< 1 Sarakuna 3 >
1 Solomon ya haɗa kai da Fir’auna sarkin Masar, ya kuwa auri’yarsa. Ya kawo ta cikin Birnin Dawuda kafin yă gama ginin fadarsa, da haikalin Ubangiji, da kuma katanga kewaye da Urushalima.
And he became son-in-law Solomon with Pharaoh [the] king of Egypt and he took [the] daughter of Pharaoh and he brought her to [the] city of David until finished he to build house his and [the] house of Yahweh and [the] wall of Jerusalem all around.
2 A lokacin dai mutane suna miƙa hadaya a wurare a bisa tuddai, domin ba a riga an gina haikali saboda Sunan Ubangiji ba.
Only the people [were] sacrificing at the high places for not it had been built a house for [the] name of Yahweh until the days those.
3 Solomon ya ƙaunaci Ubangiji ta wurin yin tafiya bisa ga farillan mahaifinsa Dawuda, sai dai ya miƙa hadayu, ya kuma ƙone turare a wuraren nan na bisa tuddai.
And he loved Solomon Yahweh to walk in [the] statutes of David father his only at the high places he [was] sacrificing and making smoke.
4 Sai sarki Solomon ya tafi Gibeyon don yă miƙa hadayu, gama a can ne wuri mafi muhimmanci na sujada. Solomon kuwa ya miƙa hadayun ƙonawa guda dubu a kan wannan bagade.
And he went the king Gibeon towards to sacrifice there for that [was] the high place great a thousand burnt offerings he offered up Solomon on the altar that.
5 A Gibeyon, Ubangiji ya bayyana ga Solomon da dare a mafarki, Allah ya ce, “Ka roƙi abin da kake so in ba ka.”
At Gibeon he appeared Yahweh to Solomon in a dream the night and he said God ask what? will I give to you.
6 Solomon ya amsa ya ce, “Ka nuna alheri mai girma ga bawanka, mahaifina Dawuda domin ya yi aminci gare ka da adalci, ya kuma kasance da zuciya mai gaskiya. Ka ci gaba da wannan alheri mai girma gare shi, ka ba shi ɗa don yă zauna a kujerar sarautarsa a wannan rana.
And he said Solomon you you have done with servant your David father my covenant loyalty great just as he walked before you in faithfulness and in righteousness and in uprightness of heart with you and you have kept to him the covenant loyalty great this and you have given to him a son [who] sits on throne his as the day this.
7 “Yanzu, ya Ubangiji Allahna, ka sa bawanka a wurin mahaifina Dawuda. Amma ni ɗan yaro ne kawai, ban kuma san yadda zan yi ayyukana ba.
And now O Yahweh God my you you have made king servant your in place of David father my and I [am] a lad young not I know to go out and to come.
8 Bawanka yana nan a cikin mutanen da ka zaɓa, mutane masu girma, waɗanda suka wuce ƙirge, ko a lissafta.
And servant your [is] in among people your which you have chosen a people numerous which not it will be numbered and not it will be counted from multitude.
9 Saboda haka ka ba bawanka zuciyar ganewa, don yă shugabanci mutanenka, yă kuma iya rarrabe tsakanin abin da yake daidai da abin da ba daidai ba. Gama wa zai iya shugabance wannan mutanenka masu girma haka?”
And you will give to servant your a heart [which] listens to judge people your to distinguish between good and evil for who? is he able to judge people your massive this.
10 Sai Ubangiji ya ji daɗi cewa Solomon ya roƙa wannan.
And it was good the thing in [the] eyes of [the] Lord that he had asked Solomon the thing this.
11 Saboda haka Allah ya ce masa, “Da yake ka nemi wannan ne, ba ka kuwa nemi tsawon rai ko arziki wa kanka ba, ba ka kuma nemi mutuwar abokan gābanka ba, amma ka nemi ganewa a aikata gaskiya,
And he said God to him because that you asked the thing this and not you asked for yourself days many and not you asked for yourself wealth and not you asked [the] life of enemies your and you asked for yourself to understand to hear judgment.
12 zan yi abin da ka roƙa. Zan ba ka zuciya mai hikima da ta ganewa, har yă zama ba a taɓa samun wani kamar ka ba, ba kuwa za a taɓa samunsa ba.
Here! I do according to words your here! - I give to you a heart wise and understanding that like you not anyone has been before you and after you not anyone will arise like you.
13 Ban da haka ma, zan ba ka abin da ba ka nema ba; arziki da girma, don a rayuwarka ba za ka kasance da wani kamar ka ba a cikin sarakuna.
And also [that] which not you asked for I give to you both wealth as well as honor that not he has been like you anyone among the kings all days your.
14 In kuma ka yi tafiya a hanyoyina, ka kuma yi biyayya da farillaina da umarnaina kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, zan ba ka tsawon rai.”
And if - you will walk in ways my to keep statutes my and commandments my just as he walked David father your and I will make long days your.
15 Sai Solomon ya farka, ya gane ashe mafarki ne. Ya koma Urushalima, ya tsaya a gaban akwatin alkawarin Ubangiji ya miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama. Sa’an nan ya shirya wa fadawansa biki.
And he awoke Solomon and there! [it was] a dream and he went Jerusalem and he stood - before - [the] ark of [the] covenant of [the] Lord and he offered up burnt offerings and he made peace offerings and he made a feast for all servants his.
16 To, ana nan sai waɗansu karuwai biyu suka zo wurin sarki, suka tsaya a gabansa.
Then they came two women prostitutes to the king and they stood before him.
17 Sai ɗaya ta ce, “Ranka yă daɗe, wannan mata da ni muna zama a gida ɗaya. Na haifi jariri yayinda take can tare da ni.
And she said the woman one pardon me O lord my I and the woman this [are] dwelling in a house one and I gave birth with her in the house.
18 Kwana uku bayan haihuwar jaririna, wannan mata ma ta haifi jariri. Mu dai kaɗai ne; babu wani a gidan sai mu biyu.
And it was on the day third of giving birth my and she gave birth also the woman this and we [were] together there not [was] a stranger with us in the house except two we [were] in the house.
19 “Da dare ɗan wannan matan ya mutu domin ta kwanta a kansa.
And he died [the] son of the woman this night that she lay on him.
20 Saboda haka ta tashi da tsakar dare ta ɗauki ɗana daga gefena yayinda baiwarka take barci. Sai ta sa shi kusa da ƙirjinta, ta kuma sa mataccen ɗanta kusa da ƙirjina.
And she rose in [the] middle of the night and she took son my from beside me and maidservant your [was] sleeping and she made lie him in bosom her and son her dead she made lie in bosom my.
21 Kashegari, da na farka don in shayar da ɗana, sai na tarar ya mutu! Amma sa’ad da na dube shi da kyau da safe, sai na ga ashe ba ɗan da na haifa ba ne.”
And I rose in the morning to suckle son my and there! he had died and I looked carefully to him in the morning and there! not it was son my whom I had borne.
22 Amma ɗaya matar ta ce, “A’a! Mai rai ɗin ne ɗana; mataccen naki ne.” Amma ta farin ta nace, “A’a! Mataccen ne naki; mai ran ne nawa.” A haka suka yi ta gardama a gaban sarki.
And she said the woman other In-deed [is] son my the living one and [is] son your the dead [one] and this [one] [was] saying In-deed [is] son your the dead [one] and [is] son my the living one and they spoke before the king.
23 Sarki ya ce, “Wannan ta ce, ‘Ɗana ne a raye, naki ne matacce,’ yayinda ɗayan tana cewa, ‘A’a! Ɗanki ne mataccen, nawa ne a raye.’”
And he said the king this [one] [is] saying this son my [is] the living one and son your [is] the dead [one] and this [one] [is] saying In-deed son your [is] the dead [one] and son my [is] the living one.
24 Sai sarki ya ce, “Kawo mini takobi.” Sai aka kawo takobi wa sarki.
And he said the king take for me a sword and they brought the sword before the king.
25 Ya ba da umarni ya ce, “Yanka yaron nan mai rai, gida biyu, kowacce ta ɗauki rabi.”
And he said the king cut the child living into two and give half to one and half to one.
26 Ainihin mamar ɗan da yake a raye ta cika da tausayi saboda ɗanta, sai ta ce wa sarki, “Ina roƙonka, ranka yă daɗe, kada ka kashe yaron! Ka ba ta kawai!” Amma ɗayan matar ta ce, “Kada a ba kowa daga cikinmu ɗan da rai, a ci gaba a raba shi!”
And she said the woman whom [was] son her the living one to the king for they had grown warm compassion her on son her and she said - pardon me O lord my give to her the child living and certainly may not you kill him and this [one] [was] saying neither to me nor to you not he will belong cut.
27 Sai sarki ya zartar da hukuncinsa ya ce, “A ba da jariri mai ran ga mata ta fari. Kada a kashe shi; ita ce ainihin mahaifiyarsa.”
And he answered the king and he said give to her the child living and certainly not you must kill him she [is] mother his.
28 Sa’ad da dukan Isra’ila suka ji hukuncin da sarki ya zartar, suka girmama sarki sosai, domin sun gane cewa Allah ya ba shi hikimar yin shari’ar adalci.
And they heard all Israel the judgment which he had judged the king and they were afraid of the king for they saw that [the] wisdom of God [was] within him to do justice.