< 1 Sarakuna 5 >

1 Sa’ad da Hiram sarkin Taya ya ji an shafe Solomon sarki yă gāji mahaifinsa Dawuda, sai ya aika da jakadunsa zuwa wurin Solomon, gama shi da Dawuda abokai ne sosai dukan kwanakinsa.
And he sent Hiram [the] king of Tyre servants his to Solomon for he had heard that him people had anointed to king in place of father his for a friend he had been Hiram of David all the days.
2 Solomon ya mayar da wannan saƙo ga Hiram ya ce,
And he sent Solomon to Hiram saying.
3 “Ka san cewa saboda yaƙe-yaƙen da abokan gāba suka yi da mahaifina a kowane gefe, ya sa bai iya gina haikali domin Sunan Ubangiji Allahnsa ba, sai da Ubangiji ya sa abokan gābansa a ƙarƙashin ƙafafunsa.
You you know David father my that not he was able to build a house for [the] name of Yahweh God his because of the war which they had surrounded him until gave Yahweh them under [the] soles of (feet my. *Q(K)*)
4 Amma yanzu Ubangiji Allahna ya ba ni hutu a kowane gefe, babu kuma gāba ko masifa.
And now he has given rest Yahweh God my to me from round about there not [is] an adversary and there not [is] an occurrence evil.
5 Ina niyya in gina haikali domin Sunan Ubangiji Allahna, yadda Ubangiji ya faɗa wa mahaifina Dawuda, sa’ad da ya ce, ‘Ɗanka wanda zai gāje ka, shi zai gina haikali domin Sunana.’
And here I [am] saying to build a house for [the] name of Yahweh God my just as - he spoke Yahweh to David father my saying son your whom I will put in place of you on throne your he he will build the house for name my.
6 “Don haka, ka ba da umarni a yanka mini itatuwan al’ul na ƙasar Lebanon. Ma’aikatana za su haɗa hannu da ma’aikatanka, ni kuwa zan biya ka albashin ma’aikatanka kamar yadda ka faɗa. Gama ka san cewa babu wani a cikinmu da ya iya yanka itacen katako kamar Sidoniyawa.”
And therefore command so they may cut for me cedars from Lebanon and servants my they will be with servants your and [the] wage[s] of servants your I will give to you according to all that you will say for - you you know that there not among us [is] anyone [who] knows to cut wood like the Sidonians.
7 Da Hiram ya ji saƙon Solomon, sai ya ji daɗi ƙwarai, ya kuma ce, “Yabo ga Ubangiji a yau, gama ya ba wa Dawuda ɗa mai hikima yă yi mulki a bisa wannan al’umma mai girma.”
And it was when heard Hiram [the] words of Solomon and he rejoiced exceedingly and he said [be] blessed Yahweh this day who he has given to David a son wise over the people great this.
8 Sai Hiram ya aike wa Solomon da kalmomin nan, “Na sami saƙon da ka aika mini, zan kuma yi duk abin da kake so ta wurin tanada katakan al’ul da na fir.
And he sent Hiram to Solomon saying I have heard [that] which you sent to me I I will do all desire your in wood of cedar and in wood of cypress.
9 Ma’aikatana za su gangara da su daga Lebanon zuwa bakin teku. Zan sa a ɗaɗɗaura su su bi ruwan teku daga Lebanon zuwa bakin Bahar Rum da za ka nuna mini. A can zan kunce maka su, sa’an nan ka kwashe. Kai kuma za ka biya bukatata ta wurin tanadin abinci wa gidana.”
Servants my they will bring [them] down from Lebanon [the] sea towards and I I will make them rafts on the sea to the place which you will send to me and I will break up them there and you you will carry [them] away and you you will do desire my by giving [the] food of household my.
10 A haka Hiram ya ci gaba da aika wa Solomon al’ul da kuma fir da yake bukata.
And he was Hiram giving to Solomon wood of cedar and wood of cypress all desire his.
11 Solomon kuma ya ba wa Hiram mudu gari dubu ashirin na alkama a matsayin abinci domin gidansa, ya ƙara da garwa dubu ashirin na tataccen man zaitun. Solomon ya ci gaba da yin haka ga Hiram, shekara-shekara.
And Solomon he gave to Hiram twenty thousand cor[s] of wheat food for household his and twenty cor[s] of oil pressed thus he gave Solomon to Hiram a year in a year.
12 Ubangiji ya ba wa Solomon hikima, kamar yadda ya yi masa alkawari. Dangantakar zaman lafiya ta kasance tsakanin Hiram da Solomon, su biyun suka yi yarjejjeniya.
And Yahweh he gave wisdom to Solomon just as he had spoken to him and it was peace between Hiram and between Solomon and they made a covenant [the] two of them.
13 Sarki Solomon ya ɗebi ma’aikata daga dukan Isra’ila, su dubu talatin.
And he raised the king Solomon forced labor from all Israel and it was the forced labor thirty thousand man.
14 Ya riƙa aika su dubu goma-goma zuwa Lebanon kowane wata, saboda su yi wata ɗaya a Lebanon, watanni biyu kuma a gida. Adoniram ne ya lura da aikin gandun.
And he sent them Lebanon towards ten thousand in the month relays a month they were in Lebanon two months in home his and Adoniram [was] over the forced labor.
15 Solomon ya kasance da’yan ɗauko guda dubu saba’in da masu yankan duwatsu guda dubu tamanin a cikin tuddai,
And it belonged to Solomon seventy thousand carrier[s] burden-bearer[s] and eighty thousand stone-cutter[s] in the hill country.
16 ya kuma kasance da shugabanni dubu uku da ɗari uku waɗanda suke lura da aikin, su ne kuma suke bi da ma’aikatan.
Apart from [the] leaders of the overseers of Solomon who [were] over the work three thousand and three hundred who ruled over the people who were doing the work.
17 Bisa ga umarnin sarki sai suka cire manyan duwatsu masu kyau don a tanada tushen duwatsun da aka gyara domin haikalin daga wurin haƙar duwatsun.
And he commanded the king and they quarried stones large stones costly to found the house stones of hewn [stone].
18 Gwanayen Solomon da na Hiram da kuma mutanen Gebal, su suka yanka, suka kuma shirya katako da dutse don ginin haikali.
And they cut [them] to shape [the] builders of Solomon and [the] builders of Hiram and the Gebalites and they prepared the wood and the stones to build the house.

< 1 Sarakuna 5 >