< 1 Sarakuna 8 >

1 Sai Sarki Solomon ya tattara dattawan Urushalima a gabansa, da dukan shugabannin kabilu, da shugabannin iyalan Isra’ilawa, domin su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Sihiyona, Birnin Dawuda.
Then, did Solomon call together the elders of Israel, and all the heads of the tribes, chiefs of the fathers of the sons of Israel, unto King Solomon in Jerusalem, —that they might bring up the ark of the covenant of Yahweh, out of the city of David, the same is Zion.
2 Dukan mutanen Isra’ila suka tattaru a gaban Sarki Solomon a lokacin biki, a watan Etanim, wato, wata na bakwai.
So all the men of Israel came together unto King Solomon, in the month of steady flowings, at the festival, —the same is the seventh month.
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka iso, sai firistoci suka ɗauki akwatin alkawarin,
And all the elders of Israel came in, —and the priests took up the ark;
4 suka haura da akwatin alkawarin Ubangiji da kuma Tentin Sujada, da dukan kayayyaki masu tsarkin da suke cikinsa. Firistoci da Lawiyawa suka ɗauko su,
and they brought up the ark of Yahweh, and the Tent of Meeting, and all the hallowed vessels that were in the tent, —yea, the priests and the Levites, did bring them up.
5 sai Sarki Solomon da dukan taron Isra’ila da suka tattaru kewaye da shi a gaban akwatin alkawari, suka yi ta miƙa hadayar tumaki da bijimai masu yawa da ba a iya lissaftawa, ko ƙirgawa.
And, King Solomon, and all the assembly of Israel who had assembled themselves unto him, were with him, before the ark, —sacrificing sheep and oxen, which could neither be recorded nor counted, for multitude.
6 Sa’an nan firistoci suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji inda aka shirya masa, can ciki cikin haikali, a Wuri Mafi Tsarki, aka kuma sa shi a ƙarƙashin fikafikan kerubobin.
So the priests brought in the ark of the covenant of Yahweh into its place, into the shrine of the house, into the holy of holies, —under the wings of the cherubim.
7 Kerubobin sun buɗe fikafikansu a bisa wurin da akwatin alkawarin yake, suka inuwartar da akwatin alkawarin da sandunan ɗaukansa.
For, the cherubim, were spreading forth their two wings, over the place of the ark, —and the cherubim made a covering over the ark and over the staves thereof, above.
8 Waɗannan sandunan sun yi tsawo har ana iya ganin bakinsu daga Wuri Mai Tsarki a gaban wuri mai tsarki na can ciki, amma ba a iya ganinsu daga waje na Wuri Mai Tsarki ba. Suna nan kuwa a can har wa yau.
And they drew out the staves, and the heads of the staves were seen from the holy place, in front of the shrine, although they were not seen on the outside, —and they have remained there until this day.
9 Ba kome a cikin akwatin alkawarin, sai dai alluna na dutse guda biyu waɗanda Musa ya ajiye a ciki tun a Horeb, inda Ubangiji ya yi alkawari da Isra’ilawa bayan sun fito Masar.
There was nothing in the ark, save the two tables of stone, which Moses deposited there in Horeb, —the tables of the covenant which Yahweh solemnised with the sons of Israel, when they came forth out of the land of Egypt.
10 Sa’ad da firistoci suka janye daga Wuri Mai Tsarki, sai girgije ya cika haikalin Ubangiji.
And so it was, when the priests came forth out of the holy place, that, a cloud, filled the house of Yahweh;
11 Firistocin kuwa ba su iya yin hidimarsu ba saboda girgijen, gama ɗaukakar Ubangiji ta cika haikalinsa.
so that the priests could not stand to minister, because of the cloud, —for, the glory of Yahweh, filled, the house of Yahweh.
12 Sai Solomon ya ce, “Ubangiji ya ce zai zauna a gizagizai masu duhu;
Then, said Solomon, —Yahweh, said, that he would make his habitation in thick gloom:
13 ga shi na gina haikali mai daraja dominka, inda za ka zauna har abada.”
I have, built, a house as a high abode for thee, —A settled place for thee to abide in, for ages.
14 Yayinda dukan taron Isra’ila suke tsattsaye a can, sai sarki ya juya ya albarkace su.
And the king turned about his face, and blessed all the convocation of Israel, —while all the convocation of Israel was standing;
15 Sa’an nan ya ce, “Ku yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda da hannunsa ya cika abin da ya yi alkawari da bakinsa ga mahaifina Dawuda. Gama ya ce,
and he said—Blessed, be Yahweh, God of Israel, who spake with his mouth, unto David my father, —that which with his hand he hath fulfilled, saying: —
16 ‘Tun ran da na fitar da mutanena Isra’ila daga Masar, ban zaɓi wani birni a cikin wata kabilar Isra’ila a gina haikali domin Sunana yă kasance a can ba, amma na zaɓi Dawuda yă yi mulkin mutanena Isra’ila.’
Since the day that I brought forth my people Israel, out of Egypt, I had chosen no city, out of all the tribes of Israel, for building a house, where my Name might be, —but I have chosen Jerusalem, that my Name should be there, and I have chosen David, to be over my people Israel:
17 “Mahaifina Dawuda ya yi niyya a cikin zuciyarsa yă gina haikali saboda Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
And so it came to pass, that it was near the heart of David my father, —to build a house for the Name of Yahweh, God of Israel.
18 Amma Ubangiji ya ce wa mahaifina Dawuda, ‘Saboda yana a zuciyarka ka gina haikali domin Sunana, ka yi daidai da ka yi niyyar wannan a zuciyarka.
Then said Yahweh unto David my father, Because it was near thy heart to build a house for my Name, thou didst well that it was near thy heart;
19 Duk da haka, ba kai ba ne za ka gina haikali, amma ɗanka, wanda yake namanka da jininka, shi ne wanda zai gina haikali domin Sunana.’
Only, thou thyself, must not build the house, —but, thine own son who hath proceeded out of thy loins, he, shall build the house, for my Name.
20 “Ubangiji ya kiyaye alkawarin da ya yi. Na gāje Dawuda mahaifina, yanzu kuma ga shi na zauna a kujerar sarautar Isra’ila, kamar dai yadda Ubangiji ya yi alkawari, na kuma gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
So then Yahweh hath established his word which he spake, —and I have been raised up in the room of David my father, and have taken my seat upon the throne of Israel, as spake Yahweh, and have built the house for the Name of Yahweh, God of Israel;
21 Na tanada wuri saboda akwatin alkawari, akwatin da ya ƙunshi alkawarin da Ubangiji ya yi da kakanninmu sa’ad da ya fitar da su daga Masar.”
and have appointed there a place for the ark, wherein is the covenant of Yahweh, —which he solemnised with our fathers, when he brought them forth out of the land of Egypt.
22 Sai Solomon ya tsaya a gaban bagaden Ubangiji, a gaban dukan taron Isra’ila, ya ɗaga hannuwansa sama,
And Solomon stood before the altar of Yahweh, in the presence of all the convocation of Israel, —and spread forth his hands towards the heavens;
23 ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, babu Allah kamar ka a sama can bisa, ko a ƙasa can ƙarƙashi, kai da kake kiyaye alkawarinka na ƙauna ga bayinka waɗanda suke cin gaba a hanyarka da dukan zuciyarsu.
and said—O Yahweh, God of Israel! Not like thee, is there a God, in the heavens above, or upon the earth beneath, —keeping Covenant and Lovingkindness for thy servants who are walking before thee, with all their heart;
24 Ka kiyaye alkawarinka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina. Da bakinka ka yi alkawari, da hannunka kuma ka cika shi, yadda yake a yau.
who hast kept for thy servant David my father, that which thou didst promise him, —in that thou didst promise with thy mouth, and, with thy hand, hast fulfilled, as it is this day.
25 “Yanzu, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bari ka cika wa bawanka Dawuda mahaifina alkawaran da ka yi masa sa’ad da ka ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani da zai zauna a gabana a kan kujerar sarautar Isra’ila ba, in kawai’ya’yanka maza sun yi hankali cikin dukan abubuwan da suke yi, don su yi tafiya a gabana kamar yadda ka yi.’
Now, therefore, O Yahweh, God of Israel, keep thou for thy servant David my father, that which thou didst promise him, saying, There shall not be cut off to thee a man from before me, to sit upon the throne of Israel, —if only, thy sons take heed to their way, by walking before me, as thou hast walked before me.
26 Yanzu fa, ya Allah na Isra’ila, bari maganarka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina tă cika.
Now, therefore, O God of Israel, —verified be thy word, I pray thee, which thou didst speak to thy servant, David my father.
27 “Amma anya, Allah, za ka zauna a duniya? Sammai, har ma da saman sammai ba za tă iya riƙe ka ba, balle wannan haikalin da na gina!
But, in very deed, will God dwell, upon the earth? Lo! the heaven, yea the heaven of heavens, cannot contain thee, how much less this house which I have built?
28 Duk da haka ka ji addu’ar bawanka da kuma roƙonsa don jinƙai, ya Ubangiji Allahna. Ka ji kuka da addu’ar da bawanka yake yi a gabanka a wannan rana.
Yet wilt thou turn unto the prayer of thy servant, and unto his supplication, O Yahweh my God, —to hearken unto the cry, and unto the prayer, wherewith thy servant doth pray before thee to-day;
29 Bari idanunka su buɗe, su fuskanci wannan haikali dare da rana, wannan wurin da ka ce, ‘Sunana zai kasance a can,’ saboda ka ji addu’ar bawanka in yana fuskantar wannan wuri.
that thine eye may be opened toward this house, night and day, toward the place of which thou hast said, My Name shall be, there; hearkening unto the prayer which thy servant shall offer toward this place.
30 Ka ji roƙon bawanka da kuma na mutanenka Isra’ila sa’ad da suka yi addu’a, suka fuskanci wannan wuri. Ka ji daga sama, mazauninka, kuma sa’ad da ka ji, ka gafarta.
Wilt, thou, therefore, hearken unto the supplication of thy servant, and of thy people Israel, whensoever they shall pray toward this place, —yea wilt, thou thyself, hear, in thine own dwelling-place, in the heavens, and, when thou hearest, then wilt thou forgive?
31 “Sa’ad da mutum ya yi abin da ba daidai ba ga maƙwabcinsa, an kuma bukace shi yă yi rantsuwa, sai ya zo ya rantse a gaban bagade a cikin haikalin nan,
When a man shall sin against his neighbour, and there shall be taken up against him an oath, to put him on oath, —and he shall come in and swear before thine altar, in this house,
32 sai ka ji daga sama, ka kuma yi wani abu. Ka shari’anta tsakanin bayinka, ka hukunta mai laifi, ka mai da laifinsa a kansa, mai gaskiya kuma ka nuna shi marar laifi ne bisa ga gaskiyarsa.
then wilt, thou thyself, hear in the heavens, and act, and judge thy servants, condemning the lawless, by setting his way upon his own head, —and justifying the righteous, by giving to him, according to his righteousness?
33 “Sa’ad da abokan gāba suka ci mutanenka Isra’ila a yaƙi saboda sun yi maka zunubi, sa’ad da kuma suka dawo gare ka don su furta sunanka, suna addu’a suna roƙo gare ka a wannan haikali,
When thy people Israel are smitten before an enemy, because they have been sinning against thee, —and they turn again unto thee, and confess thy Name, and pray and make supplication unto thee, in this house,
34 ka ji daga sama, ka gafarta zunubin mutanenka, ka kuma dawo da su ƙasar da ka ba wa kakanninsu.
then wilt, thou thyself, hear in the heavens, and forgive the sin of thy people Israel, and bring them back unto the soil, which thou gavest unto their fathers?
35 “Sa’ad da sammai sun kulle, babu kuma ruwan sama domin mutane sun yi maka zunubi, sa’ad da suka yi addu’a suna fuskantar wannan wuri, suka kuma furta sunanka, suka juye daga zunubinsu domin ka hore su,
When the heavens are shut up, and there is no rain, because they have been sinning against thee, —and they shall pray toward this place, and confess thy Name, and, from their sin, shall return, because thou hast been afflicting them,
36 ka ji daga sama, ka kuma gafarta zunubin bayinka, mutanenka Isra’ila. Ka koya musu hanyar da ta dace ta rayuwa, ka kuma aika da ruwan sama a ƙasar da ka ba wa mutanenka gādo.
then wilt, thou thyself, hear in the heavens and forgive the sin of thy servants, and of thy people Israel, that thou mayest teach them the good way, wherein they should walk, —and give rain upon thy land, which thou hast given unto thy people, for an inheritance?
37 “Sa’ad da yunwa ko annoba ta fāɗo a ƙasar, ko burtuntuna, ko fumfuna, ko fāri, ko tsutsa, ko kuwa abokan gāba sun yi musu kwanto, a wani daga cikin biranensu, duk wata cuta, ko ciwon da ya zo,
When there shall be, famine, in the land, when there shall be, pestilence, when there shall be, blasting, mildew locust, caterpillar, when their enemy shall besiege them in one of their own gates, —whatsoever plague, whatsoever sickness;
38 in suka yi addu’a ko roƙo ta wurin wani daga cikin mutanenka Isra’ila, kowa ya san wahalar zuciyarsa, ya kuma buɗe hannuwansa yana fuskantar wannan haikali,
any prayer, any supplication which, any son of earth, may have, of all thy people Israel, —who will certainly know every man the plague of his own heart, and so he shall spread abroad his hands towards this house,
39 sai ka ji daga sama, mazauninka. Ka gafarta, ka kuma yi wani abu. Ka yi da kowane mutum bisa ga dukan abin da ya yi, tun da yake ka san zuciyarsa (gama kai kaɗai ka san zukatan dukan mutane),
then wilt, thou thyself, hear in the heavens, in the settled place of thine abode, and forgive and act, and give unto every man according to all his ways, whose heart thou wilt know, —for, thou thyself alone, knowest the heart of all the sons of men;
40 saboda su ji tsoronka a kowane lokacin da suke zaune a ƙasar da ka ba wa kakanninmu.
to the end they may revere thee, all the days which they do live, upon the face of the soil, —which thou gavest unto our fathers?
41 “Game da baƙo kuwa wanda shi ba na mutanenka Isra’ila ba, amma ya zo daga ƙasa mai nisa saboda sunanka,
Moreover also, unto the stranger, who is, not of thy people Israel, —but hath come in out of a far country, for the sake of thy Name, —
42 gama mutane za su ji game da girman sunanka, da ƙarfin hannunka, da kuma hannunka mai iko, sa’ad da ya zo, ya yi addu’a yana fuskantar wannan haikali,
(for they will certainly hear of thy great Name, and of thy strong hand, and of thy stretched-out arm, —and so will come in and pray towards this house),
43 ka ji daga sama, mazauninka, ka kuma yi dukan abin da baƙon ya tambaye ka, saboda dukan mutanen duniya su san sunanka, su kuma ji tsoronka, kamar yadda mutanenka Isra’ila suke yi, bari kuma su san cewa wannan gidan da na gina, ya amsa Sunanka.
wilt, thou thyself, hear in the heavens, the settled place of thine abode, and act, according to all for which, the stranger, shall cry unto thee, —to the end that all the peoples of the earth may truly know thy Name, so as to revere thee, like thy people Israel, and to know that, thine own Name, hath been given unto this house, which I have built?
44 “Sa’ad da mutanenka suka tafi yaƙi da abokan gābansu, a duk inda ka aike su, sa’ad da kuma suka yi addu’a ga Ubangiji suna fuskantar birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka,
When thy people go forth to war against their enemy, whithersoever thou mayest send them, —and shall pray unto Yahweh, in the direction of the city which thou hast chosen, and the house which I have built for thy Name,
45 ka ji addu’arsu da roƙonsu daga sama, ka kuma biya musu bukatansu.
then wilt thou hear, in the heavens, their prayer and their supplication, —and maintain their cause?
46 “Sa’ad da suka yi maka zunubi, gama babu wanda ba ya zunubi, ka kuwa yi fushi da su, ka kuma ba da su ga abokin gāba, wanda ya kwashe su kamammu zuwa ƙasarsa, nesa ko kusa;
When they sin against thee—for there is, no son of earth, that sinneth not, and thou shalt be angry with them, and deliver them up before an enemy, —who shall carry them away as their captives, into the land of the enemy, far or near;
47 in suka canja zuciyarsu a ƙasar da aka riƙe su kamammu, suka tuba, suka kuma roƙe ka a ƙasar waɗanda suka ci su da yaƙi, suka ce, ‘Mun yi zunubi, mun yi abin da ba daidai ba, mun yi mugunta’;
and they come back to their right mind, in the land whither they have been taken captive, —and so turn and make supplication unto thee, in the land of their captors, saying, We have sinned and done perversely, we have been lawless;
48 in sun juye gare ka da dukan zuciyarsu, da dukan ransu a ƙasar abokan gābansu waɗanda suka kwashe kamammu, suka yi addu’a gare ka, suka fuskanci wajen ƙasar da ka ba wa kakanninsu, waje birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka;
and so they turn unto thee with all their heart, and with all their soul, in the land of their enemies, who have carried them away captive, —and pray unto thee in the direction of their own land, which thou gavest unto their fathers, the city which thou hast chosen, and the house which I have built for thy Name,
49 sai ka ji daga sama, mazauninka, ka ji addu’a da roƙonsu, ka kuma biya musu bukatansu.
then wilt thou hearken in the heavens, the settled place of thine abode, unto their prayer, and unto their supplication, —and maintain their cause;
50 Ka gafarta wa mutanenka, waɗanda suka yi maka zunubi; ka gafarta dukan laifofin da suka yi maka, ka kuma sa waɗanda suka ci su a yaƙi su ji tausayinsu.
and grant forgiveness to thy people, who have sinned against thee, even as to all their transgressions wherein they have transgressed against thee, —and grant them compassion before their captors, so that they may have compassion upon them;
51 Gama su mutanenka ne, abin gādonka, waɗanda ka fitar daga Masar, daga tanderu mai narken ƙarfe.
because, thy people and thine inheritance, they are, —whom thou didst bring forth out of Egypt, out of the midst of the smelting-pot of iron;
52 “Bari idanunka su buɗe ga roƙon bawanka, ga roƙon mutanenka Isra’ila, bari kuma ka saurare su sa’ad da suka yi kuka gare ka.
that thine eyes may be open unto the supplication of thy servant, and unto the supplication of thy people Israel, —to hearken unto them, in all their crying unto thee;
53 Gama ka ware su daga dukan al’umman duniya su zama abin gādonka, kamar yadda aka furta ta wurin bawanka Musa sa’ad da kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka ka fitar da kakanninmu daga Masar.”
because, thou thyself, didst separate them unto thee, for an inheritance, out of all the peoples of the earth, —as thou spakest by the hand of Moses thy servant, when thou broughtest forth our fathers out of Egypt, O Lord Yahweh.
54 Da Solomon ya gama dukan waɗannan addu’o’i da roƙe-roƙe ga Ubangiji, sai ya tashi daga gaban bagaden Ubangiji, inda ya durƙusa da hannuwansa a buɗe waje sama.
And it came to pass, when Solomon had made an end of praying unto Yahweh all this prayer and supplication, that he arose from before the altar of Yahweh, from kneeling on his knees, with his hands outspread to the heavens;
55 Ya tashi ya kuma albarkaci dukan taron Isra’ila da babbar murya, yana cewa,
and stood and blessed all the convocation of Israel, —with a loud voice, saying:
56 “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda ya ba wa mutanensa hutu kamar dai yadda ya yi alkawari. Babu magana guda da ta kāsa cika cikin dukan alkawaransa masu kyau da ya yi ta wurin bawansa Musa.
Blessed, be Yahweh, who hath given rest unto his people Israel, according to all that he promised, —there hath not failed one word of all his good promise, which he promised by the hand of Moses his servant.
57 Bari Ubangiji Allah yă kasance tare da mu kamar yadda ya kasance da kakanninmu; kada yă taɓa rabu da mu, ko yă yashe mu.
Yahweh our God be with us, as he was with our fathers, —let him not leave us, nor forsake us;
58 Bari yă juye zukatanmu gare shi, don mu yi tafiya a cikin dukan hanyoyinsa, mu kuma kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa, da kuma farillan da ya ba wa kakanninmu.
but bow our heart unto himself, —to walk in all his ways, and to keep his commandments, and his statutes, and his regulations, which he commanded our fathers.
59 Bari kuma waɗannan kalmomina, waɗanda na yi addu’a a gaban Ubangiji, su yi kusa da Ubangiji Allahnmu, dare da rana, don yă biya bukatan bawansa da na mutanensa Isra’ila, bisa ga bukatan kowa,
And let these my words, wherewith I have made supplication before Yahweh, be near unto Yahweh our God, day and night, —that he may maintain the cause of his servant, and the cause of his people Israel, as any need ariseth:
60 saboda dukan mutanen duniya su san cewa Ubangiji, shi ne Allah, babu kuma wani.
To the end that all the peoples of the earth may know, that, Yahweh, is God, —there is none else.
61 Amma dole ku miƙa zukatanku ga Ubangiji Allahnmu, don ku rayu, ta wurin bin ƙa’idodinsa, ku kuma yi biyayya da umarnansa, kamar yadda kuke yi a wannan lokaci.”
So shall your heart be sound with Yahweh our God, —to walk in his statutes, and to keep his commandments, as at this day.
62 Sai sarki da dukan Isra’ila, suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
And, the king, and all Israel with him, were offering sacrifice before Yahweh.
63 Solomon ya miƙa hadaya ta salama ga Ubangiji, shanu dubu ashirin da biyu, tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan Isra’ilawa suka keɓe haikalin Ubangiji.
So Solomon offered as a sacrifice of peace-offerings, which he offered unto Yahweh—Oxen, two and twenty thousand, and Sheep, a hundred and twenty thousand, —Thus did, the king and all the sons of Israel, dedicate the house of Yahweh.
64 A wannan rana sarki ya tsarkake sashe na tsakiyar fili a gaban haikalin Ubangiji, a can kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa, hadaya ta gari, da kitsen hadaya ta salama, gama bagaden tagulla a gaban Ubangiji ya yi ƙanƙanta sosai da za a miƙa hadayun ƙonawa, hadayun hatsi, da kuma kitsen hadayun salama.
On that day, did the king hallow the middle of the court, that was before the house of Yahweh, —for he offered there the ascending-sacrifice, and the meal-offering, and the fat portions of the peace-offerings, because, the altar of bronze that was before Yahweh, was too small to receive the ascending-sacrifice and the meal-offering, and the fat portions of the peace-offerings.
65 Ta haka Solomon da dukan Isra’ila, wato, babban taro, suka yi bikin a lokacin. Mutane suka zo, tun daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar. Suka yi biki a gaban Ubangiji Allahnmu, kwana bakwai. Suka kuma ƙara kwana bakwai, kwanaki goma sha huɗu gaba ɗaya.
And Solomon made, at that time, a festival—and all Israel with him—a great convocation, from the entering in of Hamath unto the ravine of Egypt, before Yahweh our God, seven days, and seven days, —fourteen days.
66 A rana ta biye sai ya sallame mutane. Suka sa wa sarki albarka, sa’an nan suka watse zuwa gida, da farin ciki, da murna a zukatansu saboda kyawawan abubuwan da Ubangiji ya yi domin bawansa Dawuda, da kuma mutanensa Isra’ila.
And on the eighth day, he sent the people away, and they blessed the king, —and departed to their homes, rejoicing and glad of heart, over all the goodness which Yahweh had done for David his servant, and for Israel his people.

< 1 Sarakuna 8 >