< 1 Sarakuna 8 >

1 Sai Sarki Solomon ya tattara dattawan Urushalima a gabansa, da dukan shugabannin kabilu, da shugabannin iyalan Isra’ilawa, domin su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Sihiyona, Birnin Dawuda.
Alors Salomon assembla devant lui à Jérusalem les Anciens d'Israël, et tous les chefs des Tribus, les principaux des pères des enfants d'Israël, pour transporter l'Arche de l'alliance de l'Eternel de la Cité de David, qui est Sion.
2 Dukan mutanen Isra’ila suka tattaru a gaban Sarki Solomon a lokacin biki, a watan Etanim, wato, wata na bakwai.
Et tous ceux d'Israël furent assemblés vers le Roi Salomon, au mois d'Ethanim, qui est le septième mois, le jour même de la fête.
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka iso, sai firistoci suka ɗauki akwatin alkawarin,
Tous les Anciens d'Israël donc vinrent; et les Sacrificateurs portèrent l'Arche.
4 suka haura da akwatin alkawarin Ubangiji da kuma Tentin Sujada, da dukan kayayyaki masu tsarkin da suke cikinsa. Firistoci da Lawiyawa suka ɗauko su,
Ainsi on transporta l'Arche de l'Eternel, et le Tabernacle d'assignation, et tous les saints vaisseaux qui étaient au Tabernacle; les Sacrificateurs, dis-je, et les Lévites les emportèrent.
5 sai Sarki Solomon da dukan taron Isra’ila da suka tattaru kewaye da shi a gaban akwatin alkawari, suka yi ta miƙa hadayar tumaki da bijimai masu yawa da ba a iya lissaftawa, ko ƙirgawa.
Or le Roi Salomon, et toute l'assemblée d'Israël qui s'était rendue auprès de lui, étaient ensemble devant l'Arche [et] ils sacrifiaient du gros et du menu bétail en si grand nombre, qu'on ne le pouvait ni nombrer ni compter.
6 Sa’an nan firistoci suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji inda aka shirya masa, can ciki cikin haikali, a Wuri Mafi Tsarki, aka kuma sa shi a ƙarƙashin fikafikan kerubobin.
Et les Sacrificateurs portèrent l'Arche de l'Alliance de l'Eternel en son lieu, dans l'Oracle de la maison, au lieu Très-saint, sous les ailes des Chérubins.
7 Kerubobin sun buɗe fikafikansu a bisa wurin da akwatin alkawarin yake, suka inuwartar da akwatin alkawarin da sandunan ɗaukansa.
Car les Chérubins étendaient les ailes sur l'endroit où devait être l'Arche, et les Chérubins couvraient l'Arche et ses barres, par dessus.
8 Waɗannan sandunan sun yi tsawo har ana iya ganin bakinsu daga Wuri Mai Tsarki a gaban wuri mai tsarki na can ciki, amma ba a iya ganinsu daga waje na Wuri Mai Tsarki ba. Suna nan kuwa a can har wa yau.
Et ils retirèrent les barres en dedans, de sorte que les bouts des barres se voyaient du lieu Saint sur le devant de l'Oracle, mais ils ne se voyaient point au dehors; et elles sont demeurées là jusqu'à ce jour.
9 Ba kome a cikin akwatin alkawarin, sai dai alluna na dutse guda biyu waɗanda Musa ya ajiye a ciki tun a Horeb, inda Ubangiji ya yi alkawari da Isra’ilawa bayan sun fito Masar.
Il n'y avait rien dans l'Arche que les deux tables de pierre que Moïse y avait mises en Horeb, quand l'Eternel traita [alliance] avec les enfants d'Israël, lorsqu'ils furent sortis du pays d'Egypte.
10 Sa’ad da firistoci suka janye daga Wuri Mai Tsarki, sai girgije ya cika haikalin Ubangiji.
Or il arriva que comme les Sacrificateurs furent sortis du lieu Saint, une nuée remplit la maison de l'Eternel.
11 Firistocin kuwa ba su iya yin hidimarsu ba saboda girgijen, gama ɗaukakar Ubangiji ta cika haikalinsa.
De sorte que les Sacrificateurs ne se pouvaient tenir debout pour faire le service, à cause de la nuée; car la gloire de l'Eternel avait rempli la maison de l'Eternel.
12 Sai Solomon ya ce, “Ubangiji ya ce zai zauna a gizagizai masu duhu;
Alors Salomon dit: L'Eternel a dit qu'il habiterait dans l'obscurité.
13 ga shi na gina haikali mai daraja dominka, inda za ka zauna har abada.”
J'ai achevé, [ô Eternel!] de bâtir une maison pour ta demeure, un domicile fixe, afin que tu y habites éternellement.
14 Yayinda dukan taron Isra’ila suke tsattsaye a can, sai sarki ya juya ya albarkace su.
Et le Roi tournant son visage, bénit toute l'assemblée d'Israël; car toute l'assemblée d'Israël se tenait [là] debout.
15 Sa’an nan ya ce, “Ku yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda da hannunsa ya cika abin da ya yi alkawari da bakinsa ga mahaifina Dawuda. Gama ya ce,
Et il dit: Béni soit l'Eternel, le Dieu d'Israël, qui a parlé de sa propre bouche à David mon père, et qui l'a accompli par sa puissance, et a dit:
16 ‘Tun ran da na fitar da mutanena Isra’ila daga Masar, ban zaɓi wani birni a cikin wata kabilar Isra’ila a gina haikali domin Sunana yă kasance a can ba, amma na zaɓi Dawuda yă yi mulkin mutanena Isra’ila.’
Depuis le jour que je retirai mon peuple d'Israël hors d'Egypte, je n'ai choisi aucune ville d'entre toutes les Tribus d'Israël pour y bâtir une maison, afin que mon Nom y fût; mais j'ai choisi David, afin qu'il eût la charge de mon peuple d'Israël.
17 “Mahaifina Dawuda ya yi niyya a cikin zuciyarsa yă gina haikali saboda Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Et David mon père avait au cœur de bâtir une maison au Nom de l'Eternel, le Dieu d'Israël.
18 Amma Ubangiji ya ce wa mahaifina Dawuda, ‘Saboda yana a zuciyarka ka gina haikali domin Sunana, ka yi daidai da ka yi niyyar wannan a zuciyarka.
Mais l'Eternel dit à David mon père: Quant à ce que tu as eu au cœur de bâtir une maison à mon Nom, tu as bien fait d'avoir eu cela au cœur.
19 Duk da haka, ba kai ba ne za ka gina haikali, amma ɗanka, wanda yake namanka da jininka, shi ne wanda zai gina haikali domin Sunana.’
Néanmoins tu ne bâtiras point cette maison, mais ton fils qui sortira de tes reins, sera celui qui bâtira cette maison à mon Nom.
20 “Ubangiji ya kiyaye alkawarin da ya yi. Na gāje Dawuda mahaifina, yanzu kuma ga shi na zauna a kujerar sarautar Isra’ila, kamar dai yadda Ubangiji ya yi alkawari, na kuma gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
L'Eternel a donc accompli sa parole, qu'il avait prononcée, et j'ai succédé à David mon père, et je suis assis sur le trône d'Israël, comme l'Eternel en avait parlé; et j'ai bâti cette maison au Nom de l'Eternel le Dieu d'Israël.
21 Na tanada wuri saboda akwatin alkawari, akwatin da ya ƙunshi alkawarin da Ubangiji ya yi da kakanninmu sa’ad da ya fitar da su daga Masar.”
Et j'ai assigné ici un lieu à l'Arche, dans laquelle est l'alliance de l'Eternel, qu'il traita avec nos pères, quand il les eut tirés hors du pays d'Egypte.
22 Sai Solomon ya tsaya a gaban bagaden Ubangiji, a gaban dukan taron Isra’ila, ya ɗaga hannuwansa sama,
Ensuite Salomon se tint devant l'autel de l'Eternel en la présence de toute l'assemblée d'Israël, et ayant ses mains étendues vers les cieux,
23 ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, babu Allah kamar ka a sama can bisa, ko a ƙasa can ƙarƙashi, kai da kake kiyaye alkawarinka na ƙauna ga bayinka waɗanda suke cin gaba a hanyarka da dukan zuciyarsu.
Il dit: Ô Eternel Dieu d'Israël! il n'y a point de Dieu semblable à toi dans les cieux en haut, ni sur la terre en bas; tu gardes l'alliance et la gratuité envers tes serviteurs, qui marchent de tout leur cœur devant ta face.
24 Ka kiyaye alkawarinka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina. Da bakinka ka yi alkawari, da hannunka kuma ka cika shi, yadda yake a yau.
[Et] tu as tenu à ton serviteur David mon père ce dont tu lui avais parlé; car ce dont tu lui avais parlé de ta bouche, tu l'as accompli de ta main, comme [il paraît] aujourd'hui.
25 “Yanzu, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bari ka cika wa bawanka Dawuda mahaifina alkawaran da ka yi masa sa’ad da ka ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani da zai zauna a gabana a kan kujerar sarautar Isra’ila ba, in kawai’ya’yanka maza sun yi hankali cikin dukan abubuwan da suke yi, don su yi tafiya a gabana kamar yadda ka yi.’
Maintenant donc, ô Eternel Dieu d'Israël! tiens à ton serviteur David mon père, ce dont tu lui as parlé, en disant: Jamais il ne te sera retranché de devant ma face un [successeur] pour être assis sur le trône d'Israël, pourvu seulement que tes fils prennent garde à leur voie, afin de marcher devant ma face, comme tu y as marché.
26 Yanzu fa, ya Allah na Isra’ila, bari maganarka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina tă cika.
Et maintenant, ô Dieu d'Israël! je te prie, que ta parole, laquelle tu as prononcée à ton serviteur David mon père, soit ratifiée.
27 “Amma anya, Allah, za ka zauna a duniya? Sammai, har ma da saman sammai ba za tă iya riƙe ka ba, balle wannan haikalin da na gina!
Mais Dieu habiterait-il effectivement sur la terre? Voilà, les cieux, même les cieux des cieux ne te peuvent contenir; combien moins cette maison que j'ai bâtie.
28 Duk da haka ka ji addu’ar bawanka da kuma roƙonsa don jinƙai, ya Ubangiji Allahna. Ka ji kuka da addu’ar da bawanka yake yi a gabanka a wannan rana.
Toutefois, ô Eternel mon Dieu! aie égard à la prière de ton serviteur, et à sa supplication, pour entendre le cri et la prière que ton serviteur te fait aujourd'hui;
29 Bari idanunka su buɗe, su fuskanci wannan haikali dare da rana, wannan wurin da ka ce, ‘Sunana zai kasance a can,’ saboda ka ji addu’ar bawanka in yana fuskantar wannan wuri.
[Qui est], que tes yeux soient ouverts jour et nuit sur cette maison, le lieu dont tu as dit: Mon nom sera là, pour exaucer la prière que ton serviteur fait en ce lieu-ci.
30 Ka ji roƙon bawanka da kuma na mutanenka Isra’ila sa’ad da suka yi addu’a, suka fuskanci wannan wuri. Ka ji daga sama, mazauninka, kuma sa’ad da ka ji, ka gafarta.
Exauce donc la supplication de ton serviteur, et de ton peuple d'Israël quand ils te prieront en ce lieu-ci; exauce[-les], [dis-je], du lieu de ta demeure, des cieux; exauce, et pardonne.
31 “Sa’ad da mutum ya yi abin da ba daidai ba ga maƙwabcinsa, an kuma bukace shi yă yi rantsuwa, sai ya zo ya rantse a gaban bagade a cikin haikalin nan,
Quand quelqu'un aura péché contre son prochain, et qu'on lui aura déféré le serment pour le faire jurer, et que le serment aura été fait devant ton autel dans cette maison;
32 sai ka ji daga sama, ka kuma yi wani abu. Ka shari’anta tsakanin bayinka, ka hukunta mai laifi, ka mai da laifinsa a kansa, mai gaskiya kuma ka nuna shi marar laifi ne bisa ga gaskiyarsa.
Exauce[-les] toi des cieux, et exécute [ce que portera l'exécration du serment], et juge tes serviteurs en condamnant le méchant, [et] lui rendant selon ce qu'il aura fait; et en justifiant le juste, et lui rendant selon sa justice.
33 “Sa’ad da abokan gāba suka ci mutanenka Isra’ila a yaƙi saboda sun yi maka zunubi, sa’ad da kuma suka dawo gare ka don su furta sunanka, suna addu’a suna roƙo gare ka a wannan haikali,
Quand ton peuple d'Israël aura été battu par l'ennemi, à cause qu'ils auront péché contre toi, si ensuite ils se retournent vers toi, en réclamant ton nom, et en te faisant des prières et des supplications dans cette maison;
34 ka ji daga sama, ka gafarta zunubin mutanenka, ka kuma dawo da su ƙasar da ka ba wa kakanninsu.
Exauce[-les], toi, des cieux, et pardonne le péché de ton peuple d'Israël, et ramène-les dans la terre que tu as donnée à leurs pères.
35 “Sa’ad da sammai sun kulle, babu kuma ruwan sama domin mutane sun yi maka zunubi, sa’ad da suka yi addu’a suna fuskantar wannan wuri, suka kuma furta sunanka, suka juye daga zunubinsu domin ka hore su,
Quand les cieux seront resserrés, et qu'il n'y aura point de pluie, à cause que [ceux d'Israël] auront péché contre toi, s'ils te font prière en ce lieu-ci, et s'ils réclament ton Nom, et s'ils se détournent de leurs péchés, parce que tu les auras affligés;
36 ka ji daga sama, ka kuma gafarta zunubin bayinka, mutanenka Isra’ila. Ka koya musu hanyar da ta dace ta rayuwa, ka kuma aika da ruwan sama a ƙasar da ka ba wa mutanenka gādo.
Exauce[-les], toi, des cieux, et pardonne le péché de tes serviteurs, et de ton peuple d'Israël, lorsque tu leur auras enseigné le bon chemin, par lequel ils doivent marcher, et envoie-leur la pluie sur la terre que tu as donnée à ton peuple pour héritage.
37 “Sa’ad da yunwa ko annoba ta fāɗo a ƙasar, ko burtuntuna, ko fumfuna, ko fāri, ko tsutsa, ko kuwa abokan gāba sun yi musu kwanto, a wani daga cikin biranensu, duk wata cuta, ko ciwon da ya zo,
Quand il y aura famine au pays, ou la mortalité; quand il y aura brûlure, nielle, sauterelles, et vermisseaux, même quand les ennemis les assiégeront jusques dans leur propre pays, [ou qu'il y aura plaie, ou] maladie;
38 in suka yi addu’a ko roƙo ta wurin wani daga cikin mutanenka Isra’ila, kowa ya san wahalar zuciyarsa, ya kuma buɗe hannuwansa yana fuskantar wannan haikali,
Quelque prière, et quelque supplication que te fasse quelque homme que ce soit de tout ton peuple d'Israël, selon qu'ils auront connu chacun la plaie de son cœur; et que chacun aura étendu ses mains vers cette maison;
39 sai ka ji daga sama, mazauninka. Ka gafarta, ka kuma yi wani abu. Ka yi da kowane mutum bisa ga dukan abin da ya yi, tun da yake ka san zuciyarsa (gama kai kaɗai ka san zukatan dukan mutane),
Alors exauce[-les], toi, des cieux, du domicile arrêté de ta demeure, et pardonne, et fais, et rends à chacun selon toutes ses voies, parce que tu auras connu son cœur; car tu connais toi-seul le cœur de tous les hommes;
40 saboda su ji tsoronka a kowane lokacin da suke zaune a ƙasar da ka ba wa kakanninmu.
Afin qu'ils te craignent tout le temps qu'ils vivront sur la terre que tu as donnée à nos pères.
41 “Game da baƙo kuwa wanda shi ba na mutanenka Isra’ila ba, amma ya zo daga ƙasa mai nisa saboda sunanka,
Et même lorsque l'étranger qui ne sera pas de ton peuple d'Israël, mais qui sera venu d'un pays éloigné pour l'amour de ton Nom;
42 gama mutane za su ji game da girman sunanka, da ƙarfin hannunka, da kuma hannunka mai iko, sa’ad da ya zo, ya yi addu’a yana fuskantar wannan haikali,
(Car on entendra parler de ton Nom, qui est grand, et de ta main forte, et de ton bras étendu; ) lors donc qu'il sera venu, et qu'il te priera dans cette maison;
43 ka ji daga sama, mazauninka, ka kuma yi dukan abin da baƙon ya tambaye ka, saboda dukan mutanen duniya su san sunanka, su kuma ji tsoronka, kamar yadda mutanenka Isra’ila suke yi, bari kuma su san cewa wannan gidan da na gina, ya amsa Sunanka.
Exauce[-le], toi, des cieux, du domicile arrêté de ta demeure, et fais selon tout ce pour quoi cet étranger aura crié vers toi; afin que tous les peuples de la terre connaissent ton Nom pour te craindre, comme ton peuple d'Israël; et pour connaître que ton Nom est réclamé sur cette maison que j'ai bâtie.
44 “Sa’ad da mutanenka suka tafi yaƙi da abokan gābansu, a duk inda ka aike su, sa’ad da kuma suka yi addu’a ga Ubangiji suna fuskantar birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka,
Quand ton peuple sera sorti en guerre contre son ennemi, dans le chemin par lequel tu l'auras envoyé, s'ils font prière à l'Eternel en regardant vers cette ville que tu as choisie, et vers cette maison que j'ai bâtie à ton Nom;
45 ka ji addu’arsu da roƙonsu daga sama, ka kuma biya musu bukatansu.
Alors exauce des cieux leur prière et leur supplication, et maintiens leur droit.
46 “Sa’ad da suka yi maka zunubi, gama babu wanda ba ya zunubi, ka kuwa yi fushi da su, ka kuma ba da su ga abokin gāba, wanda ya kwashe su kamammu zuwa ƙasarsa, nesa ko kusa;
Quand ils auront péché contre toi, car il n'y a point d'homme qui ne pèche, et que tu seras irrité contr'eux, tellement que tu les auras livrés entre les [mains] de leurs ennemis, et que ceux qui les auront pris les auront menés captifs en pays ennemi, soit loin, soit près;
47 in suka canja zuciyarsu a ƙasar da aka riƙe su kamammu, suka tuba, suka kuma roƙe ka a ƙasar waɗanda suka ci su da yaƙi, suka ce, ‘Mun yi zunubi, mun yi abin da ba daidai ba, mun yi mugunta’;
Si au pays où ils auront été menés captifs, ils reviennent à eux-mêmes, et se repentant ils te prient au pays de ceux qui les auront emmenés captifs, en disant: Nous avons péché, nous avons fait iniquité, et nous avons fait méchamment;
48 in sun juye gare ka da dukan zuciyarsu, da dukan ransu a ƙasar abokan gābansu waɗanda suka kwashe kamammu, suka yi addu’a gare ka, suka fuskanci wajen ƙasar da ka ba wa kakanninsu, waje birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka;
S'ils retournent donc à toi de tout leur cœur et de toute leur âme, dans le pays de leurs ennemis, qui les auront emmenés captifs, et s'ils t'adressent leurs prières, en regardant vers leur pays que tu as donné à leurs pères, vers cette ville que tu as choisie, et vers cette maison que j'ai bâtie à ton Nom;
49 sai ka ji daga sama, mazauninka, ka ji addu’a da roƙonsu, ka kuma biya musu bukatansu.
Alors exauce des cieux, du domicile arrêté de ta demeure, leur prière, et leur supplication, et maintiens leur droit.
50 Ka gafarta wa mutanenka, waɗanda suka yi maka zunubi; ka gafarta dukan laifofin da suka yi maka, ka kuma sa waɗanda suka ci su a yaƙi su ji tausayinsu.
Et pardonne à ton peuple qui aura péché contre toi, et même [pardonne-leur] tous les crimes qu'ils auront commis contre toi, et fais que ceux qui les auront emmenés captifs aient pitié d'eux, et leur fassent grâce.
51 Gama su mutanenka ne, abin gādonka, waɗanda ka fitar daga Masar, daga tanderu mai narken ƙarfe.
Car ils sont ton peuple et ton héritage, que tu as tiré hors d'Egypte, du milieu d'un fourneau de fer.
52 “Bari idanunka su buɗe ga roƙon bawanka, ga roƙon mutanenka Isra’ila, bari kuma ka saurare su sa’ad da suka yi kuka gare ka.
Que tes yeux donc soient ouverts sur la prière de ton serviteur, et sur la supplication de ton peuple d'Israël, pour les exaucer dans tout ce pourquoi ils crieront à toi.
53 Gama ka ware su daga dukan al’umman duniya su zama abin gādonka, kamar yadda aka furta ta wurin bawanka Musa sa’ad da kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka ka fitar da kakanninmu daga Masar.”
Car tu les as mis à part pour toi d'entre tous les peuples de la terre, afin qu'ils fussent ton héritage, comme tu en as parlé par le moyen de Moïse ton serviteur, quand tu retiras nos pères hors d'Egypte, ô Seigneur Eternel!
54 Da Solomon ya gama dukan waɗannan addu’o’i da roƙe-roƙe ga Ubangiji, sai ya tashi daga gaban bagaden Ubangiji, inda ya durƙusa da hannuwansa a buɗe waje sama.
Or aussitôt que Salomon eut achevé de faire toute cette prière, et cette supplication à l'Eternel, il se leva de devant l'autel de l'Eternel, et n'étant plus à genoux, mais ayant [encore] les mains étendues vers les cieux;
55 Ya tashi ya kuma albarkaci dukan taron Isra’ila da babbar murya, yana cewa,
Il se tint debout, et bénit toute l'assemblée d'Israël à haute voix, en disant:
56 “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda ya ba wa mutanensa hutu kamar dai yadda ya yi alkawari. Babu magana guda da ta kāsa cika cikin dukan alkawaransa masu kyau da ya yi ta wurin bawansa Musa.
Béni soit l'Eternel, qui a donné du repos à son peuple d'Israël, comme il en avait parlé; il n'est pas tombé [à terre] un seul mot de toutes les bonnes paroles qu'il avait prononcées par le moyen de Moïse son serviteur.
57 Bari Ubangiji Allah yă kasance tare da mu kamar yadda ya kasance da kakanninmu; kada yă taɓa rabu da mu, ko yă yashe mu.
Que l'Eternel notre Dieu soit avec nous, comme il a été avec nos pères; qu'il ne nous abandonne point, et qu'il ne nous délaisse point.
58 Bari yă juye zukatanmu gare shi, don mu yi tafiya a cikin dukan hanyoyinsa, mu kuma kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa, da kuma farillan da ya ba wa kakanninmu.
[Mais] qu'il incline notre cœur vers lui, afin que nous marchions en toutes ses voies, et que nous gardions ses commandements, ses statuts, et ses ordonnances qu'il a prescrites à nos pères;
59 Bari kuma waɗannan kalmomina, waɗanda na yi addu’a a gaban Ubangiji, su yi kusa da Ubangiji Allahnmu, dare da rana, don yă biya bukatan bawansa da na mutanensa Isra’ila, bisa ga bukatan kowa,
Et que mes paroles, par lesquelles j'ai fait supplication à l'Eternel, soient présentes devant l'Eternel notre Dieu jour et nuit; afin qu'il maintienne le droit de son serviteur, et le droit de son peuple d'Israël, selon qu'il en aura besoin chaque jour.
60 saboda dukan mutanen duniya su san cewa Ubangiji, shi ne Allah, babu kuma wani.
Afin que tous les peuples de la terre connaissent que c'est l'Eternel qui est Dieu, [et] qu'il n'y en a point d'autre;
61 Amma dole ku miƙa zukatanku ga Ubangiji Allahnmu, don ku rayu, ta wurin bin ƙa’idodinsa, ku kuma yi biyayya da umarnansa, kamar yadda kuke yi a wannan lokaci.”
Et afin que votre cœur soit pur envers l'Eternel votre Dieu, pour marcher dans ses statuts, et pour garder ses commandements, comme aujourd'hui.
62 Sai sarki da dukan Isra’ila, suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
Et le Roi, et tout Israël avec lui, sacrifièrent des sacrifices devant l'Eternel.
63 Solomon ya miƙa hadaya ta salama ga Ubangiji, shanu dubu ashirin da biyu, tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan Isra’ilawa suka keɓe haikalin Ubangiji.
Et Salomon offrit un sacrifice de prospérités, qu'il sacrifia à l'Eternel, [savoir], vingt et deux mille bœufs, et six vingt mille brebis. Ainsi le Roi et tous les enfants d'Israël dédièrent la maison de l'Eternel.
64 A wannan rana sarki ya tsarkake sashe na tsakiyar fili a gaban haikalin Ubangiji, a can kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa, hadaya ta gari, da kitsen hadaya ta salama, gama bagaden tagulla a gaban Ubangiji ya yi ƙanƙanta sosai da za a miƙa hadayun ƙonawa, hadayun hatsi, da kuma kitsen hadayun salama.
En ce jour-là le Roi consacra le milieu du parvis, qui était devant la maison de l'Eternel; car il offrit là les holocaustes, et les gâteaux, et les graisses des sacrifices de prospérités, parce que l'autel d'airain qui était devant l'Eternel, était trop petit pour contenir les holocaustes, et les gâteaux, et les graisses des sacrifices de prospérités.
65 Ta haka Solomon da dukan Isra’ila, wato, babban taro, suka yi bikin a lokacin. Mutane suka zo, tun daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar. Suka yi biki a gaban Ubangiji Allahnmu, kwana bakwai. Suka kuma ƙara kwana bakwai, kwanaki goma sha huɗu gaba ɗaya.
Et en ce temps-là Salomon célébra une fête solennelle; et avec lui tout Israël qui était une grande assemblée, [venue] depuis où l'on entre en Hamath jusqu'au torrent d'Egypte, devant l'Eternel notre Dieu, et cela dura sept jours, et sept autres jours, ce qui fut quatorze jours.
66 A rana ta biye sai ya sallame mutane. Suka sa wa sarki albarka, sa’an nan suka watse zuwa gida, da farin ciki, da murna a zukatansu saboda kyawawan abubuwan da Ubangiji ya yi domin bawansa Dawuda, da kuma mutanensa Isra’ila.
[Et] au huitième jour il renvoya le peuple, qui bénit le Roi; puis ils s'en allèrent dans leurs tentes, en se réjouissant, et ayant le cœur plein de joie à cause de tout le bien que l'Eternel avait fait à David son serviteur, et à Israël son peuple.

< 1 Sarakuna 8 >