil pred menoj.‹
26 Yanzu fa, ya Allah na Isra’ila, bari maganarka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina tă cika.
Sedaj, oh Izraelov Bog, naj bo tvoja beseda, prosim te, resnična, ki si jo govoril svojemu služabniku, mojemu očetu Davidu.
27 “Amma anya, Allah, za ka zauna a duniya? Sammai, har ma da saman sammai ba za tă iya riƙe ka ba, balle wannan haikalin da na gina!
Toda ali bo Bog zares prebival na zemlji? Glej, nebo in nebesa nebes te ne morejo obseči, kako veliko manj ta hiša, ki sem jo zgradil?
28 Duk da haka ka ji addu’ar bawanka da kuma roƙonsa don jinƙai, ya Ubangiji Allahna. Ka ji kuka da addu’ar da bawanka yake yi a gabanka a wannan rana.
Vendar se ozri na molitev svojega služabnika in k njegovi ponižni prošnji, oh Gospod, moj Bog, da prisluhneš klicu in molitvi, ki jo ta dan tvoj služabnik moli pred teboj,
29 Bari idanunka su buɗe, su fuskanci wannan haikali dare da rana, wannan wurin da ka ce, ‘Sunana zai kasance a can,’ saboda ka ji addu’ar bawanka in yana fuskantar wannan wuri.
da bodo tvoje oči lahko ponoči in podnevi odprte proti tej hiši, torej proti kraju, o katerem si rekel: ›Moje ime bo tam, ‹ da boš lahko prisluhnil molitvi, ki jo bo tvoj služabnik naredil k temu kraju.
30 Ka ji roƙon bawanka da kuma na mutanenka Isra’ila sa’ad da suka yi addu’a, suka fuskanci wannan wuri. Ka ji daga sama, mazauninka, kuma sa’ad da ka ji, ka gafarta.
Prisluhni ponižni prošnji svojega služabnika in svojega ljudstva Izraela, ko bodo molili k temu kraju. Pozorno poslušaj v nebesih, svojem prebivališču. In ko si pozorno slišal, odpusti.
31 “Sa’ad da mutum ya yi abin da ba daidai ba ga maƙwabcinsa, an kuma bukace shi yă yi rantsuwa, sai ya zo ya rantse a gaban bagade a cikin haikalin nan,
Če se katerikoli človek prekrši zoper svojega bližnjega in je nanj položena prisega, da mu povzroči, da priseže in prisega pride pred tvoj oltar v tej hiši,
32 sai ka ji daga sama, ka kuma yi wani abu. Ka shari’anta tsakanin bayinka, ka hukunta mai laifi, ka mai da laifinsa a kansa, mai gaskiya kuma ka nuna shi marar laifi ne bisa ga gaskiyarsa.
potem pozorno poslušaj v nebesih, ukrepaj in sodi svoja služabnika, obsodi zlobnega, da privedeš njegovo pot na njegovo glavo in opraviči pravičnega, da mu daš glede na njegovo pravičnost.
33 “Sa’ad da abokan gāba suka ci mutanenka Isra’ila a yaƙi saboda sun yi maka zunubi, sa’ad da kuma suka dawo gare ka don su furta sunanka, suna addu’a suna roƙo gare ka a wannan haikali,
Ko bo tvoje ljudstvo Izrael udarjeno pred sovražnikom, ker so grešili zoper tebe in se bo ponovno obrnilo k tebi, priznalo tvoje ime, molilo in naredilo ponižno prošnjo k tebi v tej hiši,
34 ka ji daga sama, ka gafarta zunubin mutanenka, ka kuma dawo da su ƙasar da ka ba wa kakanninsu.
potem pozorno poslušaj v nebesih in odpusti greh svojega ljudstva Izraela in jih ponovno privedi v deželo, ki jo daješ njihovim očetom.
35 “Sa’ad da sammai sun kulle, babu kuma ruwan sama domin mutane sun yi maka zunubi, sa’ad da suka yi addu’a suna fuskantar wannan wuri, suka kuma furta sunanka, suka juye daga zunubinsu domin ka hore su,
Ko je nebo zaprto in ni dežja, ker so grešili zoper tebe; če molijo k temu kraju in priznajo tvoje ime in se obrnejo od svojega greha, ko si jih ti prizadel,
36 ka ji daga sama, ka kuma gafarta zunubin bayinka, mutanenka Isra’ila. Ka koya musu hanyar da ta dace ta rayuwa, ka kuma aika da ruwan sama a ƙasar da ka ba wa mutanenka gādo.
potem pozorno poslušaj v nebesih in odpusti greh svojih služabnikov in svojega ljudstva Izraela, da jih naučiš dobro pot, po kateri naj bi hodili in jim daš dež na svojo deželo, ki si jo dal svojemu ljudstvu v dediščino.
37 “Sa’ad da yunwa ko annoba ta fāɗo a ƙasar, ko burtuntuna, ko fumfuna, ko fāri, ko tsutsa, ko kuwa abokan gāba sun yi musu kwanto, a wani daga cikin biranensu, duk wata cuta, ko ciwon da ya zo,
Če bo v deželi lakota, če bo kužna bolezen, kvarjenje, plesen, leteča kobilica ali če bo tam gosenica; če jih njihov sovražnik oblega v deželi njihovih mest, kakršnakoli nadloga, kakršnakoli bolezen bo,
38 in suka yi addu’a ko roƙo ta wurin wani daga cikin mutanenka Isra’ila, kowa ya san wahalar zuciyarsa, ya kuma buɗe hannuwansa yana fuskantar wannan haikali,
kakršnokoli molitev in ponižno prošnjo bo naredil katerikoli človek ali vse tvoje ljudstvo Izrael, ki bo spoznal, vsak mož nadlogo svojega lastnega srca in bo svoje roke razširil proti tej hiši,
39 sai ka ji daga sama, mazauninka. Ka gafarta, ka kuma yi wani abu. Ka yi da kowane mutum bisa ga dukan abin da ya yi, tun da yake ka san zuciyarsa (gama kai kaɗai ka san zukatan dukan mutane),
potem pozorno poslušaj v nebesih, svojem prebivališču, odpusti, ukrepaj in daj vsakemu možu glede na njegove poti, čigar srce poznaš (kajti ti, celó le ti, poznaš srca vseh človeških otrok),
40 saboda su ji tsoronka a kowane lokacin da suke zaune a ƙasar da ka ba wa kakanninmu.
da se te bodo lahko bali vse dni, ki jih živijo v deželi, ki si jo dal našim očetom.
41 “Game da baƙo kuwa wanda shi ba na mutanenka Isra’ila ba, amma ya zo daga ƙasa mai nisa saboda sunanka,
Poleg tega glede tujca, ki ni iz tvojega ljudstva Izraela, temveč zaradi tvojega imena prihaja iz daljne dežele
42 gama mutane za su ji game da girman sunanka, da ƙarfin hannunka, da kuma hannunka mai iko, sa’ad da ya zo, ya yi addu’a yana fuskantar wannan haikali,
(kajti slišali bodo o tvojem velikem imenu, o tvoji močni roki in o tvojem iztegnjenem laktu), ko bo prišel in molil k tej hiši,
43 ka ji daga sama, mazauninka, ka kuma yi dukan abin da baƙon ya tambaye ka, saboda dukan mutanen duniya su san sunanka, su kuma ji tsoronka, kamar yadda mutanenka Isra’ila suke yi, bari kuma su san cewa wannan gidan da na gina, ya amsa Sunanka.
pozorno poslušaj v nebesih, svojem bivališču in ukrepaj glede na vse, za kar bo tujec klical k tebi, da bo vse ljudstvo zemlje lahko spoznalo tvoje ime, da se te boji, kakor to dela tvoje ljudstvo Izrael in da bodo lahko vedeli, da je ta hiša, ki sem jo zgradil, imenovana po tvojem imenu.
44 “Sa’ad da mutanenka suka tafi yaƙi da abokan gābansu, a duk inda ka aike su, sa’ad da kuma suka yi addu’a ga Ubangiji suna fuskantar birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka,
Če gre tvoje ljudstvo ven na bitko zoper svojega sovražnika, kamorkoli jih boš poslal in bodo molili h Gospodu, k mestu, ki si ga ti izbral in k hiši, ki sem jo zgradil za tvoje ime,
45 ka ji addu’arsu da roƙonsu daga sama, ka kuma biya musu bukatansu.
potem pozorno poslušaj v nebesih njihovo molitev, njihovo ponižno prošnjo in obravnavaj njihov primer.
46 “Sa’ad da suka yi maka zunubi, gama babu wanda ba ya zunubi, ka kuwa yi fushi da su, ka kuma ba da su ga abokin gāba, wanda ya kwashe su kamammu zuwa ƙasarsa, nesa ko kusa;
Če grešijo zoper tebe (kajti tam ni človeka, ki ne greši) in si jezen nanje in jih izročiš sovražniku, tako da jih odvedejo ujetnike v deželo sovražnika, daleč ali blizu,
47 in suka canja zuciyarsu a ƙasar da aka riƙe su kamammu, suka tuba, suka kuma roƙe ka a ƙasar waɗanda suka ci su da yaƙi, suka ce, ‘Mun yi zunubi, mun yi abin da ba daidai ba, mun yi mugunta’;
vendar če si bodo premislili v deželi, kamor so bili odvedeni ujeti in se pokesajo in naredijo ponižno prošnjo k tebi, v deželi tistih, ki so jih odvedli ujete, rekoč: ›Grešili smo in storili pokvarjeno, zagrešili smo zlobnost‹
48 in sun juye gare ka da dukan zuciyarsu, da dukan ransu a ƙasar abokan gābansu waɗanda suka kwashe kamammu, suka yi addu’a gare ka, suka fuskanci wajen ƙasar da ka ba wa kakanninsu, waje birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka;
in se tako vrnejo k tebi z vsem svojim srcem in z vso svojo dušo v deželi svojih sovražnikov, ki so jih odvedli ujete in molijo k tebi, k svoji deželi, ki si jo dal njihovim očetom, mestu, ki si ga ti izbral in hiši, ki sem jo zgradil za tvoje ime,
49 sai ka ji daga sama, mazauninka, ka ji addu’a da roƙonsu, ka kuma biya musu bukatansu.
potem pozorno poslušaj njihovo molitev in njihovo ponižno prošnjo v nebesih, svojem prebivališču in obravnavaj njihov primer
50 Ka gafarta wa mutanenka, waɗanda suka yi maka zunubi; ka gafarta dukan laifofin da suka yi maka, ka kuma sa waɗanda suka ci su a yaƙi su ji tausayinsu.
in odpusti svojemu ljudstvu, ker so grešili zoper tebe in vse njihove prestopke, s katerimi so se prekršili zoper tebe in jim daj sočutje pred tistimi, ki so jih odvedli ujete, da bodo lahko imeli sočutje do njih,
51 Gama su mutanenka ne, abin gādonka, waɗanda ka fitar daga Masar, daga tanderu mai narken ƙarfe.
kajti oni so tvoje ljudstvo in tvoja dediščina, ki si jo privedel iz Egipta, iz srede železne talilne peči,
52 “Bari idanunka su buɗe ga roƙon bawanka, ga roƙon mutanenka Isra’ila, bari kuma ka saurare su sa’ad da suka yi kuka gare ka.
da bodo tvoje oči lahko odprte k ponižni prošnji tvojega služabnika in k ponižni prošnji tvojega ljudstva Izraela, da jim prisluhneš v vsem, v čemer kličejo k tebi.
53 Gama ka ware su daga dukan al’umman duniya su zama abin gādonka, kamar yadda aka furta ta wurin bawanka Musa sa’ad da kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka ka fitar da kakanninmu daga Masar.”
Kajti oddvojil si jih izmed vsega zemeljskega ljudstva, da bi bili tvoja dediščina, kakor si govoril po roki svojega služabnika Mojzesa, ko si naše očete privedel iz Egipta, oh Gospod Bog.«
54 Da Solomon ya gama dukan waɗannan addu’o’i da roƙe-roƙe ga Ubangiji, sai ya tashi daga gaban bagaden Ubangiji, inda ya durƙusa da hannuwansa a buɗe waje sama.
Bilo je tako, ko je Salomon nehal moliti vso to molitev in ponižno prošnjo h Gospodu, da je vstal izpred Gospodovega oltarja od klečanja na svojih kolenih, s svojima rokama, razširjenima k nebu.
55 Ya tashi ya kuma albarkaci dukan taron Isra’ila da babbar murya, yana cewa,
Vstal je in z močnim glasom blagoslovil vso Izraelovo skupnost, rekoč:
56 “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda ya ba wa mutanensa hutu kamar dai yadda ya yi alkawari. Babu magana guda da ta kāsa cika cikin dukan alkawaransa masu kyau da ya yi ta wurin bawansa Musa.
»Blagoslovljen bodi Gospod, ki je svojemu ljudstvu Izraelu dal počitek, glede na vse, kar je obljubil. Niti ena beseda ni manjkala od vse njegove dobre obljube, ki jo je obljubil po roki svojega služabnika Mojzesa.
57 Bari Ubangiji Allah yă kasance tare da mu kamar yadda ya kasance da kakanninmu; kada yă taɓa rabu da mu, ko yă yashe mu.
Gospod, naš Bog, naj bo z nami, kakor je bil z našimi očeti. Naj nas ne pusti niti naj nas ne zapusti,
58 Bari yă juye zukatanmu gare shi, don mu yi tafiya a cikin dukan hanyoyinsa, mu kuma kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa, da kuma farillan da ya ba wa kakanninmu.
da bo lahko naša srca nagnil k sebi, da hodimo po vseh njegovih poteh in da ohranjamo vse njegove zapovedi, njegove zakone in njegove sodbe, ki jih je zapovedal našim očetom.
59 Bari kuma waɗannan kalmomina, waɗanda na yi addu’a a gaban Ubangiji, su yi kusa da Ubangiji Allahnmu, dare da rana, don yă biya bukatan bawansa da na mutanensa Isra’ila, bisa ga bukatan kowa,
Naj bodo te moje besede, s katerimi sem naredil ponižno prošnjo pred Gospodom, blizu Gospodu, našemu Bogu, podnevi in ponoči, da ohrani zadevo svojega služabnika in zadevo svojega ljudstva Izraela ob vseh časih, kakor bo stvar zahtevala,
60 saboda dukan mutanen duniya su san cewa Ubangiji, shi ne Allah, babu kuma wani.
da bo vse ljudstvo zemlje lahko vedelo, da Gospod je Bog in da tam ni nobenega drugega.
61 Amma dole ku miƙa zukatanku ga Ubangiji Allahnmu, don ku rayu, ta wurin bin ƙa’idodinsa, ku kuma yi biyayya da umarnansa, kamar yadda kuke yi a wannan lokaci.”
Naj bo vaše srce torej popolno z Gospodom, našim Bogom, da se ravna po njegovih zakonih in da ohranja njegove zapovedi, kakor je ta dan.«
62 Sai sarki da dukan Isra’ila, suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
Kralj in ves Izrael z njim je daroval klavno daritev pred Gospodom.
63 Solomon ya miƙa hadaya ta salama ga Ubangiji, shanu dubu ashirin da biyu, tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan Isra’ilawa suka keɓe haikalin Ubangiji.
Salomon je daroval žrtvovanje mirovnih daritev, ki jih je daroval Gospodu, dvaindvajset tisoč volov in sto dvajset tisoč ovc. Tako so kralj in vsi Izraelovi otroci posvetili Gospodovo hišo.
64 A wannan rana sarki ya tsarkake sashe na tsakiyar fili a gaban haikalin Ubangiji, a can kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa, hadaya ta gari, da kitsen hadaya ta salama, gama bagaden tagulla a gaban Ubangiji ya yi ƙanƙanta sosai da za a miƙa hadayun ƙonawa, hadayun hatsi, da kuma kitsen hadayun salama.
Istega dne je kralj posvetil sredino dvora, ki je bila pred Gospodovo hišo, kajti tam je daroval žgalne daritve, jedilne daritve in tolščo mirovnih daritev, ker je bil bronast oltar, ki je bil pred Gospodom, premajhen, da sprejme žgalne daritve, jedilne daritve in tolščo mirovnih daritev.
65 Ta haka Solomon da dukan Isra’ila, wato, babban taro, suka yi bikin a lokacin. Mutane suka zo, tun daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar. Suka yi biki a gaban Ubangiji Allahnmu, kwana bakwai. Suka kuma ƙara kwana bakwai, kwanaki goma sha huɗu gaba ɗaya.
Ob tistem času je Salomon priredil praznovanje in ves Izrael z njim, velika skupnost, od vhoda v Hamát do egiptovske reke, pred Gospodom, svojim Bogom, sedem dni in sedem dni, torej štirinajst dni.
66 A rana ta biye sai ya sallame mutane. Suka sa wa sarki albarka, sa’an nan suka watse zuwa gida, da farin ciki, da murna a zukatansu saboda kyawawan abubuwan da Ubangiji ya yi domin bawansa Dawuda, da kuma mutanensa Isra’ila.
Na osmi dan je ljudstvo odposlal proč in blagoslovili so kralja in radostni in veselega srca zaradi vse dobrote, ki jo je Gospod storil za svojega služabnika Davida in za svoje ljudstvo Izrael, odšli k svojim šotorom.

< 1 Sarakuna 8 >