< 1 Sarakuna 8 >

1 Sai Sarki Solomon ya tattara dattawan Urushalima a gabansa, da dukan shugabannin kabilu, da shugabannin iyalan Isra’ilawa, domin su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Sihiyona, Birnin Dawuda.
Bangʼe Ruoth Solomon noluongo jodong jo-Israel mondo odhi ire Jerusalem gi jodong dhoudi duto gi jotend anywola mag Israel mondo gikel Sandug Muma mar singruok mar Jehova Nyasaye koa Dala Maduongʼ mar Daudi miluongo ni Sayun.
2 Dukan mutanen Isra’ila suka tattaru a gaban Sarki Solomon a lokacin biki, a watan Etanim, wato, wata na bakwai.
Jo-Israel duto nochokore kanyakla ir Ruoth Solomon e kinde mag nyasi e dwe mar Ethanim, ma en dwe mar abiriyo.
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka iso, sai firistoci suka ɗauki akwatin alkawarin,
Kane jodong Israel duto osechopo, jodolo nokawo Sandug Muma,
4 suka haura da akwatin alkawarin Ubangiji da kuma Tentin Sujada, da dukan kayayyaki masu tsarkin da suke cikinsa. Firistoci da Lawiyawa suka ɗauko su,
kendo negikelo Sandug Muma mar Jehova Nyasaye gi Hemb Romo kod gik moko duto maler mane ni e iye. Jodolo kod jo-Lawi notingʼogi,
5 sai Sarki Solomon da dukan taron Isra’ila da suka tattaru kewaye da shi a gaban akwatin alkawari, suka yi ta miƙa hadayar tumaki da bijimai masu yawa da ba a iya lissaftawa, ko ƙirgawa.
kendo Ruoth Solomon kod oganda jo-Israel duto mane ochokore molwore nochopo e nyim Sandug Muma; kendo negichiwo rombe kod dhok mangʼeny mane kwan-gi ok nyal ndiki kata kwan kaka misango.
6 Sa’an nan firistoci suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji inda aka shirya masa, can ciki cikin haikali, a Wuri Mafi Tsarki, aka kuma sa shi a ƙarƙashin fikafikan kerubobin.
Eka jodolo nokelo Sandug Muma mar singruok mar Jehova Nyasaye kama ne olosne ei kama ler mar lemo mar hekalu ma en Kama Ler Moloyo mi gikete e bwomb kerubi.
7 Kerubobin sun buɗe fikafikansu a bisa wurin da akwatin alkawarin yake, suka inuwartar da akwatin alkawarin da sandunan ɗaukansa.
Kerubigo noyaro bwombegi ewi kama noketie Sandug Muma kendo ne giumo Sandug Muma gi ludhe mitingʼego.
8 Waɗannan sandunan sun yi tsawo har ana iya ganin bakinsu daga Wuri Mai Tsarki a gaban wuri mai tsarki na can ciki, amma ba a iya ganinsu daga waje na Wuri Mai Tsarki ba. Suna nan kuwa a can har wa yau.
Ludhegi ne boyo ahinya ma gikogi ne inyalo ne koa e nyim Kama Ler e nyim kama ler mar lemo, to ne ok ginen gi oko mar Kama Ler kendo pod gin kanyo nyaka chil kawuono.
9 Ba kome a cikin akwatin alkawarin, sai dai alluna na dutse guda biyu waɗanda Musa ya ajiye a ciki tun a Horeb, inda Ubangiji ya yi alkawari da Isra’ilawa bayan sun fito Masar.
Ne onge gimoro ei Sandug Muma makmana kite ariyo mopa mane Musa oketo e iye kane en Horeb kama Jehova Nyasaye ne otimoe singruok kod jo-Israel kane gisewuok Misri.
10 Sa’ad da firistoci suka janye daga Wuri Mai Tsarki, sai girgije ya cika haikalin Ubangiji.
Kane jodolo osewuok ei Kama Ler, bor polo noimo hekalu mar Jehova Nyasaye,
11 Firistocin kuwa ba su iya yin hidimarsu ba saboda girgijen, gama ɗaukakar Ubangiji ta cika haikalinsa.
kendo jodolo ne ok nyal tiyo tijegi nikech bor polo nimar duongʼ mar Jehova Nyasaye nopongʼo hekalu.
12 Sai Solomon ya ce, “Ubangiji ya ce zai zauna a gizagizai masu duhu;
Eka Solomon nowacho niya, “Jehova Nyasaye osewacho ni enodag ei bor polo motimo mudho;
13 ga shi na gina haikali mai daraja dominka, inda za ka zauna har abada.”
adier asegeroni hekalu marahuma kama inidagie nyaka chiengʼ.”
14 Yayinda dukan taron Isra’ila suke tsattsaye a can, sai sarki ya juya ya albarkace su.
Kane oganda jo-Israel duto ochungʼ kanyo, ruoth nolokore mogwedhogi.
15 Sa’an nan ya ce, “Ku yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda da hannunsa ya cika abin da ya yi alkawari da bakinsa ga mahaifina Dawuda. Gama ya ce,
Eka nowacho niya, “Pak obed ne Jehova Nyasaye, ma Nyasach Israel, mosetimo gi lwete gima ne osingo gi dhoge owuon ni Daudi wuonwa.
16 ‘Tun ran da na fitar da mutanena Isra’ila daga Masar, ban zaɓi wani birni a cikin wata kabilar Isra’ila a gina haikali domin Sunana yă kasance a can ba, amma na zaɓi Dawuda yă yi mulkin mutanena Isra’ila.’
Nimar nowacho ni, ‘Chakre ndalo mane agolo joga koa Misri, pok ayiero dala maduongʼ e dhoot moro amora mar Israel mondo oger hekalu kanyo ni Nyinga, to aseyiero Daudi mondo otel ni joga Israel.’
17 “Mahaifina Dawuda ya yi niyya a cikin zuciyarsa yă gina haikali saboda Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
“Daudi wuora noketo e chunye mondo oger hekalu moluongo nying Jehova Nyasaye, ma Nyasach Israel.
18 Amma Ubangiji ya ce wa mahaifina Dawuda, ‘Saboda yana a zuciyarka ka gina haikali domin Sunana, ka yi daidai da ka yi niyyar wannan a zuciyarka.
To Jehova Nyasaye nowacho ni Daudi wuora ni, ‘Nitimo maber mondo ibed gi wach gero hekalu ni nyinga e chunyi.
19 Duk da haka, ba kai ba ne za ka gina haikali, amma ɗanka, wanda yake namanka da jininka, shi ne wanda zai gina haikali domin Sunana.’
Kata kamano, in ok niger hekalu, to wuodi, ma en ringri gi rembi iwuon, en ema noger hekalu ni Nyinga.’
20 “Ubangiji ya kiyaye alkawarin da ya yi. Na gāje Dawuda mahaifina, yanzu kuma ga shi na zauna a kujerar sarautar Isra’ila, kamar dai yadda Ubangiji ya yi alkawari, na kuma gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
“Jehova Nyasaye oserito singruok mane otimo: Asekawo loch wuora Daudi kendo asebet e kom loch mar Israel, mana kaka Jehova Nyasaye nosingo, kendo asegero hekalu ni Nying Jehova Nyasaye, ma Nyasach Israel.
21 Na tanada wuri saboda akwatin alkawari, akwatin da ya ƙunshi alkawarin da Ubangiji ya yi da kakanninmu sa’ad da ya fitar da su daga Masar.”
Aseloso kar Sandug Muma, moketie singruok mane Jehova Nyasaye otimo kod kwerewa kane ogologi Misri.”
22 Sai Solomon ya tsaya a gaban bagaden Ubangiji, a gaban dukan taron Isra’ila, ya ɗaga hannuwansa sama,
Eka Solomon nochungʼ e nyim kendo mar misango mar Jehova Nyasaye e nyim oganda duto mar jo-Israel, kendo norieyo bedene kochomo polo
23 ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, babu Allah kamar ka a sama can bisa, ko a ƙasa can ƙarƙashi, kai da kake kiyaye alkawarinka na ƙauna ga bayinka waɗanda suke cin gaba a hanyarka da dukan zuciyarsu.
kowacho kama: “Yaye Jehova Nyasaye, ma Nyasach Israel, onge Nyasaye moro amora machal kodi e polo malo kata e piny mwalo, in e Nyasaye marito singruok mar herane ni jotichne maluwo yoreni gi chunygi duto.
24 Ka kiyaye alkawarinka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina. Da bakinka ka yi alkawari, da hannunka kuma ka cika shi, yadda yake a yau.
Iserito singruokni mane itimo gi jatichni Daudi wuora ne isingori gi dhogi kendo isechopo singruokno gi lweti mana kaka en kawuononi.
25 “Yanzu, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bari ka cika wa bawanka Dawuda mahaifina alkawaran da ka yi masa sa’ad da ka ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani da zai zauna a gabana a kan kujerar sarautar Isra’ila ba, in kawai’ya’yanka maza sun yi hankali cikin dukan abubuwan da suke yi, don su yi tafiya a gabana kamar yadda ka yi.’
“Koro Jehova Nyasaye, ma Nyasach Israel rit singruok mane itimo gi jatichni Daudi wuora kiwachone niya, ‘Ok inibed maonge gi ngʼato mobedo e kom loch e nyima e piny Israel, to mana ka yawuoti otimo tim makare e nyima mana kaka isetimo.’
26 Yanzu fa, ya Allah na Isra’ila, bari maganarka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina tă cika.
To koro, yaye Nyasach Israel, yie wach mane isingo ni jatichni Daudi wuora otimre mana kaka ne isingo.
27 “Amma anya, Allah, za ka zauna a duniya? Sammai, har ma da saman sammai ba za tă iya riƙe ka ba, balle wannan haikalin da na gina!
“To bende Nyasaye nyalo dak e piny? Kata polo malo kata polo mabor moloyo ok nyal romi. To koro hekalu mageroni, to diromi nade!
28 Duk da haka ka ji addu’ar bawanka da kuma roƙonsa don jinƙai, ya Ubangiji Allahna. Ka ji kuka da addu’ar da bawanka yake yi a gabanka a wannan rana.
Kata kamano chik iti ni lamo jatichni gi kwayone mar ngʼwono, yaye Jehova Nyasaye Nyasacha. Winji ywak gi lemo ma jatichni lamo e nyimi kawuono.
29 Bari idanunka su buɗe, su fuskanci wannan haikali dare da rana, wannan wurin da ka ce, ‘Sunana zai kasance a can,’ saboda ka ji addu’ar bawanka in yana fuskantar wannan wuri.
Mad wangʼi rang hekaluni otieno kod odiechiengʼ, kama niwacho niya, ‘Nyinga nobed kanyo,’ mondo iwinji lemo ma jatichni lamo kochomo odni.
30 Ka ji roƙon bawanka da kuma na mutanenka Isra’ila sa’ad da suka yi addu’a, suka fuskanci wannan wuri. Ka ji daga sama, mazauninka, kuma sa’ad da ka ji, ka gafarta.
Winji lamo mar jatichni kaachiel gi jogi Israel ka gilamo ka gichomo odni. Winji gi e polo kar dakni, kendo kiwinjo, to iwenwa richowa.
31 “Sa’ad da mutum ya yi abin da ba daidai ba ga maƙwabcinsa, an kuma bukace shi yă yi rantsuwa, sai ya zo ya rantse a gaban bagade a cikin haikalin nan,
“Ka ngʼato oketho ni wadgi kendo dwarore ni mondo okwongʼre kendo obiro mokwongʼore e nyim kendo mar misango manie hekaluni,
32 sai ka ji daga sama, ka kuma yi wani abu. Ka shari’anta tsakanin bayinka, ka hukunta mai laifi, ka mai da laifinsa a kansa, mai gaskiya kuma ka nuna shi marar laifi ne bisa ga gaskiyarsa.
to iwinji gi e polo kendo itim kaka owinjore. Ngʼad bura e kind jotichni, kikumo joketho kendo iket richogi e wigi bende joma onge ketho iket kare kaluwore gi timgi makare.
33 “Sa’ad da abokan gāba suka ci mutanenka Isra’ila a yaƙi saboda sun yi maka zunubi, sa’ad da kuma suka dawo gare ka don su furta sunanka, suna addu’a suna roƙo gare ka a wannan haikali,
“Ka jogi Israel olo e lweny gi jowasikgi nikech gisekethoni, to bangʼe gilokore mi gipako nyingi, ka gilamo kendo gikwayo e hekaluni,
34 ka ji daga sama, ka gafarta zunubin mutanenka, ka kuma dawo da su ƙasar da ka ba wa kakanninsu.
to iwinjgi gi e polo kendo iwe richo jogi Israel kendo iduog-gi e piny mane imiyo kweregi.
35 “Sa’ad da sammai sun kulle, babu kuma ruwan sama domin mutane sun yi maka zunubi, sa’ad da suka yi addu’a suna fuskantar wannan wuri, suka kuma furta sunanka, suka juye daga zunubinsu domin ka hore su,
“Ka polo olor kendo koth onge nikech jogi osekethoni to ka gilemo kaeni ka gipako nyingi kendo ka gilokore giweyo richogi nikech isekelonegi chandruok,
36 ka ji daga sama, ka kuma gafarta zunubin bayinka, mutanenka Isra’ila. Ka koya musu hanyar da ta dace ta rayuwa, ka kuma aika da ruwan sama a ƙasar da ka ba wa mutanenka gādo.
to yie mondo iwinjgi gie polo kendo iwene jotichni ma jo-Israel richogi. Puonjgi yo makare mar dak kendo iornegi koth e piny mane imiyo jogi kaka girkeni margi.
37 “Sa’ad da yunwa ko annoba ta fāɗo a ƙasar, ko burtuntuna, ko fumfuna, ko fāri, ko tsutsa, ko kuwa abokan gāba sun yi musu kwanto, a wani daga cikin biranensu, duk wata cuta, ko ciwon da ya zo,
“Ka kech kata dera omako piny, kata ka abach omako cham ewi dongo kata ka bonyo kata kungu kata ka jowasigu olworo miechgi madongo kata ka midekre kata tuo omakogi,
38 in suka yi addu’a ko roƙo ta wurin wani daga cikin mutanenka Isra’ila, kowa ya san wahalar zuciyarsa, ya kuma buɗe hannuwansa yana fuskantar wannan haikali,
to ka ngʼato kuom jogi ma jo-Israel olemo kata okwayi, ka gingʼeyo gima chando chunygi kendo ka girieyo bedegi kochomo hekaluni,
39 sai ka ji daga sama, mazauninka. Ka gafarta, ka kuma yi wani abu. Ka yi da kowane mutum bisa ga dukan abin da ya yi, tun da yake ka san zuciyarsa (gama kai kaɗai ka san zukatan dukan mutane),
to yie iwinji gie polo, kama idakie. Wenegi richogi kendo tim ne ngʼato ka ngʼato gima owinjore gi gik motimo nikech ingʼeyo chunygi (nikech in kendi ema ingʼeyo chuny dhano),
40 saboda su ji tsoronka a kowane lokacin da suke zaune a ƙasar da ka ba wa kakanninmu.
mondo omi gilwori ndalogi duto ma gin-go e piny mane imiyo kwerewa.
41 “Game da baƙo kuwa wanda shi ba na mutanenka Isra’ila ba, amma ya zo daga ƙasa mai nisa saboda sunanka,
“To kuom jadak ma ok achiel kuom jogi Israel moa e piny mabor nikech nyingi,
42 gama mutane za su ji game da girman sunanka, da ƙarfin hannunka, da kuma hannunka mai iko, sa’ad da ya zo, ya yi addu’a yana fuskantar wannan haikali,
nimar ji biro winjo humb nyingi maduongʼ gi mar lweti maratego kod badi marabora moriere, ka gibiro ma gilemo ka gichomo hekaluni
43 ka ji daga sama, mazauninka, ka kuma yi dukan abin da baƙon ya tambaye ka, saboda dukan mutanen duniya su san sunanka, su kuma ji tsoronka, kamar yadda mutanenka Isra’ila suke yi, bari kuma su san cewa wannan gidan da na gina, ya amsa Sunanka.
to yie mondo iwinji gie polo kama idakie kendo tim gimoro amora ma jadakno okwayi, mondo ogendini duto mag piny ongʼe nyingi kendo oluori mana kaka jogi Israel, kendo mondo gingʼe ni ot ma asegeroni luongo nyingi.
44 “Sa’ad da mutanenka suka tafi yaƙi da abokan gābansu, a duk inda ka aike su, sa’ad da kuma suka yi addu’a ga Ubangiji suna fuskantar birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka,
“Ka jogi odhi kedo gi jowasikgi, kamoro amora ma ibiro orogie, ka gilamo Jehova Nyasaye ka gichomo dalani miseyiero kendo hekalu masegero maluongo nyingi;
45 ka ji addu’arsu da roƙonsu daga sama, ka kuma biya musu bukatansu.
to yie iwinji gie polo lamogi kod kwayogi kendo konygi.
46 “Sa’ad da suka yi maka zunubi, gama babu wanda ba ya zunubi, ka kuwa yi fushi da su, ka kuma ba da su ga abokin gāba, wanda ya kwashe su kamammu zuwa ƙasarsa, nesa ko kusa;
“To ka giketho e nyimi, nimar onge ngʼato kata achiel ma ok jaketho mi ikecho kodgi, kendo ichiwogi e lwet wasikgi mondo otergi e twech e piny wasikgigo, kuma bor kata machiegni;
47 in suka canja zuciyarsu a ƙasar da aka riƙe su kamammu, suka tuba, suka kuma roƙe ka a ƙasar waɗanda suka ci su da yaƙi, suka ce, ‘Mun yi zunubi, mun yi abin da ba daidai ba, mun yi mugunta’;
to eka bangʼe giloko pachgi e piny motwegieno mi chunygi olokore giweyo richo, kendo gikwayi ka gin e piny wasikgi niya, ‘Wasetimo richo kendo waseketho bende wasetimo tim mamono.’
48 in sun juye gare ka da dukan zuciyarsu, da dukan ransu a ƙasar abokan gābansu waɗanda suka kwashe kamammu, suka yi addu’a gare ka, suka fuskanci wajen ƙasar da ka ba wa kakanninsu, waje birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka;
Kendo ka gidwogo iri gi chunygi duto kod ngimagi duto, e piny wasikgi mane otweyogieno, kendo gilami ka gichomo pinygi mane imiyo kweregi, kod dala mane iyiero, gi hekalu ma asegero ni nyingi;
49 sai ka ji daga sama, mazauninka, ka ji addu’a da roƙonsu, ka kuma biya musu bukatansu.
to yie mondo iwinj lemogi gi kwayogi gie polo kama idakie kendo ikonygi.
50 Ka gafarta wa mutanenka, waɗanda suka yi maka zunubi; ka gafarta dukan laifofin da suka yi maka, ka kuma sa waɗanda suka ci su a yaƙi su ji tausayinsu.
Yie iwe ni jogi mosetimo richo e nyimi, wenegi kethogi duto magisetimo e nyimi kendo mi joma ne omakogi okechgi.
51 Gama su mutanenka ne, abin gādonka, waɗanda ka fitar daga Masar, daga tanderu mai narken ƙarfe.
Nimar gin jogi kendo mwanduni mane igolo e piny Misri, kigologi kama mae kakni ka kama ithedhe nyinyo.
52 “Bari idanunka su buɗe ga roƙon bawanka, ga roƙon mutanenka Isra’ila, bari kuma ka saurare su sa’ad da suka yi kuka gare ka.
“Yie wangʼi one kwayo jatichni kod kwayo mag jogi Israel, bende yie iwinjgi kinde moro amora ma giywaknie.
53 Gama ka ware su daga dukan al’umman duniya su zama abin gādonka, kamar yadda aka furta ta wurin bawanka Musa sa’ad da kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka ka fitar da kakanninmu daga Masar.”
Nimar niyierogi e kind ogendini duto mag piny mondo gibed girkeni, mana kaka ninyiso jatichni Musa kane igolo kwerewa e piny Misri; yaye Jehova Nyasaye Manyalo Gik Moko Duto.”
54 Da Solomon ya gama dukan waɗannan addu’o’i da roƙe-roƙe ga Ubangiji, sai ya tashi daga gaban bagaden Ubangiji, inda ya durƙusa da hannuwansa a buɗe waje sama.
Kane Solomon osetieko lamogi duto kod kwayogi ni Jehova Nyasaye, nochungʼ oa e nyim kendo mar misango mar Jehova Nyasaye, kama nogoyoe chonge kotingʼo bade kochomo polo.
55 Ya tashi ya kuma albarkaci dukan taron Isra’ila da babbar murya, yana cewa,
Nochungʼ mogwedho chokruok duto mar Israel gi dwol maduongʼ kowacho niya,
56 “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda ya ba wa mutanensa hutu kamar dai yadda ya yi alkawari. Babu magana guda da ta kāsa cika cikin dukan alkawaransa masu kyau da ya yi ta wurin bawansa Musa.
“Pak obed ni Jehova Nyasaye mosemiyo joge Israel kwe mana kaka nosingo. Onge kata mana wach achiel ma ok osechopo kuom gik moko duto mabeyo mane ochiwo kuom jatichne Musa.
57 Bari Ubangiji Allah yă kasance tare da mu kamar yadda ya kasance da kakanninmu; kada yă taɓa rabu da mu, ko yă yashe mu.
Mad Jehova Nyasaye ma Nyasachwa obed kodwa mana kaka nobedo gi kwerewa, mad kik owewa kata jwangʼowa.
58 Bari yă juye zukatanmu gare shi, don mu yi tafiya a cikin dukan hanyoyinsa, mu kuma kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa, da kuma farillan da ya ba wa kakanninmu.
Mad olok chunywa ire, mondo wawuoth e yorene duto kendo wamak chikene gi puonjne kod buchene mane omiyo kwerewa.
59 Bari kuma waɗannan kalmomina, waɗanda na yi addu’a a gaban Ubangiji, su yi kusa da Ubangiji Allahnmu, dare da rana, don yă biya bukatan bawansa da na mutanensa Isra’ila, bisa ga bukatan kowa,
Kendo mad wechenagi maselamo e nyim Jehova Nyasaye, obed machiegni gi Jehova Nyasaye ma Nyasachwa odiechiengʼ gotieno, mondo okony jatichne kendo okony joge Israel kaluwore gi dwaro mar odiechiengʼ kodiechiengʼ;
60 saboda dukan mutanen duniya su san cewa Ubangiji, shi ne Allah, babu kuma wani.
mondo ji duto manie piny ongʼe ni Jehova Nyasaye e Nyasaye kendo ni onge moro.
61 Amma dole ku miƙa zukatanku ga Ubangiji Allahnmu, don ku rayu, ta wurin bin ƙa’idodinsa, ku kuma yi biyayya da umarnansa, kamar yadda kuke yi a wannan lokaci.”
To chunyu nyaka chiwre chuth ni Jehova Nyasaye ma Nyasachwa kudak moluwore gi yorene kendo kurito chikene kaka e kindeni.”
62 Sai sarki da dukan Isra’ila, suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
Eka ruoth kod jo-Israel duto mane ni kode nochiwo misengini e nyim Jehova Nyasaye.
63 Solomon ya miƙa hadaya ta salama ga Ubangiji, shanu dubu ashirin da biyu, tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan Isra’ilawa suka keɓe haikalin Ubangiji.
Solomon nochiwo misango mag lalruok ni Jehova Nyasaye: kwan-gi ne romo dhok alufu piero ariyo gi ariyo kod rombe gi diek maromo alufu mia achiel gi piero ariyo. Kamano ruoth kod jo-Israel duto nowalo hekalu ni Jehova Nyasaye.
64 A wannan rana sarki ya tsarkake sashe na tsakiyar fili a gaban haikalin Ubangiji, a can kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa, hadaya ta gari, da kitsen hadaya ta salama, gama bagaden tagulla a gaban Ubangiji ya yi ƙanƙanta sosai da za a miƙa hadayun ƙonawa, hadayun hatsi, da kuma kitsen hadayun salama.
Chiengʼono ruoth nopwodho dier laru mane nitie e nyim hekalu mar Jehova Nyasaye kendo kanyo nochiwoe misengini miwangʼo pep gi cham michiwo kod bor misango mar lalruok, nikech kendo mar misango mar mula mantie e nyim Jehova Nyasaye ne tin ahinya mane ok nyal tingʼo misangogo duto, kaka misango miwangʼo pep gi mag cham kod mag sawo.
65 Ta haka Solomon da dukan Isra’ila, wato, babban taro, suka yi bikin a lokacin. Mutane suka zo, tun daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar. Suka yi biki a gaban Ubangiji Allahnmu, kwana bakwai. Suka kuma ƙara kwana bakwai, kwanaki goma sha huɗu gaba ɗaya.
Kamano Solomon notimo sawo e kindeno kaachiel gi jo-Israel duto mane ni kode chokruok maduongʼ miwuoro kotingʼo joma oa Lebo Hamath nyaka Wadi man Misri. Negitimo nyasino e nyim Jehova Nyasaye ma Nyasachwa kuom ndalo abiriyo kendo gichak gimedo ndalo abiriyo mamoko duto ne gin ndalo apar gangʼwen.
66 A rana ta biye sai ya sallame mutane. Suka sa wa sarki albarka, sa’an nan suka watse zuwa gida, da farin ciki, da murna a zukatansu saboda kyawawan abubuwan da Ubangiji ya yi domin bawansa Dawuda, da kuma mutanensa Isra’ila.
Kinyne nomiyo ji thuolo mar ke. Negigwedho ruoth mi gidhi e miechgi, ka gimor kendo giil e chunygi nikech gik moko duto mabeyo mane Jehova Nyasaye osetimo ni jatichne Daudi kod joge Israel.

< 1 Sarakuna 8 >