< 1 Sarakuna 4 >

1 Sai Sarki Solomon ya yi mulki a bisa dukan Isra’ila.
Now king Solomon was reigning over all of Israel.
2 Waɗannan su ne manyan shugabanninsa. Azariya ɗan Zadok shi ne firist;
And these were the leaders that he had: Azariah, the son of Zadok, the priest;
3 Elihoref da Ahiya,’ya’yan Shisha maza, su ne marubuta. Yehoshafat ɗan Ahilud, shi ne mai lura da takardu.
Elihoreph and Ahijah, the sons of Shisha, the scribes; Jehoshaphat, the son of Ahilud, the keeper of records;
4 Benahiya ɗan Yehohiyada, shi ne shugaban mayaƙa. Zadok da Abiyatar, su ne firistoci.
Benaiah, the son of Jehoiada, over the army; and Zadok, and Abiathar, priests;
5 Azariya ɗan Natan, shi ne mai lura da shugabannin yanki. Zabud ɗan Natan, shi ne firist da kuma mai wa sarki shawara.
Azariah, the son of Nathan, over those who were assisting the king; Zabud, the son of Nathan, the priest, the friend of the king;
6 Ahishar, shi ne sarkin fada. Adoniram ɗan Abda, shi ne mai lura da aikin gandu.
and Ahishar, first ruler of the house; and Adoniram, the son of Abda, over the tribute.
7 Solomon yana da gwamnoni yankuna goma sha biyu a bisa dukan Isra’ila, waɗanda suke tanaji abinci domin sarki da kuma gidan sarauta. Kowanne yakan tanada abinci na wata ɗaya a shekara.
And Solomon had twelve commanders over all of Israel, who offered yearly provisions for the king and his house. For each was ministering the necessities, by each month of the year.
8 Ga sunayensu, Ben-Hur, shi ne a ƙasar tudun Efraim;
And these are their names: Benhur, on mount Ephraim;
9 Ben-Deker, shi ne a Makaz, Sha’albim, Bet-Shemesh da Elon Bet-Hanan;
Bendeker, in Makaz, and in Shaalbim, and in Beth-shemesh, and in Elon, and in Beth-hanan;
10 Ben-Hesed, shi ne a Arubbot (Soko da dukan ƙasar Hefer);
Benhesed, in Arubboth: his was Socoh and the entire land of Hepher;
11 Ben-Abinadab, shi ne a Nafot Dor (ya auri Tafat’yar Solomon);
Benabinadab, to whom was all of Naphath-Dor, who had Taphath, the daughter of Solomon, as wife;
12 Ba’ana ɗan Ahilud, shi ne a Ta’anak da Megiddo, da kuma dukan Bet-Sheyan biye da Zaretan ƙasa da Yezireyel, daga Bet-Sheyan zuwa Abel-Mehola a ƙetaren Yokmeyam;
Baana, the son of Ahilud, who was reigning in Taanach, and Megiddo, and all of Bethshean, which is beside Zarethan and below Jezreel, from Bethshean as far as Abelmeholah, opposite Jokmeam;
13 Ben-Geber, shi ne a Ramot Gileyad (Mazaunan Yayir ɗan Manasse a Gileyad suna a ƙarƙashinsa, haka ma yankin Argob a Bashan tare da manyan biranen sittin masu katanga da suke da ƙyamare na tagulla);
Bengeber, in Ramoth Gilead, who had the town of Jair, the son of Manasseh, in Gilead; the same was first in the entire region of Argob, which is in Bashan, sixty great cities with walls that had bronze bars;
14 Ahinadab ɗan Iddo, shi ne a Mahanayim;
Ahinadab, the son of Iddo, who was first in Mahanaim;
15 Ahimawaz, shi ne a Naftali (ya auri Basemat’yar Solomon);
Ahimaaz, in Naphtali, and he also had Basemath, the daughter of Solomon, in marriage;
16 Ba’ana ɗan Hushai, shi ne a Asher da Bayelot;
Baana, the son of Hushai, in Asher and in Bealoth;
17 Yehoshafat ɗan Faruwa, shi ne a Issakar;
Jehoshaphat, the son of Paruah, in Issachar;
18 Shimeyi ɗan Ela, shi ne a Benyamin;
Shimei, the son of Ela, in Benjamin;
19 Geber ɗan Uri, shi ne a Gileyad (ƙasar Sihon sarkin Amoriyawa da kuma Og sarkin Bashan). Shi ne kaɗai gwamna a bisa yankin.
Geber, the son of Uri, in the land of Gilead, in the land of Sihon, king of the Amorites, and of Og, king of Bashan, over all who were in that land.
20 Mutanen Yahuda da na Isra’ila sun yi yawa sai ka ce yashi a bakin teku. Suka ci, suka sha, suka kuma yi farin ciki.
Judah and Israel were innumerable, like the sand of the sea in multitude: eating and drinking, and rejoicing.
21 Solomon kuwa ya yi mulki a bisa dukan masarautai daga Kogi zuwa ƙasar Filistiyawa, har zuwa iyakar Masar. Waɗannan ƙasashe sun yi ta kawo haraji, suka kuma zama bayin Solomon dukan kwanakin ransa.
Now Solomon had, in his dominion, all the kingdoms, from the river to the land of the Philistines, even to the border of Egypt. And they offered gifts to him, and they served him all the days of his life.
22 Tanajin Solomon na kowace rana su ne, garwa talatin na garin abinci,
And the provisions of Solomon, for each day, were thirty cor of fine wheat flour, and sixty cor of meal,
23 shanun da aka yi kiwo a gida guda goma, shanu ashirin da suka ƙoshi daga kiwo, tumaki da awaki ɗari; ban da ƙishimai, bareyi, batsiyoyi, da kaji masu ƙiba.
ten fattened oxen, and twenty oxen from the pastures, and one hundred rams, aside from the venison of stags, roe deer, and gazelles, and fattened poultry.
24 Gama ya yi mulki a bisa dukan masarautai yamma da Kogi, daga Tifsa zuwa Gaza, aka kuwa sami zaman lafiya a kowane gefe.
For he had obtained the entire region which was beyond the river, from Tiphsah as far as Gaza, and all the kings of those regions. And he had peace on every side all around.
25 A kwanakin da Solomon yake raye, Yahuda da Isra’ila, daga Dan zuwa Beyersheba, sun zauna lafiya, kowane mutum ya zauna a ƙarƙashin itacen inabi da na ɓaurensa.
And so, Judah and Israel were living without any fear, each one under his own vine and under his own fig tree, from Dan as far as Beersheba, during all the days of Solomon.
26 Solomon yana da rumfunan dawakai masu jan kekunan yaƙi, dubu huɗu, da kuma dawakai dubu goma sha biyu
And Solomon had forty thousand stalls of chariot horses, and twelve thousand riding horses.
27 Shugabannin yankuna, kowanne a watansa yakan yi tanajin abinci domin Sarki Solomon da kuma duk wanda ya zo teburin sarki. Sun tabbatar ba a rasa kome ba.
And the above-stated commanders of the king nourished these. And they also offered the necessities for the table of king Solomon, with immense diligence, each in his time.
28 Kowa a cikinsu, bisa ga lokacin da aka ba shi, yakan kai hatsin sha’ir da ciyawa domin dawakan-kekunan yaƙi, da sauran dawakai a inda aka ajiye su.
Also, they brought barley and straw for the horses and beasts of burden, to the place where the king was, just as it was appointed to them.
29 Allah ya ba Solomon hikima da hangen nesa mai girma, da kuma fāɗin fahimta marar iyaka, kamar yashi a bakin teku.
And God gave wisdom to Solomon, and an exceedingly great prudence, and a spacious heart, like the sand which is on the shore of the sea.
30 Hikimar Solomon ta fi hikimar mutanen Gabas, ta kuma fi dukan hikimar Masar girma.
And the wisdom of Solomon surpassed the wisdom of all the East, and of the Egyptians.
31 Ya fi kowane mutum hikima, har da Etan dangin Ezra ma. Yana da hikima fiye da Heman, Kalkol da Darda,’ya’yan Mahol maza. Sunansa ya bazu ko’ina a ƙasashen da suke kewaye.
And he was wiser than all men: wiser than Ethan, the Ezrahite, and Heman, and Calcol, and Darda, the sons of Mahol. And he was renowned in all the nations on every side.
32 Ya yi karin magana dubu uku. Waƙoƙinsa kuwa sun kai dubu ɗaya da biyar.
Solomon also spoke three thousand parables. And his verses were one thousand and five.
33 Ya yi magana a kan rayuwar itatuwa, daga al’ul na Lebanon zuwa hizzob da yake girma a bangaye. Ya kuma yi koyarwa game da dabbobi, da tsuntsaye, da abubuwa masu rarrafe, da kuma kifi.
And he discoursed about trees, from the cedar which is in Lebanon, to the hyssop which grows out from the wall. And he explained about beasts, and birds, and reptiles, and fish.
34 Mutane suka yi ta zuwa daga ƙasashe dabam-dabam don su ji hikimar Solomon. Sarakuna daga ko’ina a duniya, sun ji labarin hikimarsa, suka kuma aika da mutane don su ji shi.
And they came from all the peoples in order to hear the wisdom of Solomon, and from all the kings of the earth, who were hearing about his wisdom.

< 1 Sarakuna 4 >