< 1 Sarakuna 8 >

1 Sai Sarki Solomon ya tattara dattawan Urushalima a gabansa, da dukan shugabannin kabilu, da shugabannin iyalan Isra’ilawa, domin su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Sihiyona, Birnin Dawuda.
Tad ķēniņš Salamans sapulcināja pie sevis Israēla vecajus un visus cilšu priekšniekus un Israēla bērnu tēvu namu virsniekus Jeruzālemē pie ķēniņa Salamana, pārvest Tā Kunga derības šķirstu no Dāvida pilsētas, - šī ir Ciāna.
2 Dukan mutanen Isra’ila suka tattaru a gaban Sarki Solomon a lokacin biki, a watan Etanim, wato, wata na bakwai.
Un visi Israēla vīri sapulcējās pie ķēniņa Salamana uz svētkiem Etanim mēnesī, šis ir tas septītais mēnesis.
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka iso, sai firistoci suka ɗauki akwatin alkawarin,
Un kad visi Israēla vecaji sanāca, tad priesteri ņēma to šķirstu
4 suka haura da akwatin alkawarin Ubangiji da kuma Tentin Sujada, da dukan kayayyaki masu tsarkin da suke cikinsa. Firistoci da Lawiyawa suka ɗauko su,
Un nesa Tā Kunga šķirstu un saiešanas telti ar visiem svētiem rīkiem, kas bija teltī, tos priesteri un Leviti nesa.
5 sai Sarki Solomon da dukan taron Isra’ila da suka tattaru kewaye da shi a gaban akwatin alkawari, suka yi ta miƙa hadayar tumaki da bijimai masu yawa da ba a iya lissaftawa, ko ƙirgawa.
Un ķēniņš Salamans un visa Israēla draudze, kas pie viņa bija sapulcējusies, gāja viņam līdz šķirsta priekšā, un upurēja avis un vēršus, neizskaitāmu pulku un neizzināmu skaitu.
6 Sa’an nan firistoci suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji inda aka shirya masa, can ciki cikin haikali, a Wuri Mafi Tsarki, aka kuma sa shi a ƙarƙashin fikafikan kerubobin.
Tā priesteri nesa Tā Kunga derības šķirstu savā vietā, Dieva nama dziļumā, visusvētajā vietā, apakš ķerubu spārniem.
7 Kerubobin sun buɗe fikafikansu a bisa wurin da akwatin alkawarin yake, suka inuwartar da akwatin alkawarin da sandunan ɗaukansa.
Jo tie ķerubi izplēta savus spārnus pār šķirsta vietu, un tie ķerubi apklāja šķirstu un viņa nesamās kārtis no augšienes.
8 Waɗannan sandunan sun yi tsawo har ana iya ganin bakinsu daga Wuri Mai Tsarki a gaban wuri mai tsarki na can ciki, amma ba a iya ganinsu daga waje na Wuri Mai Tsarki ba. Suna nan kuwa a can har wa yau.
Un tās nesamās kārtis bija tik garas, ka kāršu gali bija redzami no tās svētās vietas tās visusvētās vietas priekšā, bet ārpusē tās nebija redzamas, un tās tur ir līdz šai dienai.
9 Ba kome a cikin akwatin alkawarin, sai dai alluna na dutse guda biyu waɗanda Musa ya ajiye a ciki tun a Horeb, inda Ubangiji ya yi alkawari da Isra’ilawa bayan sun fito Masar.
Tai šķirstā nebija nekā, kā vien tie abi akmens galdiņi, ko Mozus Horebā bija ielicis, kad Tas Kungs derību derēja ar Israēla bērniem, kad tie izgāja no Ēģiptes zemes.
10 Sa’ad da firistoci suka janye daga Wuri Mai Tsarki, sai girgije ya cika haikalin Ubangiji.
Kad nu tie priesteri izgāja no tās svētās vietas, tad mākonis piepildīja Tā Kunga namu;
11 Firistocin kuwa ba su iya yin hidimarsu ba saboda girgijen, gama ɗaukakar Ubangiji ta cika haikalinsa.
Un tie priesteri nevarēja stāvēt un kalpot tā mākoņa dēļ. Jo Tā Kunga godība bija piepildījusi Tā Kunga namu.
12 Sai Solomon ya ce, “Ubangiji ya ce zai zauna a gizagizai masu duhu;
Tad Salamans sacīja: Tas Kungs ir sacījis, ka viņš tumsā gribot dzīvot.
13 ga shi na gina haikali mai daraja dominka, inda za ka zauna har abada.”
Celt esmu cēlis namu tev par dzīvokli, mājokli, tev mājot mūžīgi.
14 Yayinda dukan taron Isra’ila suke tsattsaye a can, sai sarki ya juya ya albarkace su.
Tad ķēniņš atgrieza savu vaigu un svētīja visu Israēla draudzi, un visa Israēla draudze stāvēja, un viņš sacīja:
15 Sa’an nan ya ce, “Ku yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda da hannunsa ya cika abin da ya yi alkawari da bakinsa ga mahaifina Dawuda. Gama ya ce,
Slavēts lai ir Tas Kungs, Israēla Dievs, kas ar Savu muti runājis uz manu tēvu Dāvidu un ar Savu roku to piepildījis, ko Viņš sacījis:
16 ‘Tun ran da na fitar da mutanena Isra’ila daga Masar, ban zaɓi wani birni a cikin wata kabilar Isra’ila a gina haikali domin Sunana yă kasance a can ba, amma na zaɓi Dawuda yă yi mulkin mutanena Isra’ila.’
No tās dienas, kad Es savus Israēla ļaudis esmu izvedis no Ēģiptes, Es nevienu pilsētu neesmu izredzējis starp visām Israēla ciltīm, taisīt namu, lai Mans vārds tur būtu. Bet Dāvidu Es esmu izredzējis, ka tas būtu pār Maniem Israēla ļaudīm.
17 “Mahaifina Dawuda ya yi niyya a cikin zuciyarsa yă gina haikali saboda Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Un manam tēvam Dāvidam gan bija prātā, taisīt namu Tā Kunga, Israēla Dieva, vārdam.
18 Amma Ubangiji ya ce wa mahaifina Dawuda, ‘Saboda yana a zuciyarka ka gina haikali domin Sunana, ka yi daidai da ka yi niyyar wannan a zuciyarka.
Bet Tas Kungs sacīja uz manu tēvu Dāvidu: ka tu savā sirdī esi apņēmies, taisīt namu Manam vārdam, to tu gan esi labi darījis, ka tas tavā sirdī.
19 Duk da haka, ba kai ba ne za ka gina haikali, amma ɗanka, wanda yake namanka da jininka, shi ne wanda zai gina haikali domin Sunana.’
Bet tev to namu nebūs taisīt, bet tavam dēlam, kas nāks no taviem gurniem, tas uztaisīs namu Manam vārdam.
20 “Ubangiji ya kiyaye alkawarin da ya yi. Na gāje Dawuda mahaifina, yanzu kuma ga shi na zauna a kujerar sarautar Isra’ila, kamar dai yadda Ubangiji ya yi alkawari, na kuma gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Un Tas Kungs savu vārdu ir apstiprinājis, ko Viņš runājis. Jo es esmu stājies sava tēva Dāvida vietā, un sēžu uz Israēla goda krēsla, itin kā Tas Kungs runājis, un es esmu uztaisījis namu Tā Kunga, Israēla Dieva, vārdam.
21 Na tanada wuri saboda akwatin alkawari, akwatin da ya ƙunshi alkawarin da Ubangiji ya yi da kakanninmu sa’ad da ya fitar da su daga Masar.”
Un tur esmu taisījis vietu tam šķirstam, kur Tā Kunga derība, ko Viņš derējis ar mūsu tēviem, kad Viņš tos izveda no Ēģiptes zemes.
22 Sai Solomon ya tsaya a gaban bagaden Ubangiji, a gaban dukan taron Isra’ila, ya ɗaga hannuwansa sama,
Un Salamans stājās Tā Kunga altāra priekšā, visai Israēla draudzei pretī, un izplēta savas rokas pret debesīm un sacīja:
23 ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, babu Allah kamar ka a sama can bisa, ko a ƙasa can ƙarƙashi, kai da kake kiyaye alkawarinka na ƙauna ga bayinka waɗanda suke cin gaba a hanyarka da dukan zuciyarsu.
Kungs, Israēla Dievs, neviena tāda Dieva nav kā Tu, ne augšā debesīs, nedz apakšā virs zemes; derību un žēlastību Tu turi Saviem kalpiem, kas Tavā priekšā staigā no visas savas sirds.
24 Ka kiyaye alkawarinka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina. Da bakinka ka yi alkawari, da hannunka kuma ka cika shi, yadda yake a yau.
Tu Savam kalpam, manam tēvam Dāvidam, esi turējis, ko tam esi runājis. Ar Savu muti Tu esi runājis un ar Savu roku to piepildījis, tā kā tas šodien ir.
25 “Yanzu, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bari ka cika wa bawanka Dawuda mahaifina alkawaran da ka yi masa sa’ad da ka ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani da zai zauna a gabana a kan kujerar sarautar Isra’ila ba, in kawai’ya’yanka maza sun yi hankali cikin dukan abubuwan da suke yi, don su yi tafiya a gabana kamar yadda ka yi.’
Un nu Kungs, Israēla Dievs, turi Savam kalpam, manam tēvam Dāvidam, arī to, ko Tu tam vēl esi runājis sacīdams: tev netrūks vīra Manā priekšā, kas sēdēs uz Israēla goda krēsla, ja tikai tavi dēli sargās savu ceļu, staigādami Manā priekša, itin kā tu esi staigājis Manā priekšā.
26 Yanzu fa, ya Allah na Isra’ila, bari maganarka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina tă cika.
Nu tad, Israēla Dievs, lai jel Tavs vārds tiešām notiek, ko Tu esi runājis Savam kalpam, manam tēvam Dāvidam!
27 “Amma anya, Allah, za ka zauna a duniya? Sammai, har ma da saman sammai ba za tă iya riƙe ka ba, balle wannan haikalin da na gina!
Vai tad patiesi Tas Kungs dzīvotu virs zemes? Redzi, debesis un visu debesu debesis Tevi nevar saņemt, kā tad nu vēl šis nams, ko es esmu taisījis.
28 Duk da haka ka ji addu’ar bawanka da kuma roƙonsa don jinƙai, ya Ubangiji Allahna. Ka ji kuka da addu’ar da bawanka yake yi a gabanka a wannan rana.
Bet griezies pie Sava kalpa lūgšanām un pie viņa piesaukšanām, Kungs, mans Dievs, un klausi to saukšanu un lūgšanu, ko Tavs kalps šodien lūdz priekš Tava vaiga.
29 Bari idanunka su buɗe, su fuskanci wannan haikali dare da rana, wannan wurin da ka ce, ‘Sunana zai kasance a can,’ saboda ka ji addu’ar bawanka in yana fuskantar wannan wuri.
Lai Tavas acis stāv atvērtas dienām naktīm pār šo namu, pār šo vietu, par ko Tu esi sacījis: Mans vārds lai tur ir; ka Tu klausi to lūgšanu, ko Tavs kalps lūgs šinī vietā.
30 Ka ji roƙon bawanka da kuma na mutanenka Isra’ila sa’ad da suka yi addu’a, suka fuskanci wannan wuri. Ka ji daga sama, mazauninka, kuma sa’ad da ka ji, ka gafarta.
Klausi tad Sava kalpa un Savu Israēla ļaužu sirds lūgšanu, ko tie lūgs šinī vietā, un klausi, kur Tu mīti debesīs, ak klausi un piedod!
31 “Sa’ad da mutum ya yi abin da ba daidai ba ga maƙwabcinsa, an kuma bukace shi yă yi rantsuwa, sai ya zo ya rantse a gaban bagade a cikin haikalin nan,
Ja kāds būs apgrēkojies pret savu tuvāko un viņam liks zvērēt un nodievoties, un šis nāks un zvērēs priekš Tava altāra šinī namā,
32 sai ka ji daga sama, ka kuma yi wani abu. Ka shari’anta tsakanin bayinka, ka hukunta mai laifi, ka mai da laifinsa a kansa, mai gaskiya kuma ka nuna shi marar laifi ne bisa ga gaskiyarsa.
Tad klausi Tu debesīs un dari un tiesā Savus kalpus, netaisno notiesādams un atmaksādams viņa ceļu uz viņa galvu, un taisno taisnodams, dodams viņam pēc viņa taisnības.
33 “Sa’ad da abokan gāba suka ci mutanenka Isra’ila a yaƙi saboda sun yi maka zunubi, sa’ad da kuma suka dawo gare ka don su furta sunanka, suna addu’a suna roƙo gare ka a wannan haikali,
Kad Tavi Israēla ļaudis taps kauti savu ienaidnieku priekšā, tāpēc ka tie pret Tevi būs grēkojuši, un kad tie pie Tevis atgriezīsies un dos godu Tavam vārdam un Tevi pielūgs un no sirds piesauks šinī namā,
34 ka ji daga sama, ka gafarta zunubin mutanenka, ka kuma dawo da su ƙasar da ka ba wa kakanninsu.
Tad klausi Tu debesīs un piedod Savu Israēla ļaužu grēkus un ved tos atkal tai zemē, ko Tu esi devis viņu tēviem.
35 “Sa’ad da sammai sun kulle, babu kuma ruwan sama domin mutane sun yi maka zunubi, sa’ad da suka yi addu’a suna fuskantar wannan wuri, suka kuma furta sunanka, suka juye daga zunubinsu domin ka hore su,
Kad debess būs aizslēgta, ka lietus nelīst, tāpēc ka tie pret Tevi grēkojuši, un kad tie šinī vietā lūgs un dos godu Tavam vārdam un atgriezīsies no saviem grēkiem, kad Tu tos pazemojis,
36 ka ji daga sama, ka kuma gafarta zunubin bayinka, mutanenka Isra’ila. Ka koya musu hanyar da ta dace ta rayuwa, ka kuma aika da ruwan sama a ƙasar da ka ba wa mutanenka gādo.
Tad klausi Tu debesīs un piedod Savu kalpu un Savu Israēla ļaužu grēkus, ka Tu tiem parādi to labo ceļu, kur tiem jāstaigā, un dod lietu tai zemē, ko Tu devis Saviem ļaudīm par mantību.
37 “Sa’ad da yunwa ko annoba ta fāɗo a ƙasar, ko burtuntuna, ko fumfuna, ko fāri, ko tsutsa, ko kuwa abokan gāba sun yi musu kwanto, a wani daga cikin biranensu, duk wata cuta, ko ciwon da ya zo,
Kad zemei būs bads, kad būs mēris, bula laiks, rūsa, siseņi, kukaiņi, kad viņu ienaidnieks zemē ielauzīsies pret viņu vārtiem, vai būs kāda cita mocība vai sērga,
38 in suka yi addu’a ko roƙo ta wurin wani daga cikin mutanenka Isra’ila, kowa ya san wahalar zuciyarsa, ya kuma buɗe hannuwansa yana fuskantar wannan haikali,
Visas lūgšanas, visas piesaukšanas, lai lūgtu kas lūgdams no visiem Taviem Israēla ļaudīm, kad tie atzīs savas sirds bēdas un izplētīs savas rokas šinī namā,
39 sai ka ji daga sama, mazauninka. Ka gafarta, ka kuma yi wani abu. Ka yi da kowane mutum bisa ga dukan abin da ya yi, tun da yake ka san zuciyarsa (gama kai kaɗai ka san zukatan dukan mutane),
Tad klausi Tu debesīs, Savā mājoklī, kur Tu mīti, un piedod un dari un dod ikvienam pēc visiem viņa ceļiem, itin kā Tu pazīsti viņa sirdi, jo Tu vien pazīsti visu cilvēka bērnu sirdis; -
40 saboda su ji tsoronka a kowane lokacin da suke zaune a ƙasar da ka ba wa kakanninmu.
Lai tie Tevi bīstas visu savu mūžu, kamēr tie dzīvos tai zemē, ko Tu esi devis mūsu tēviem.
41 “Game da baƙo kuwa wanda shi ba na mutanenka Isra’ila ba, amma ya zo daga ƙasa mai nisa saboda sunanka,
Kad arī kāds svešinieks būs, kas nav no taviem Israēla ļaudīm, bet atnācis no tālas zemes Tava vārda dēļ,
42 gama mutane za su ji game da girman sunanka, da ƙarfin hannunka, da kuma hannunka mai iko, sa’ad da ya zo, ya yi addu’a yana fuskantar wannan haikali,
(Jo tie dzirdēs par Tavu lielo vārdu un par Tavu stipro roku un par Tavu izstiepto elkoni, ) un kad tas nāks un pielūgs šinī namā,
43 ka ji daga sama, mazauninka, ka kuma yi dukan abin da baƙon ya tambaye ka, saboda dukan mutanen duniya su san sunanka, su kuma ji tsoronka, kamar yadda mutanenka Isra’ila suke yi, bari kuma su san cewa wannan gidan da na gina, ya amsa Sunanka.
Tad klausi Tu debesīs, Savā mājoklī, kur Tu mīti, un dari visu, par ko tas svešais Tevi piesauks, lai visas tautas virs zemes atzīst Tavu vārdu un Tevi bīstas, kā Tavi Israēla ļaudis, un lai tie atzīst, ka Tavs vārds ir saukts pār šo namu, ko es esmu uztaisījis.
44 “Sa’ad da mutanenka suka tafi yaƙi da abokan gābansu, a duk inda ka aike su, sa’ad da kuma suka yi addu’a ga Ubangiji suna fuskantar birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka,
Kad Tavi ļaudis ies karā pret saviem ienaidniekiem tai ceļā, kur Tu tos sūtīsi, un pielūgs To Kungu, griezušies uz šo pilsētu, ko Tu esi izredzējis, un uz šo namu, ko es tavam vārdam esmu uztaisījis,
45 ka ji addu’arsu da roƙonsu daga sama, ka kuma biya musu bukatansu.
Tad klausi Tu debesīs viņu lūgšanas un viņu sirds saukšanas un nes viņiem tiesu.
46 “Sa’ad da suka yi maka zunubi, gama babu wanda ba ya zunubi, ka kuwa yi fushi da su, ka kuma ba da su ga abokin gāba, wanda ya kwashe su kamammu zuwa ƙasarsa, nesa ko kusa;
Kad tie pret Tevi apgrēkosies, (jo neviena cilvēka nav, kas negrēkotu) un Tu par tiem dusmosies, un tos nodosi ienaidniekiem, ka viņu uzvarētāji tos cietumā noved ienaidnieku zemē, vai tālu, vai tuvu,
47 in suka canja zuciyarsu a ƙasar da aka riƙe su kamammu, suka tuba, suka kuma roƙe ka a ƙasar waɗanda suka ci su da yaƙi, suka ce, ‘Mun yi zunubi, mun yi abin da ba daidai ba, mun yi mugunta’;
Un kad tie to atkal ņems pie sirds tai zemē, kur tie cietumā aizvesti, un atgriezīsies un Tevi piesauks sava cietuma zemē sacīdami: mēs esam grēkojuši un ļaunu darījuši, mēs esam bezdievīgi bijuši;
48 in sun juye gare ka da dukan zuciyarsu, da dukan ransu a ƙasar abokan gābansu waɗanda suka kwashe kamammu, suka yi addu’a gare ka, suka fuskanci wajen ƙasar da ka ba wa kakanninsu, waje birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka;
Un kad tie pie Tevis atgriezīsies no visas savas sirds un no visas savas dvēseles savu ienaidnieku zemē, kas tos aizveduši cietumā, un kad tie Tevi pielūgs, griezušies uz savu zemi, ko Tu devis viņu tēviem, uz to pilsētu, ko Tu izredzējis, un uz to namu, ko es tavam vārdam uztaisījis,
49 sai ka ji daga sama, mazauninka, ka ji addu’a da roƙonsu, ka kuma biya musu bukatansu.
Tad klausi Tu debesīs, Savā mājoklī, kur Tu mīti, viņu lūgšanu un viņu sirds saukšanu un nes viņiem tiesu,
50 Ka gafarta wa mutanenka, waɗanda suka yi maka zunubi; ka gafarta dukan laifofin da suka yi maka, ka kuma sa waɗanda suka ci su a yaƙi su ji tausayinsu.
Un piedod Saviem ļaudīm, ko tie pret Tevi grēkojuši, un visus viņu pārkāpumus, ar ko tie pret Tevi noziegušies, un dod tiem žēlastību atrast pie tiem, kas tos cietumā tur, ka tie par viņiem apžēlojās;
51 Gama su mutanenka ne, abin gādonka, waɗanda ka fitar daga Masar, daga tanderu mai narken ƙarfe.
Jo tie ir Tavi ļaudis un Tavs īpašums, ko Tu esi izvedis no Ēģiptes no tā dzelzs cepļa.
52 “Bari idanunka su buɗe ga roƙon bawanka, ga roƙon mutanenka Isra’ila, bari kuma ka saurare su sa’ad da suka yi kuka gare ka.
Lai Tavas acis atvērtas stāv uz Tava kalpa lūgšanu un uz Tavu Israēla ļaužu lūgšanu, ka Tu tos klausi visās lietās, par ko tie Tevi piesauc.
53 Gama ka ware su daga dukan al’umman duniya su zama abin gādonka, kamar yadda aka furta ta wurin bawanka Musa sa’ad da kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka ka fitar da kakanninmu daga Masar.”
Jo Tu tos Sev esi izredzējis par īpašumu no visām pasaules tautām, itin kā Tu esi runājis caur Savu kalpu Mozu, kad Tu mūsu tēvus izvedi no Ēģiptes zemes, Kungs, Dievs!
54 Da Solomon ya gama dukan waɗannan addu’o’i da roƙe-roƙe ga Ubangiji, sai ya tashi daga gaban bagaden Ubangiji, inda ya durƙusa da hannuwansa a buɗe waje sama.
Un notikās, kad Salamans bija pabeidzis lūgt šo lūgšanu un sirds saukšanu uz To Kungu, tad viņš pacēlās priekš Tā Kunga altāra, kur viņš bija ceļos nometies un savas rokas izpletis pret debesīm,
55 Ya tashi ya kuma albarkaci dukan taron Isra’ila da babbar murya, yana cewa,
Un viņš nostājās un svētīja visu Israēla draudzi ar stipru balsi un sacīja:
56 “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda ya ba wa mutanensa hutu kamar dai yadda ya yi alkawari. Babu magana guda da ta kāsa cika cikin dukan alkawaransa masu kyau da ya yi ta wurin bawansa Musa.
Slavēts lai ir Tas Kungs, kas dusu devis Saviem Israēla ļaudīm, itin kā Viņš runājis; neviens vārds nav zemē kritis no visiem Viņa labiem vārdiem, ko Viņš runājis caur Savu kalpu Mozu.
57 Bari Ubangiji Allah yă kasance tare da mu kamar yadda ya kasance da kakanninmu; kada yă taɓa rabu da mu, ko yă yashe mu.
Lai Tas Kungs, mūsu Dievs, ir ar mums, itin kā Viņš bijis ar mūsu tēviem. Viņš lai mūs neatstāj un lai mūs neatmet.
58 Bari yă juye zukatanmu gare shi, don mu yi tafiya a cikin dukan hanyoyinsa, mu kuma kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa, da kuma farillan da ya ba wa kakanninmu.
Lai Viņš mūsu sirdis griež pie Sevis, ka mēs staigājam visos Viņa ceļos, turēdami Viņa baušļus un Viņa likumus un Viņa tiesas, ko Viņš pavēlējis mūsu tēviem.
59 Bari kuma waɗannan kalmomina, waɗanda na yi addu’a a gaban Ubangiji, su yi kusa da Ubangiji Allahnmu, dare da rana, don yă biya bukatan bawansa da na mutanensa Isra’ila, bisa ga bukatan kowa,
Un lai šie vārdi, ar ko es lūdzis Tā Kunga priekšā, tuvu ir pie Tā Kunga, mūsu Dieva, dienām naktīm, lai Viņš tiesu nes Savam kalpam un Saviem Israēla ļaudīm dienu no dienas,
60 saboda dukan mutanen duniya su san cewa Ubangiji, shi ne Allah, babu kuma wani.
Lai visas pasaules tautas atzīst, ka Tas Kungs ir Dievs un cits neviens.
61 Amma dole ku miƙa zukatanku ga Ubangiji Allahnmu, don ku rayu, ta wurin bin ƙa’idodinsa, ku kuma yi biyayya da umarnansa, kamar yadda kuke yi a wannan lokaci.”
Un lai jūsu sirds paliek pilnīgi pie Tā Kunga, mūsu Dieva, ka jūs staigājat Viņa likumos un turat Viņa baušļus, tāpat kā šodien.
62 Sai sarki da dukan Isra’ila, suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
Un ķēniņš un viss Israēls līdz ar viņu upurēja upurus Tā Kunga priekšā.
63 Solomon ya miƙa hadaya ta salama ga Ubangiji, shanu dubu ashirin da biyu, tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan Isra’ilawa suka keɓe haikalin Ubangiji.
Un Salamans upurēja pateicības upurus, ko viņš Tam Kungam atnesa, divdesmit un divtūkstoš vēršus un simts un divdesmit tūkstoš avis. Tā ķēniņš ar visiem Israēla bērniem iesvētīja Tā Kunga namu.
64 A wannan rana sarki ya tsarkake sashe na tsakiyar fili a gaban haikalin Ubangiji, a can kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa, hadaya ta gari, da kitsen hadaya ta salama, gama bagaden tagulla a gaban Ubangiji ya yi ƙanƙanta sosai da za a miƙa hadayun ƙonawa, hadayun hatsi, da kuma kitsen hadayun salama.
Tai dienā ķēniņš svētīja to iekšējo pagalmu, kas Tā Kunga nama priekšā, jo viņš tur upurēja dedzināmu upuri un ēdamu upuri un pateicības upuru taukus. Jo tas vara altāris Tā Kunga priekšā bija pa mazu priekš tā dedzināma upura un tā ēdama upura un tiem pateicības upuru taukiem.
65 Ta haka Solomon da dukan Isra’ila, wato, babban taro, suka yi bikin a lokacin. Mutane suka zo, tun daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar. Suka yi biki a gaban Ubangiji Allahnmu, kwana bakwai. Suka kuma ƙara kwana bakwai, kwanaki goma sha huɗu gaba ɗaya.
Un tanī laikā Salamans noturēja svētkus ar visu Israēli, lielu draudzi no Hamata robežas līdz Ēģiptes upei Tā Kunga, mūsu Dieva, priekšā, septiņas dienas un atkal septiņas dienas, pavisam četrpadsmit dienas; astotā dienā viņš tos ļaudis atlaida.
66 A rana ta biye sai ya sallame mutane. Suka sa wa sarki albarka, sa’an nan suka watse zuwa gida, da farin ciki, da murna a zukatansu saboda kyawawan abubuwan da Ubangiji ya yi domin bawansa Dawuda, da kuma mutanensa Isra’ila.
Un tie svētīja ķēniņu un gāja uz saviem dzīvokļiem priecīgi un ar līksmu sirdi par visu to labumu, ko Tas Kungs bija darījis Savam kalpam Dāvidam un Saviem Israēla ļaudīm.

< 1 Sarakuna 8 >