< 1 Sarakuna 3 >

1 Solomon ya haɗa kai da Fir’auna sarkin Masar, ya kuwa auri’yarsa. Ya kawo ta cikin Birnin Dawuda kafin yă gama ginin fadarsa, da haikalin Ubangiji, da kuma katanga kewaye da Urushalima.
Or, Salomon s'allia avec Pharaon, roi d'Égypte; et il épousa la fille de Pharaon, qu'il amena dans la ville de David, jusqu'à ce qu'il eût achevé de bâtir sa maison et la maison de l'Éternel, ainsi que la muraille autour de Jérusalem.
2 A lokacin dai mutane suna miƙa hadaya a wurare a bisa tuddai, domin ba a riga an gina haikali saboda Sunan Ubangiji ba.
Le peuple sacrifiait seulement sur les hauts lieux, parce que jusqu'alors on n'avait pas bâti de maison au nom de l'Éternel.
3 Solomon ya ƙaunaci Ubangiji ta wurin yin tafiya bisa ga farillan mahaifinsa Dawuda, sai dai ya miƙa hadayu, ya kuma ƙone turare a wuraren nan na bisa tuddai.
Et Salomon aimait l'Éternel et suivait les ordonnances de David, son père; seulement il offrait les sacrifices et le parfum sur les hauts lieux.
4 Sai sarki Solomon ya tafi Gibeyon don yă miƙa hadayu, gama a can ne wuri mafi muhimmanci na sujada. Solomon kuwa ya miƙa hadayun ƙonawa guda dubu a kan wannan bagade.
Le roi s'en alla donc à Gabaon pour y sacrifier; car c'était le plus considérable des hauts lieux; et Salomon offrit mille holocaustes sur cet autel.
5 A Gibeyon, Ubangiji ya bayyana ga Solomon da dare a mafarki, Allah ya ce, “Ka roƙi abin da kake so in ba ka.”
A Gabaon, l'Éternel apparut en songe à Salomon, pendant la nuit, et Dieu lui dit: Demande ce que tu veux que je te donne.
6 Solomon ya amsa ya ce, “Ka nuna alheri mai girma ga bawanka, mahaifina Dawuda domin ya yi aminci gare ka da adalci, ya kuma kasance da zuciya mai gaskiya. Ka ci gaba da wannan alheri mai girma gare shi, ka ba shi ɗa don yă zauna a kujerar sarautarsa a wannan rana.
Et Salomon dit: Tu as usé d'une grande bienveillance envers ton serviteur David, mon père, selon qu'il a marché en ta présence dans la vérité, dans la justice et dans la droiture de son cœur devant toi; et tu lui as conservé cette grande bienveillance, et lui as donné un fils qui est assis sur son trône, comme il paraît aujourd'hui.
7 “Yanzu, ya Ubangiji Allahna, ka sa bawanka a wurin mahaifina Dawuda. Amma ni ɗan yaro ne kawai, ban kuma san yadda zan yi ayyukana ba.
Et maintenant, ô Éternel mon Dieu, tu as fait régner ton serviteur à la place de David, mon père; et moi je ne suis qu'un tout jeune homme; je ne sais pas me conduire.
8 Bawanka yana nan a cikin mutanen da ka zaɓa, mutane masu girma, waɗanda suka wuce ƙirge, ko a lissafta.
Et ton serviteur est au milieu du peuple que tu as choisi, ce grand peuple qui ne se peut dénombrer ni compter à cause de sa multitude.
9 Saboda haka ka ba bawanka zuciyar ganewa, don yă shugabanci mutanenka, yă kuma iya rarrabe tsakanin abin da yake daidai da abin da ba daidai ba. Gama wa zai iya shugabance wannan mutanenka masu girma haka?”
Donne donc à ton serviteur un cœur intelligent, pour juger ton peuple, et pour discerner entre le bien et le mal; car qui pourrait juger ton peuple, ce peuple si nombreux?
10 Sai Ubangiji ya ji daɗi cewa Solomon ya roƙa wannan.
Or ce discours plut au Seigneur, en ce que Salomon lui avait fait cette demande.
11 Saboda haka Allah ya ce masa, “Da yake ka nemi wannan ne, ba ka kuwa nemi tsawon rai ko arziki wa kanka ba, ba ka kuma nemi mutuwar abokan gābanka ba, amma ka nemi ganewa a aikata gaskiya,
Et Dieu lui dit: Puisque tu m'as fait cette demande, et que tu n'as demandé ni une longue vie, ni des richesses, ni la mort de tes ennemis, mais que tu as demandé de l'intelligence pour rendre la justice:
12 zan yi abin da ka roƙa. Zan ba ka zuciya mai hikima da ta ganewa, har yă zama ba a taɓa samun wani kamar ka ba, ba kuwa za a taɓa samunsa ba.
Voici, je fais selon ta parole. Je te donne un cœur sage et intelligent, de sorte qu'avant toi nul n'aura été pareil à toi, et qu'il n'y en aura point après toi qui te soit semblable.
13 Ban da haka ma, zan ba ka abin da ba ka nema ba; arziki da girma, don a rayuwarka ba za ka kasance da wani kamar ka ba a cikin sarakuna.
Et même, je te donne ce que tu n'as pas demandé, et les richesses et la gloire; de sorte qu'entre les rois il n'y en aura point de semblable à toi, pendant tous les jours de ta vie.
14 In kuma ka yi tafiya a hanyoyina, ka kuma yi biyayya da farillaina da umarnaina kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, zan ba ka tsawon rai.”
Et si tu marches dans mes voies, gardant mes statuts et mes ordonnances, comme y a marché David, ton père, je prolongerai tes jours.
15 Sai Solomon ya farka, ya gane ashe mafarki ne. Ya koma Urushalima, ya tsaya a gaban akwatin alkawarin Ubangiji ya miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama. Sa’an nan ya shirya wa fadawansa biki.
Alors Salomon se réveilla, et voici, c'était un songe. Puis il vint à Jérusalem, et se tint devant l'arche de l'alliance de l'Éternel; et il offrit des holocaustes et des sacrifices de prospérités, et fit un festin à tous ses serviteurs.
16 To, ana nan sai waɗansu karuwai biyu suka zo wurin sarki, suka tsaya a gabansa.
Alors deux femmes de mauvaise vie vinrent vers le roi, et se présentèrent devant lui.
17 Sai ɗaya ta ce, “Ranka yă daɗe, wannan mata da ni muna zama a gida ɗaya. Na haifi jariri yayinda take can tare da ni.
Et l'une de ces femmes dit: Ah! mon seigneur! nous demeurions, cette femme et moi, dans le même logis, et je suis accouchée près d'elle dans cette maison-là.
18 Kwana uku bayan haihuwar jaririna, wannan mata ma ta haifi jariri. Mu dai kaɗai ne; babu wani a gidan sai mu biyu.
Le troisième jour après mes couches, cette femme est aussi accouchée, et nous étions ensemble; personne d'autre n'était avec nous dans cette maison; il n'y avait que nous deux.
19 “Da dare ɗan wannan matan ya mutu domin ta kwanta a kansa.
Or le fils de cette femme est mort pendant la nuit, parce qu'elle s'était couchée sur lui.
20 Saboda haka ta tashi da tsakar dare ta ɗauki ɗana daga gefena yayinda baiwarka take barci. Sai ta sa shi kusa da ƙirjinta, ta kuma sa mataccen ɗanta kusa da ƙirjina.
Et elle s'est levée au milieu de la nuit, et a pris mon fils que j'avais près de moi, pendant que ta servante dormait; et elle l'a couché dans son sein, et elle a couché son fils mort dans mon sein.
21 Kashegari, da na farka don in shayar da ɗana, sai na tarar ya mutu! Amma sa’ad da na dube shi da kyau da safe, sai na ga ashe ba ɗan da na haifa ba ne.”
Puis, le matin, je me suis levée pour allaiter mon fils, et voici, il était mort; mais je l'ai considéré avec attention le matin, et voici, ce n'était pas mon fils que j'avais enfanté.
22 Amma ɗaya matar ta ce, “A’a! Mai rai ɗin ne ɗana; mataccen naki ne.” Amma ta farin ta nace, “A’a! Mataccen ne naki; mai ran ne nawa.” A haka suka yi ta gardama a gaban sarki.
Et l'autre femme répliqua: Non, celui qui vit est mon fils, et celui qui est mort est ton fils. Mais celle-là dit: Non, celui qui est mort est ton fils, et celui qui vit est mon fils. C'est ainsi qu'elles parlaient devant le roi.
23 Sarki ya ce, “Wannan ta ce, ‘Ɗana ne a raye, naki ne matacce,’ yayinda ɗayan tana cewa, ‘A’a! Ɗanki ne mataccen, nawa ne a raye.’”
Et le roi dit: L'une dit: C'est mon fils qui est vivant, et ton fils qui est mort; et l'autre dit: Non; mais c'est ton fils qui est mort, et celui qui vit est mon fils.
24 Sai sarki ya ce, “Kawo mini takobi.” Sai aka kawo takobi wa sarki.
Et le roi dit: Apportez-moi une épée! Et on apporta une épée devant le roi.
25 Ya ba da umarni ya ce, “Yanka yaron nan mai rai, gida biyu, kowacce ta ɗauki rabi.”
Puis le roi dit: Partagez en deux l'enfant qui vit, et donnez-en la moitié à l'une et la moitié à l'autre.
26 Ainihin mamar ɗan da yake a raye ta cika da tausayi saboda ɗanta, sai ta ce wa sarki, “Ina roƙonka, ranka yă daɗe, kada ka kashe yaron! Ka ba ta kawai!” Amma ɗayan matar ta ce, “Kada a ba kowa daga cikinmu ɗan da rai, a ci gaba a raba shi!”
Alors la femme dont le fils vivait, dit au roi (car ses entrailles furent émues au sujet de son fils): Ah! mon seigneur! donnez-lui l'enfant qui vit, et qu'on se garde bien de le faire mourir! tandis que l'autre disait: Il ne sera ni à moi ni à toi; partagez-le!
27 Sai sarki ya zartar da hukuncinsa ya ce, “A ba da jariri mai ran ga mata ta fari. Kada a kashe shi; ita ce ainihin mahaifiyarsa.”
Alors le roi répondit, et dit: Donnez à celle-là l'enfant qui vit, et gardez-vous de le faire mourir: c'est elle qui est la mère.
28 Sa’ad da dukan Isra’ila suka ji hukuncin da sarki ya zartar, suka girmama sarki sosai, domin sun gane cewa Allah ya ba shi hikimar yin shari’ar adalci.
Et tout Israël, ayant su le jugement que le roi avait prononcé, craignit le roi; car on vit qu'il y avait en lui une sagesse divine pour rendre la justice.

< 1 Sarakuna 3 >