< 1 Sarakuna 5 >
1 Sa’ad da Hiram sarkin Taya ya ji an shafe Solomon sarki yă gāji mahaifinsa Dawuda, sai ya aika da jakadunsa zuwa wurin Solomon, gama shi da Dawuda abokai ne sosai dukan kwanakinsa.
And Hiram the king of Tyre sent his servants unto Solomon; for he had heard that they had anointed him king in the room of his father; for Hiram had all the time been a lover of David.
2 Solomon ya mayar da wannan saƙo ga Hiram ya ce,
And Solomon sent to Hiram, saying,
3 “Ka san cewa saboda yaƙe-yaƙen da abokan gāba suka yi da mahaifina a kowane gefe, ya sa bai iya gina haikali domin Sunan Ubangiji Allahnsa ba, sai da Ubangiji ya sa abokan gābansa a ƙarƙashin ƙafafunsa.
Thou well knowest of David my father, that he was not able to build a house unto the name of the Lord his God, on account of the war wherewith his enemies encompassed him, until the Lord had put them under the soles of his feet.
4 Amma yanzu Ubangiji Allahna ya ba ni hutu a kowane gefe, babu kuma gāba ko masifa.
But now hath the Lord my God given me rest on every side, there is neither adversary nor evil hinderance.
5 Ina niyya in gina haikali domin Sunan Ubangiji Allahna, yadda Ubangiji ya faɗa wa mahaifina Dawuda, sa’ad da ya ce, ‘Ɗanka wanda zai gāje ka, shi zai gina haikali domin Sunana.’
And, behold, I purpose to build a house unto the name of the Lord my God, as the Lord hath spoken unto David my father, saying, Thy son, whom I will place in thy room upon thy throne, he it is that shall build the house unto my name.
6 “Don haka, ka ba da umarni a yanka mini itatuwan al’ul na ƙasar Lebanon. Ma’aikatana za su haɗa hannu da ma’aikatanka, ni kuwa zan biya ka albashin ma’aikatanka kamar yadda ka faɗa. Gama ka san cewa babu wani a cikinmu da ya iya yanka itacen katako kamar Sidoniyawa.”
And now command thou that they hew me cedar-trees out of Lebanon; and my servants shall be with thy servants; and the wages of thy servants will I give unto thee in accordance with all that thou wilt say; for thou well knowest that there is not among us a man that hath the skill to hew timber like unto the Zidonians.
7 Da Hiram ya ji saƙon Solomon, sai ya ji daɗi ƙwarai, ya kuma ce, “Yabo ga Ubangiji a yau, gama ya ba wa Dawuda ɗa mai hikima yă yi mulki a bisa wannan al’umma mai girma.”
And it came to pass, when Hiram heard the words of Solomon, that he rejoiced greatly; and he said, Blessed be the Lord this day, who hath given unto David a wise son over this numerous people.
8 Sai Hiram ya aike wa Solomon da kalmomin nan, “Na sami saƙon da ka aika mini, zan kuma yi duk abin da kake so ta wurin tanada katakan al’ul da na fir.
And Hiram sent to Solomon, saying, I have heard what thou hast sent to me for: I will gladly execute all thy desire in respect of timber of cedar, and in respect of timber of fir.
9 Ma’aikatana za su gangara da su daga Lebanon zuwa bakin teku. Zan sa a ɗaɗɗaura su su bi ruwan teku daga Lebanon zuwa bakin Bahar Rum da za ka nuna mini. A can zan kunce maka su, sa’an nan ka kwashe. Kai kuma za ka biya bukatata ta wurin tanadin abinci wa gidana.”
My servants shall bring them down from the Lebanon unto the sea: and I will convey them by sea in floats unto the place of which thou wilt send me word, and I will cause them to be taken apart there, and thou shalt take them away; and thou shalt accomplish my desire, in giving the food for my household.
10 A haka Hiram ya ci gaba da aika wa Solomon al’ul da kuma fir da yake bukata.
So Hiram gave Solomon cedar-trees and fir-trees, all his desire.
11 Solomon kuma ya ba wa Hiram mudu gari dubu ashirin na alkama a matsayin abinci domin gidansa, ya ƙara da garwa dubu ashirin na tataccen man zaitun. Solomon ya ci gaba da yin haka ga Hiram, shekara-shekara.
And Solomon gave Hiram twenty thousand kors of wheat as provision for his household, and twenty kors of beaten oil: thus did Solomon give to Hiram year by year.
12 Ubangiji ya ba wa Solomon hikima, kamar yadda ya yi masa alkawari. Dangantakar zaman lafiya ta kasance tsakanin Hiram da Solomon, su biyun suka yi yarjejjeniya.
And the Lord gave wisdom unto Solomon, as he had spoken to him; and there was peace between Hiram and Solomon; and they made a covenant with each other.
13 Sarki Solomon ya ɗebi ma’aikata daga dukan Isra’ila, su dubu talatin.
And king Solomon raised a levy out of all Israel; and the levy was thirty thousand men.
14 Ya riƙa aika su dubu goma-goma zuwa Lebanon kowane wata, saboda su yi wata ɗaya a Lebanon, watanni biyu kuma a gida. Adoniram ne ya lura da aikin gandun.
And he sent them into the Lebanon, ten thousand in each month by turns; one month they used to be in the Lebanon, two months at home: and Adoniram was over the levy.
15 Solomon ya kasance da’yan ɗauko guda dubu saba’in da masu yankan duwatsu guda dubu tamanin a cikin tuddai,
And there belonged to Solomon seventy thousand bearers of burdens, and eighty thousand stone-cutters in the mountains;
16 ya kuma kasance da shugabanni dubu uku da ɗari uku waɗanda suke lura da aikin, su ne kuma suke bi da ma’aikatan.
Besides the chiefs who were appointed by Solomon over the work, three thousand and three hundred, who ruled over the people that wrought on the work.
17 Bisa ga umarnin sarki sai suka cire manyan duwatsu masu kyau don a tanada tushen duwatsun da aka gyara domin haikalin daga wurin haƙar duwatsun.
And when the king commanded, they quarried out great stones, heavy stones, to lay the foundation of the house, and hewn stones.
18 Gwanayen Solomon da na Hiram da kuma mutanen Gebal, su suka yanka, suka kuma shirya katako da dutse don ginin haikali.
And the builders of Solomon, and the builders of Hiram, and the Giblites hewed them; and so they prepared the wood and the stones to build the house.