< 1 Sarakuna 5 >

1 Sa’ad da Hiram sarkin Taya ya ji an shafe Solomon sarki yă gāji mahaifinsa Dawuda, sai ya aika da jakadunsa zuwa wurin Solomon, gama shi da Dawuda abokai ne sosai dukan kwanakinsa.
Hiram, roi de Tyr, envoya aussi ses serviteurs vers Salomon; car il apprit qu’on l’avait oint roi, en la place de son père, parce qu’Hiram avait toujours été l’ami de David.
2 Solomon ya mayar da wannan saƙo ga Hiram ya ce,
Or Salomon envoya vers Hiram, disant:
3 “Ka san cewa saboda yaƙe-yaƙen da abokan gāba suka yi da mahaifina a kowane gefe, ya sa bai iya gina haikali domin Sunan Ubangiji Allahnsa ba, sai da Ubangiji ya sa abokan gābansa a ƙarƙashin ƙafafunsa.
Vous savez le désir de David mon père, et qu’il n’a pu bâtir une maison au nom du Seigneur son Dieu, à cause des guerres qui le menaçaient de toutes parts, jusqu’à ce que le Seigneur eût mis ses ennemis sous la plante de ses pieds.
4 Amma yanzu Ubangiji Allahna ya ba ni hutu a kowane gefe, babu kuma gāba ko masifa.
Mais maintenant le Seigneur mon Dieu m’a donné la paix alentour; et il n’y a ni adversaire, ni obstacle fâcheux.
5 Ina niyya in gina haikali domin Sunan Ubangiji Allahna, yadda Ubangiji ya faɗa wa mahaifina Dawuda, sa’ad da ya ce, ‘Ɗanka wanda zai gāje ka, shi zai gina haikali domin Sunana.’
C’est pourquoi je pense à bâtir un temple au nom du Seigneur mon Dieu, comme a parlé le Seigneur à David, mon père, disant: Ton fils, que je mettrai en ta place sur ton trône, sera celui qui bâtira une maison à mon nom.
6 “Don haka, ka ba da umarni a yanka mini itatuwan al’ul na ƙasar Lebanon. Ma’aikatana za su haɗa hannu da ma’aikatanka, ni kuwa zan biya ka albashin ma’aikatanka kamar yadda ka faɗa. Gama ka san cewa babu wani a cikinmu da ya iya yanka itacen katako kamar Sidoniyawa.”
Ordonnez donc que vos serviteurs coupent pour moi des cèdres du Liban, et que mes serviteurs soient avec les vôtres; quant à la récompense de vos serviteurs, je vous la donnerai telle que vous la demanderez; car vous savez que parmi mon peuple, il n’est pas d’homme qui sache couper le bois comme les Sidoniens.
7 Da Hiram ya ji saƙon Solomon, sai ya ji daɗi ƙwarai, ya kuma ce, “Yabo ga Ubangiji a yau, gama ya ba wa Dawuda ɗa mai hikima yă yi mulki a bisa wannan al’umma mai girma.”
Lors donc qu’Hiram eut entendu les paroles de Salomon, il se réjouit beaucoup, et dit: Béni aujourd’hui le Seigneur Dieu, qui a donné à David un fils très sage pour gouverner ce très grand peuple!
8 Sai Hiram ya aike wa Solomon da kalmomin nan, “Na sami saƙon da ka aika mini, zan kuma yi duk abin da kake so ta wurin tanada katakan al’ul da na fir.
Et Hiram envoya vers Salomon, disant: J’ai entendu tout ce que vous m’avez mandé; je ferai tout ce que vous désirez pour les bois de cèdre et de sapin.
9 Ma’aikatana za su gangara da su daga Lebanon zuwa bakin teku. Zan sa a ɗaɗɗaura su su bi ruwan teku daga Lebanon zuwa bakin Bahar Rum da za ka nuna mini. A can zan kunce maka su, sa’an nan ka kwashe. Kai kuma za ka biya bukatata ta wurin tanadin abinci wa gidana.”
Mes serviteurs les porteront du Liban à la mer, et moi je les ferai mettre en radeaux sur la mer, jusqu’au lieu que vous m’aurez marqué; je les y ferai aborder; vous les enlèverez, et vous me fournirez tout ce qui me sera nécessaire pour nourrir ma maison.
10 A haka Hiram ya ci gaba da aika wa Solomon al’ul da kuma fir da yake bukata.
C’est pourquoi Hiram donnait à Salomon des bois de cèdre et de sapin, selon tous ses désirs.
11 Solomon kuma ya ba wa Hiram mudu gari dubu ashirin na alkama a matsayin abinci domin gidansa, ya ƙara da garwa dubu ashirin na tataccen man zaitun. Solomon ya ci gaba da yin haka ga Hiram, shekara-shekara.
Et Salomon fournissait à Hiram, pour nourrir sa maison, vingt mille cors de froment et vingt cors d’huile très pure: voilà ce que Salomon livrait chaque année à Hiram.
12 Ubangiji ya ba wa Solomon hikima, kamar yadda ya yi masa alkawari. Dangantakar zaman lafiya ta kasance tsakanin Hiram da Solomon, su biyun suka yi yarjejjeniya.
Le Seigneur donna aussi la sagesse à Salomon, comme il le lui avait dit: et il y avait paix entre Hiram et Salomon, et ils firent tous deux alliance.
13 Sarki Solomon ya ɗebi ma’aikata daga dukan Isra’ila, su dubu talatin.
Et le roi Salomon choisit des ouvriers de tout Israël, et la taxation était de trente mille hommes.
14 Ya riƙa aika su dubu goma-goma zuwa Lebanon kowane wata, saboda su yi wata ɗaya a Lebanon, watanni biyu kuma a gida. Adoniram ne ya lura da aikin gandun.
Et il les envoyait au Liban tour à tour, dix mille chaque mois, de sorte qu’ils étaient deux mois dans leurs maisons; et Adoniram était préposé à cette taxation.
15 Solomon ya kasance da’yan ɗauko guda dubu saba’in da masu yankan duwatsu guda dubu tamanin a cikin tuddai,
Salomon avait soixante-dix mille hommes qui portaient des fardeaux, et quatre-vingt mille qui taillaient des pierres sur la montagne,
16 ya kuma kasance da shugabanni dubu uku da ɗari uku waɗanda suke lura da aikin, su ne kuma suke bi da ma’aikatan.
Sans les préposés qui présidaient à chaque ouvrage, au nombre de trois mille trois cents, et qui donnaient les ordres au peuple et à ceux qui faisaient l’ouvrage.
17 Bisa ga umarnin sarki sai suka cire manyan duwatsu masu kyau don a tanada tushen duwatsun da aka gyara domin haikalin daga wurin haƙar duwatsun.
Et le roi leur ordonna de prendre de grandes pierres, des pierres de prix, pour les fondements du temple, et de les équarrir;
18 Gwanayen Solomon da na Hiram da kuma mutanen Gebal, su suka yanka, suka kuma shirya katako da dutse don ginin haikali.
Et les maçons de Salomon et les maçons d’Hiram les taillèrent; or ceux de Giblos préparèrent les bois et les pierres pour bâtir la maison du Seigneur.

< 1 Sarakuna 5 >