< 1 Sarakuna 8 >

1 Sai Sarki Solomon ya tattara dattawan Urushalima a gabansa, da dukan shugabannin kabilu, da shugabannin iyalan Isra’ilawa, domin su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Sihiyona, Birnin Dawuda.
Then Solomon assembled the elders of Israel, and all the heads of the tribes, the princes of the fathers’ [houses] of the children of Israel, unto king Solomon in Jerusalem, to bring up the ark of the covenant of Jehovah out of the city of David, which is Zion.
2 Dukan mutanen Isra’ila suka tattaru a gaban Sarki Solomon a lokacin biki, a watan Etanim, wato, wata na bakwai.
And all the men of Israel assembled themselves unto king Solomon at the feast, in the month Ethanim, which is the seventh month.
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka iso, sai firistoci suka ɗauki akwatin alkawarin,
And all the elders of Israel came, and the priests took up the ark.
4 suka haura da akwatin alkawarin Ubangiji da kuma Tentin Sujada, da dukan kayayyaki masu tsarkin da suke cikinsa. Firistoci da Lawiyawa suka ɗauko su,
And they brought up the ark of Jehovah, and the tent of meeting, and all the holy vessels that were in the Tent; even these did the priests and the Levites bring up.
5 sai Sarki Solomon da dukan taron Isra’ila da suka tattaru kewaye da shi a gaban akwatin alkawari, suka yi ta miƙa hadayar tumaki da bijimai masu yawa da ba a iya lissaftawa, ko ƙirgawa.
And king Solomon and all the congregation of Israel, that were assembled unto him, were with him before the ark, sacrificing sheep and oxen, that could not be counted nor numbered for multitude.
6 Sa’an nan firistoci suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji inda aka shirya masa, can ciki cikin haikali, a Wuri Mafi Tsarki, aka kuma sa shi a ƙarƙashin fikafikan kerubobin.
And the priests brought in the ark of the covenant of Jehovah unto its place, into the oracle of the house, to the most holy place, even under the wings of the cherubim.
7 Kerubobin sun buɗe fikafikansu a bisa wurin da akwatin alkawarin yake, suka inuwartar da akwatin alkawarin da sandunan ɗaukansa.
For the cherubim spread forth their wings over the place of the ark, and the cherubim covered the ark and the staves thereof above.
8 Waɗannan sandunan sun yi tsawo har ana iya ganin bakinsu daga Wuri Mai Tsarki a gaban wuri mai tsarki na can ciki, amma ba a iya ganinsu daga waje na Wuri Mai Tsarki ba. Suna nan kuwa a can har wa yau.
And the staves were so long that the ends of the staves were seen from the holy place before the oracle; but they were not seen without: and there they are unto this day.
9 Ba kome a cikin akwatin alkawarin, sai dai alluna na dutse guda biyu waɗanda Musa ya ajiye a ciki tun a Horeb, inda Ubangiji ya yi alkawari da Isra’ilawa bayan sun fito Masar.
There was nothing in the ark save the two tables of stone which Moses put there at Horeb, when Jehovah made a covenant with the children of Israel, when they came out of the land of Egypt.
10 Sa’ad da firistoci suka janye daga Wuri Mai Tsarki, sai girgije ya cika haikalin Ubangiji.
And it came to pass, when the priests were come out of the holy place, that the cloud filled the house of Jehovah,
11 Firistocin kuwa ba su iya yin hidimarsu ba saboda girgijen, gama ɗaukakar Ubangiji ta cika haikalinsa.
so that the priests could not stand to minister by reason of the cloud; for the glory of Jehovah filled the house of Jehovah.
12 Sai Solomon ya ce, “Ubangiji ya ce zai zauna a gizagizai masu duhu;
Then spake Solomon, Jehovah hath said that he would dwell in the thick darkness.
13 ga shi na gina haikali mai daraja dominka, inda za ka zauna har abada.”
I have surely built thee a house of habitation, a place for thee to dwell in for ever.
14 Yayinda dukan taron Isra’ila suke tsattsaye a can, sai sarki ya juya ya albarkace su.
And the king turned his face about, and blessed all the assembly of Israel: and all the assembly of Israel stood.
15 Sa’an nan ya ce, “Ku yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda da hannunsa ya cika abin da ya yi alkawari da bakinsa ga mahaifina Dawuda. Gama ya ce,
And he said, Blessed be Jehovah, the God of Israel, who spake with his mouth unto David my father, and hath with his hand fulfilled it, saying,
16 ‘Tun ran da na fitar da mutanena Isra’ila daga Masar, ban zaɓi wani birni a cikin wata kabilar Isra’ila a gina haikali domin Sunana yă kasance a can ba, amma na zaɓi Dawuda yă yi mulkin mutanena Isra’ila.’
Since the day that I brought forth my people Israel out of Egypt, I chose no city out of all the tribes of Israel to build a house, that my name might be there; but I chose David to be over my people Israel.
17 “Mahaifina Dawuda ya yi niyya a cikin zuciyarsa yă gina haikali saboda Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Now it was in the heart of David my father to build a house for the name of Jehovah, the God of Israel.
18 Amma Ubangiji ya ce wa mahaifina Dawuda, ‘Saboda yana a zuciyarka ka gina haikali domin Sunana, ka yi daidai da ka yi niyyar wannan a zuciyarka.
But Jehovah said unto David my father, Whereas it was in thy heart to build a house for my name, thou didst well that it was in thy heart:
19 Duk da haka, ba kai ba ne za ka gina haikali, amma ɗanka, wanda yake namanka da jininka, shi ne wanda zai gina haikali domin Sunana.’
nevertheless thou shalt not build the house; but thy son that shall come forth out of thy loins, he shall build the house for my name.
20 “Ubangiji ya kiyaye alkawarin da ya yi. Na gāje Dawuda mahaifina, yanzu kuma ga shi na zauna a kujerar sarautar Isra’ila, kamar dai yadda Ubangiji ya yi alkawari, na kuma gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
And Jehovah hath established his word that he spake; for I am risen up in the room of David my father, and sit on the throne of Israel, as Jehovah promised, and have built the house for the name of Jehovah, the God of Israel.
21 Na tanada wuri saboda akwatin alkawari, akwatin da ya ƙunshi alkawarin da Ubangiji ya yi da kakanninmu sa’ad da ya fitar da su daga Masar.”
And there have I set a place for the ark, wherein is the covenant of Jehovah, which he made with our fathers, when he brought them out of the land of Egypt.
22 Sai Solomon ya tsaya a gaban bagaden Ubangiji, a gaban dukan taron Isra’ila, ya ɗaga hannuwansa sama,
And Solomon stood before the altar of Jehovah in the presence of all the assembly of Israel, and spread forth his hands toward heaven;
23 ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, babu Allah kamar ka a sama can bisa, ko a ƙasa can ƙarƙashi, kai da kake kiyaye alkawarinka na ƙauna ga bayinka waɗanda suke cin gaba a hanyarka da dukan zuciyarsu.
and he said, O Jehovah, the God of Israel, there is no God like thee, in heaven above, or on earth beneath; who keepest covenant and lovingkindness with thy servants, that walk before thee with all their heart;
24 Ka kiyaye alkawarinka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina. Da bakinka ka yi alkawari, da hannunka kuma ka cika shi, yadda yake a yau.
who hast kept with thy servant David my father that which thou didst promise him: yea, thou spakest with thy mouth, and hast fulfilled it with thy hand, as it is this day.
25 “Yanzu, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bari ka cika wa bawanka Dawuda mahaifina alkawaran da ka yi masa sa’ad da ka ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani da zai zauna a gabana a kan kujerar sarautar Isra’ila ba, in kawai’ya’yanka maza sun yi hankali cikin dukan abubuwan da suke yi, don su yi tafiya a gabana kamar yadda ka yi.’
Now therefore, O Jehovah, the God of Israel, keep with thy servant David my father that which thou hast promised him, saying, There shall not fail thee a man in my sight to sit on the throne of Israel, if only thy children take heed to their way, to walk before me as thou hast walked before me.
26 Yanzu fa, ya Allah na Isra’ila, bari maganarka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina tă cika.
Now therefore, O God of Israel, let thy word, I pray thee, be verified, which thou spakest unto thy servant David my father.
27 “Amma anya, Allah, za ka zauna a duniya? Sammai, har ma da saman sammai ba za tă iya riƙe ka ba, balle wannan haikalin da na gina!
But will God in very deed dwell on the earth? behold, heaven and the heaven of heavens cannot contain thee; how much less this house that I have builded!
28 Duk da haka ka ji addu’ar bawanka da kuma roƙonsa don jinƙai, ya Ubangiji Allahna. Ka ji kuka da addu’ar da bawanka yake yi a gabanka a wannan rana.
Yet have thou respect unto the prayer of thy servant, and to his supplication, O Jehovah my God, to hearken unto the cry and to the prayer which thy servant prayeth before thee this day;
29 Bari idanunka su buɗe, su fuskanci wannan haikali dare da rana, wannan wurin da ka ce, ‘Sunana zai kasance a can,’ saboda ka ji addu’ar bawanka in yana fuskantar wannan wuri.
that thine eyes may be open toward this house night and day, even toward the place whereof thou hast said, My name shall be there; to hearken unto the prayer which thy servant shall pray toward this place.
30 Ka ji roƙon bawanka da kuma na mutanenka Isra’ila sa’ad da suka yi addu’a, suka fuskanci wannan wuri. Ka ji daga sama, mazauninka, kuma sa’ad da ka ji, ka gafarta.
And hearken thou to the supplication of thy servant, and of thy people Israel, when they shall pray toward this place: yea, hear thou in heaven thy dwelling-place; and when thou hearest, forgive.
31 “Sa’ad da mutum ya yi abin da ba daidai ba ga maƙwabcinsa, an kuma bukace shi yă yi rantsuwa, sai ya zo ya rantse a gaban bagade a cikin haikalin nan,
If a man sin against his neighbor, and an oath be laid upon him to cause him to swear, and he come [and] swear before thine altar in this house;
32 sai ka ji daga sama, ka kuma yi wani abu. Ka shari’anta tsakanin bayinka, ka hukunta mai laifi, ka mai da laifinsa a kansa, mai gaskiya kuma ka nuna shi marar laifi ne bisa ga gaskiyarsa.
then hear thou in heaven, and do, and judge thy servants, condemning the wicked, to bring his way upon his own head, and justifying the righteous, to give him according to his righteousness.
33 “Sa’ad da abokan gāba suka ci mutanenka Isra’ila a yaƙi saboda sun yi maka zunubi, sa’ad da kuma suka dawo gare ka don su furta sunanka, suna addu’a suna roƙo gare ka a wannan haikali,
When thy people Israel are smitten down before the enemy, because they have sinned against thee; if they turn again to thee, and confess thy name, and pray and make supplication unto thee in this house:
34 ka ji daga sama, ka gafarta zunubin mutanenka, ka kuma dawo da su ƙasar da ka ba wa kakanninsu.
then hear thou in heaven, and forgive the sin of thy people Israel, and bring them again unto the land which thou gavest unto their fathers.
35 “Sa’ad da sammai sun kulle, babu kuma ruwan sama domin mutane sun yi maka zunubi, sa’ad da suka yi addu’a suna fuskantar wannan wuri, suka kuma furta sunanka, suka juye daga zunubinsu domin ka hore su,
When heaven is shut up, and there is no rain, because they have sinned against thee; if they pray toward this place, and confess thy name, and turn from their sin, when thou dost afflict them:
36 ka ji daga sama, ka kuma gafarta zunubin bayinka, mutanenka Isra’ila. Ka koya musu hanyar da ta dace ta rayuwa, ka kuma aika da ruwan sama a ƙasar da ka ba wa mutanenka gādo.
then hear thou in heaven, and forgive the sin of thy servants, and of thy people Israel, when thou teachest them the good way wherein they should walk; and send rain upon thy land, which thou hast given to thy people for an inheritance.
37 “Sa’ad da yunwa ko annoba ta fāɗo a ƙasar, ko burtuntuna, ko fumfuna, ko fāri, ko tsutsa, ko kuwa abokan gāba sun yi musu kwanto, a wani daga cikin biranensu, duk wata cuta, ko ciwon da ya zo,
If there be in the land famine, if there be pestilence, if there be blasting [or] mildew, locust [or] caterpillar; if their enemy besiege them in the land of their cities; whatsoever plague, whatsoever sickness there be;
38 in suka yi addu’a ko roƙo ta wurin wani daga cikin mutanenka Isra’ila, kowa ya san wahalar zuciyarsa, ya kuma buɗe hannuwansa yana fuskantar wannan haikali,
what prayer and supplication soever be made by any man, [or] by all thy people Israel, who shall know every man the plague of his own heart, and spread forth his hands toward this house:
39 sai ka ji daga sama, mazauninka. Ka gafarta, ka kuma yi wani abu. Ka yi da kowane mutum bisa ga dukan abin da ya yi, tun da yake ka san zuciyarsa (gama kai kaɗai ka san zukatan dukan mutane),
then hear thou in heaven thy dwelling-place, and forgive, and do, and render unto every man according to all his ways, whose heart thou knowest; (for thou, even thou only, knowest the hearts of all the children of men; )
40 saboda su ji tsoronka a kowane lokacin da suke zaune a ƙasar da ka ba wa kakanninmu.
that they may fear thee all the days that they live in the land which thou gavest unto our fathers.
41 “Game da baƙo kuwa wanda shi ba na mutanenka Isra’ila ba, amma ya zo daga ƙasa mai nisa saboda sunanka,
Moreover concerning the foreigner, that is not of thy people Israel, when he shall come out of a far country for thy name’s sake
42 gama mutane za su ji game da girman sunanka, da ƙarfin hannunka, da kuma hannunka mai iko, sa’ad da ya zo, ya yi addu’a yana fuskantar wannan haikali,
(for they shall hear of thy great name, and of thy mighty hand, and of thine outstretched arm); when he shall come and pray toward this house;
43 ka ji daga sama, mazauninka, ka kuma yi dukan abin da baƙon ya tambaye ka, saboda dukan mutanen duniya su san sunanka, su kuma ji tsoronka, kamar yadda mutanenka Isra’ila suke yi, bari kuma su san cewa wannan gidan da na gina, ya amsa Sunanka.
hear thou in heaven thy dwelling-place, and do according to all that the foreigner calleth to thee for; that all the peoples of the earth may know thy name, to fear thee, as doth thy people Israel, and that they may know that this house which I have built is called by thy name.
44 “Sa’ad da mutanenka suka tafi yaƙi da abokan gābansu, a duk inda ka aike su, sa’ad da kuma suka yi addu’a ga Ubangiji suna fuskantar birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka,
If thy people go out to battle against their enemy, by whatsoever way thou shalt send them, and they pray unto Jehovah toward the city which thou hast chosen, and toward the house which I have built for thy name;
45 ka ji addu’arsu da roƙonsu daga sama, ka kuma biya musu bukatansu.
then hear thou in heaven their prayer and their supplication, and maintain their cause.
46 “Sa’ad da suka yi maka zunubi, gama babu wanda ba ya zunubi, ka kuwa yi fushi da su, ka kuma ba da su ga abokin gāba, wanda ya kwashe su kamammu zuwa ƙasarsa, nesa ko kusa;
If they sin against thee (for there is no man that sinneth not), and thou be angry with them, and deliver them to the enemy, so that they carry them away captive unto the land of the enemy, far off or near;
47 in suka canja zuciyarsu a ƙasar da aka riƙe su kamammu, suka tuba, suka kuma roƙe ka a ƙasar waɗanda suka ci su da yaƙi, suka ce, ‘Mun yi zunubi, mun yi abin da ba daidai ba, mun yi mugunta’;
yet if they shall bethink themselves in the land whither they are carried captive, and turn again, and make supplication unto thee in the land of them that carried them captive, saying, We have sinned, and have done perversely, we have dealt wickedly;
48 in sun juye gare ka da dukan zuciyarsu, da dukan ransu a ƙasar abokan gābansu waɗanda suka kwashe kamammu, suka yi addu’a gare ka, suka fuskanci wajen ƙasar da ka ba wa kakanninsu, waje birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka;
if they return unto thee with all their heart and with all their soul in the land of their enemies, who carried them captive, and pray unto thee toward their land, which thou gavest unto their fathers, the city which thou hast chosen, and the house which I have built for thy name:
49 sai ka ji daga sama, mazauninka, ka ji addu’a da roƙonsu, ka kuma biya musu bukatansu.
then hear thou their prayer and their supplication in heaven thy dwelling-place, and maintain their cause;
50 Ka gafarta wa mutanenka, waɗanda suka yi maka zunubi; ka gafarta dukan laifofin da suka yi maka, ka kuma sa waɗanda suka ci su a yaƙi su ji tausayinsu.
and forgive thy people who have sinned against thee, and all their transgressions wherein they have transgressed against thee; and give them compassion before those who carried them captive, that they may have compassion on them
51 Gama su mutanenka ne, abin gādonka, waɗanda ka fitar daga Masar, daga tanderu mai narken ƙarfe.
(for they are thy people, and thine inheritance, which thou broughtest forth out of Egypt, from the midst of the furnace of iron);
52 “Bari idanunka su buɗe ga roƙon bawanka, ga roƙon mutanenka Isra’ila, bari kuma ka saurare su sa’ad da suka yi kuka gare ka.
that thine eyes may be open unto the supplication of thy servant, and unto the supplication of thy people Israel, to hearken unto them whensoever they cry unto thee.
53 Gama ka ware su daga dukan al’umman duniya su zama abin gādonka, kamar yadda aka furta ta wurin bawanka Musa sa’ad da kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka ka fitar da kakanninmu daga Masar.”
For thou didst separate them from among all the peoples of the earth, to be thine inheritance, as thou spakest by Moses thy servant, when thou broughtest our fathers out of Egypt, O Lord Jehovah.
54 Da Solomon ya gama dukan waɗannan addu’o’i da roƙe-roƙe ga Ubangiji, sai ya tashi daga gaban bagaden Ubangiji, inda ya durƙusa da hannuwansa a buɗe waje sama.
And it was so, that, when Solomon had made an end of praying all this prayer and supplication unto Jehovah, he arose from before the altar of Jehovah, from kneeling on his knees with his hands spread forth toward heaven.
55 Ya tashi ya kuma albarkaci dukan taron Isra’ila da babbar murya, yana cewa,
And he stood, and blessed all the assembly of Israel with a loud voice, saying,
56 “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda ya ba wa mutanensa hutu kamar dai yadda ya yi alkawari. Babu magana guda da ta kāsa cika cikin dukan alkawaransa masu kyau da ya yi ta wurin bawansa Musa.
Blessed be Jehovah, that hath given rest unto his people Israel, according to all that he promised: there hath not failed one word of all his good promise, which he promised by Moses his servant.
57 Bari Ubangiji Allah yă kasance tare da mu kamar yadda ya kasance da kakanninmu; kada yă taɓa rabu da mu, ko yă yashe mu.
Jehovah our God be with us, as he was with our fathers: let him not leave us, nor forsake us;
58 Bari yă juye zukatanmu gare shi, don mu yi tafiya a cikin dukan hanyoyinsa, mu kuma kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa, da kuma farillan da ya ba wa kakanninmu.
that he may incline our hearts unto him, to walk in all his ways, and to keep his commandments, and his statutes, and his ordinances, which he commanded our fathers.
59 Bari kuma waɗannan kalmomina, waɗanda na yi addu’a a gaban Ubangiji, su yi kusa da Ubangiji Allahnmu, dare da rana, don yă biya bukatan bawansa da na mutanensa Isra’ila, bisa ga bukatan kowa,
And let these my words, wherewith I have made supplication before Jehovah, be nigh unto Jehovah our God day and night, that he maintain the cause of his servant, and the cause of his people Israel, as every day shall require;
60 saboda dukan mutanen duniya su san cewa Ubangiji, shi ne Allah, babu kuma wani.
that all the peoples of the earth may know that Jehovah, he is God; there is none else.
61 Amma dole ku miƙa zukatanku ga Ubangiji Allahnmu, don ku rayu, ta wurin bin ƙa’idodinsa, ku kuma yi biyayya da umarnansa, kamar yadda kuke yi a wannan lokaci.”
Let your heart therefore be perfect with Jehovah our God, to walk in his statutes, and to keep his commandments, as at this day.
62 Sai sarki da dukan Isra’ila, suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
And the king, and all Israel with him, offered sacrifice before Jehovah.
63 Solomon ya miƙa hadaya ta salama ga Ubangiji, shanu dubu ashirin da biyu, tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan Isra’ilawa suka keɓe haikalin Ubangiji.
And Solomon offered for the sacrifice of peace-offerings, which he offered unto Jehovah, two and twenty thousand oxen, and a hundred and twenty thousand sheep. So the king and all the children of Israel dedicated the house of Jehovah.
64 A wannan rana sarki ya tsarkake sashe na tsakiyar fili a gaban haikalin Ubangiji, a can kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa, hadaya ta gari, da kitsen hadaya ta salama, gama bagaden tagulla a gaban Ubangiji ya yi ƙanƙanta sosai da za a miƙa hadayun ƙonawa, hadayun hatsi, da kuma kitsen hadayun salama.
The same day did the king hallow the middle of the court that was before the house of Jehovah; for there he offered the burnt-offering, and the meal-offering, and the fat of the peace-offerings, because the brazen altar that was before Jehovah was too little to receive the burnt-offering, and the meal-offering, and the fat of the peace-offerings.
65 Ta haka Solomon da dukan Isra’ila, wato, babban taro, suka yi bikin a lokacin. Mutane suka zo, tun daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar. Suka yi biki a gaban Ubangiji Allahnmu, kwana bakwai. Suka kuma ƙara kwana bakwai, kwanaki goma sha huɗu gaba ɗaya.
So Solomon held the feast at that time, and all Israel with him, a great assembly, from the entrance of Hamath unto the brook of Egypt, before Jehovah our God, seven days and seven days, even fourteen days.
66 A rana ta biye sai ya sallame mutane. Suka sa wa sarki albarka, sa’an nan suka watse zuwa gida, da farin ciki, da murna a zukatansu saboda kyawawan abubuwan da Ubangiji ya yi domin bawansa Dawuda, da kuma mutanensa Isra’ila.
On the eighth day he sent the people away; and they blessed the king, and went unto their tents joyful and glad of heart for all the goodness that Jehovah had showed unto David his servant, and to Israel his people.

< 1 Sarakuna 8 >