< 1 Sarakuna 5 >

1 Sa’ad da Hiram sarkin Taya ya ji an shafe Solomon sarki yă gāji mahaifinsa Dawuda, sai ya aika da jakadunsa zuwa wurin Solomon, gama shi da Dawuda abokai ne sosai dukan kwanakinsa.
و حیرام، پادشاه صور، خادمان خود را نزدسلیمان فرستاد، چونکه شنیده بود که او رابه‌جای پدرش به پادشاهی مسح کرده‌اند، زیرا که حیرام همیشه دوست داود بود.۱
2 Solomon ya mayar da wannan saƙo ga Hiram ya ce,
و سلیمان نزد حیرام فرستاده، گفت۲
3 “Ka san cewa saboda yaƙe-yaƙen da abokan gāba suka yi da mahaifina a kowane gefe, ya sa bai iya gina haikali domin Sunan Ubangiji Allahnsa ba, sai da Ubangiji ya sa abokan gābansa a ƙarƙashin ƙafafunsa.
که «تو پدر من داود رامی دانی که نتوانست خانه‌ای به اسم یهوه، خدای خود بنا نماید به‌سبب جنگهایی که او را احاطه می‌نمود تا خداوند ایشان را زیر کف پایهای اونهاد.۳
4 Amma yanzu Ubangiji Allahna ya ba ni hutu a kowane gefe, babu kuma gāba ko masifa.
اما الان یهوه، خدای من، مرا از هر طرف آرامی داده است که هیچ دشمنی و هیچ واقعه بدی وجود ندارد.۴
5 Ina niyya in gina haikali domin Sunan Ubangiji Allahna, yadda Ubangiji ya faɗa wa mahaifina Dawuda, sa’ad da ya ce, ‘Ɗanka wanda zai gāje ka, shi zai gina haikali domin Sunana.’
و اینک مراد من این است که خانه‌ای به اسم یهوه، خدای خود، بنا نمایم چنانکه خداوند به پدرم داود وعده داد و گفت که پسرت که او را به‌جای تو بر کرسی خواهم نشانید، خانه را به اسم من بنا خواهد کرد.۵
6 “Don haka, ka ba da umarni a yanka mini itatuwan al’ul na ƙasar Lebanon. Ma’aikatana za su haɗa hannu da ma’aikatanka, ni kuwa zan biya ka albashin ma’aikatanka kamar yadda ka faɗa. Gama ka san cewa babu wani a cikinmu da ya iya yanka itacen katako kamar Sidoniyawa.”
و حال امر فرما که سروهای آزاد از لبنان برای من قطع نمایند و خادمان من همراه خادمان تو خواهندبود، و مزد خادمانت را موافق هرآنچه بفرمایی به تو خواهم داد، زیرا تو می‌دانی که در میان ما کسی نیست که مثل صیدونیان در قطع نمودن درختان ماهر باشد.»۶
7 Da Hiram ya ji saƙon Solomon, sai ya ji daɗi ƙwarai, ya kuma ce, “Yabo ga Ubangiji a yau, gama ya ba wa Dawuda ɗa mai hikima yă yi mulki a bisa wannan al’umma mai girma.”
پس چون حیرام سخنان سلیمان را شنید، به غایت شادمان شده، گفت: «امروز خداوند متبارک باد که به داود پسری حکیم بر این قوم عظیم عطانموده است.»۷
8 Sai Hiram ya aike wa Solomon da kalmomin nan, “Na sami saƙon da ka aika mini, zan kuma yi duk abin da kake so ta wurin tanada katakan al’ul da na fir.
و حیرام نزد سلیمان فرستاده، گفت: «پیغامی که نزد من فرستادی اجابت نمودم و من خواهش تو را درباره چوب سرو آزاد وچوب صنوبر بجا خواهم آورد.۸
9 Ma’aikatana za su gangara da su daga Lebanon zuwa bakin teku. Zan sa a ɗaɗɗaura su su bi ruwan teku daga Lebanon zuwa bakin Bahar Rum da za ka nuna mini. A can zan kunce maka su, sa’an nan ka kwashe. Kai kuma za ka biya bukatata ta wurin tanadin abinci wa gidana.”
خادمان من آنهارا از لبنان به دریا فرود خواهند‌آورد و من آنها رابستنه خواهم ساخت در دریا، تا مکانی که برای من معین کنی و آنها را در آنجا از هم باز خواهم کرد تا آنها را ببری و اما تو درباره دادن آذوقه به خانه من اراده مرا به‌جا خواهی آورد.»۹
10 A haka Hiram ya ci gaba da aika wa Solomon al’ul da kuma fir da yake bukata.
پس حیرام چوبهای سرو آزاد و چوبهای صنوبر را موافق تمامی اراده‌اش به سلیمان داد.۱۰
11 Solomon kuma ya ba wa Hiram mudu gari dubu ashirin na alkama a matsayin abinci domin gidansa, ya ƙara da garwa dubu ashirin na tataccen man zaitun. Solomon ya ci gaba da yin haka ga Hiram, shekara-shekara.
وسلیمان بیست هزار کر گندم و بیست هزار کرروغن صاف به حیرام به جهت قوت خانه‌اش داد، و سلیمان هرساله اینقدر به حیرام می‌داد.۱۱
12 Ubangiji ya ba wa Solomon hikima, kamar yadda ya yi masa alkawari. Dangantakar zaman lafiya ta kasance tsakanin Hiram da Solomon, su biyun suka yi yarjejjeniya.
وخداوند سلیمان را به نوعی که به او وعده داده بود، حکمت بخشید و در میان حیرام و سلیمان صلح بود و با یکدیگر عهد بستند.۱۲
13 Sarki Solomon ya ɗebi ma’aikata daga dukan Isra’ila, su dubu talatin.
و سلیمان پادشاه از تمامی اسرائیل سخره گرفت و آن سخره سی هزار نفر بود.۱۳
14 Ya riƙa aika su dubu goma-goma zuwa Lebanon kowane wata, saboda su yi wata ɗaya a Lebanon, watanni biyu kuma a gida. Adoniram ne ya lura da aikin gandun.
و از ایشان ده هزار نفر، هر ماهی به نوبت به لبنان می‌فرستاد. یک ماه در لبنان و دو ماه در خانه خویش می‌ماندند. و ادونیرام رئیس سخره بود.۱۴
15 Solomon ya kasance da’yan ɗauko guda dubu saba’in da masu yankan duwatsu guda dubu tamanin a cikin tuddai,
وسلیمان را هفتاد هزار مرد باربردار و هشتاد هزارنفر چوب بر در کوه بود.۱۵
16 ya kuma kasance da shugabanni dubu uku da ɗari uku waɗanda suke lura da aikin, su ne kuma suke bi da ma’aikatan.
سوای سروران گماشتگان سلیمان که ناظر کار بود، یعنی سه هزارو سیصد نفر که بر عاملان کار ضابط بودند.۱۶
17 Bisa ga umarnin sarki sai suka cire manyan duwatsu masu kyau don a tanada tushen duwatsun da aka gyara domin haikalin daga wurin haƙar duwatsun.
وپادشاه امر فرمود تا سنگهای بزرگ و سنگهای گرانبها و سنگهای تراشیده شده به جهت بنای خانه کندند.۱۷
18 Gwanayen Solomon da na Hiram da kuma mutanen Gebal, su suka yanka, suka kuma shirya katako da dutse don ginin haikali.
و بنایان سلیمان و بنایان حیرام وجبلیان آنها را تراشیدند، پس چوبها و سنگها را به جهت بنای خانه مهیا ساختند.۱۸

< 1 Sarakuna 5 >