< 1 Sarakuna 22 >

1 Aka yi shekaru uku ba a yi yaƙi tsakanin Aram da Isra’ila ba.
Och de sutto i ro i tre år, under vilka intet krig var mellan Aram och Israel.
2 Amma a shekara ta uku, Yehoshafat sarkin Yahuda ya gangara don yă ga sarki Isra’ila.
Men i det tredje året for Josafat, Juda konung, ned till Israels konung.
3 Sarkin Isra’ila ya ce wa shugabanninsa, “Ba ku san cewa Ramot Gileyad namu ne ba, duk da haka ba mu yi kome ba don mu sāke karɓanta daga sarkin Aram?”
Och Israels konung sade till sina tjänare: "I veten ju att Ramot i Gilead tillhör oss. Och likväl sitta vi stilla och taga det icke ifrån konungen i Aram."
4 Saboda haka ya tambayi Yehoshafat, ya ce, “Za ka tafi tare da ni don in yi yaƙi da Ramot Gileyad?” Yehoshafat ya amsa wa sarkin Isra’ila, ya ce, “Ni ma kamar ka ne, mutanena kuwa kamar mutanenka, dawakaina kamar dawakanka.”
Och han frågade Josafat: Vill du draga med mig för att belägra Ramot i Gilead?" Josafat svarade Israels konung: "Jag såsom du, mitt folk såsom ditt folk, mina hästar såsom dina hästar!"
5 Amma Yehoshafat ya ce wa sarkin Isra’ila, “Da farko mu nemi nufin Ubangiji.”
Men Josafat sade ytterligare till Israels konung: "Fråga dock först HERREN härom."
6 Saboda haka sarkin Isra’ila ya tattara annabawa, kamar ɗari huɗu, ya tambaye su, “In kai yaƙi a kan Ramot Gileyad, ko kada in kai?” Suka amsa, “Ka tafi, gama Ubangiji zai ba ka ita a hannunka.”
Då församlade Israels konung profeterna, vid pass fyra hundra män, och frågade dem: "Skall jag draga åstad mot Ramot i Gilead för att belägra det, eller skall jag avstå därifrån?" De svarade: "Drag ditupp; Herren skall giva det i konungens hand."
7 Amma Yehoshafat ya yi tambaya, ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu tambaya?”
Men Josafat sade: "Finnes här ingen annan HERRENS profet, så att vi kunna fråga genom honom?"
8 Sarkin Isra’ila ya amsa wa Yehoshafat, ya ce, “Akwai mutum guda har yanzu wanda ta wurinsa za mu iya nemi nufin Ubangiji, amma na ƙi jininsa domin bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni ba, sai dai mummuna kullum. Shi ne Mikahiya ɗan Imla.” Yehoshafat ya ce, “Kada sarki ya ce haka.”
Israels konung svarade Josafat: "Här finnes ännu en man, Mika, Jimlas son, genom vilken vi kunna fråga HERREN; men han är mig förhatlig, ty han profeterar aldrig lycka åt mig, utan allenast olycka." Josafat sade: "Konungen säge icke så."
9 Saboda haka sarkin Isra’ila ya kira ɗaya daga cikin shugabanninsa ya ce, “Kawo Mikahiya ɗan Imla nan take.”
Då kallade Israels konung till sig en hovman och sade: "Skaffa skyndsamt hit Mika, Jimlas son."
10 Saye da rigunansu na sarauta, sarkin Isra’ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suna zama a kujerun sarautarsu a masussuka ta mashigin ƙofar Samariya, tare da dukan annabawa suna ta annabci a gabansu.
Israels konung och Josafat, Juda konung, sutto nu var och en på sin tron, iklädda sina skrudar, på en tröskplats vid Samarias port, under det att alla profeterna profeterade inför dem.
11 Zedekiya ɗan Kena’ana kuwa ya yi ƙahonin ƙarfe ya kuma furta, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Da waɗannan za ka tunkuyi Arameyawa har su hallaka.’”
Då gjorde sig Sidkia, Kenaanas son, horn av järn och sade: "Så säger HERREN: Med dessa skall du stånga araméerna, så att de förgöras."
12 Dukan sauran annabawan suka yi annabci iri abu ɗaya. Suka ce, “Ka yaƙi Ramot Gileyad, ka kuma yi nasara, gama Ubangiji zai ba da ita cikin hannun sarki.”
Och alla profeterna profeterade på samma sätt och sade: "Drag upp mot Ramot i Gilead, så skall du bliva lyckosam; HERREN skall giva det i konungens hand."
13 Ɗan aikan da ya je yă kawo Mikahiya, ya ce masa, “Duba, sauran annabawa suna maganar nasara wa sarki, sai ka ce mutum guda. Bari maganarka tă yarda da tasu, ka kuma yi maganar alheri.”
Och budet som hade gått för att tillkalla Mika talade till honom och sade: "Det är så, att profeterna med en mun lova konungen lycka; låt nu dina ord stämma överens med vad de hava talat, och lova också du lycka."
14 Amma Mikahiya ya ce, “Na rantse da Ubangiji mai rai, zan faɗa masa kawai abin da Ubangiji ya faɗa mini.”
Men Mika svarade: "Så sant HERREN lever, jag skall allenast tala det som HERREN säger till mig."
15 Da suka kai, sai sarki ya tambaye shi, ya ce, “Mikahiya, mu kai yaƙi a kan Ramot Gileyad, ko kada mu kai?” Ya amsa ya ce, “Yaƙe ta, za ka kuwa yi nasara, gama Ubangiji zai ba da ita cikin hannun sarki.”
När han sedan kom till konungen, frågade konungen honom: "Mika, skola vi draga åstad till Ramot i Gilead för att belägra det, eller skola vi avstå därifrån?" Han svarade honom: "Drag ditupp, så skall du bliva lyckosam; HERREN skall giva det i konungens hand."
16 Sai sarki ya ce masa, “Sau nawa ne zan sa ka rantse cewa ba za ka faɗa mini kome ba sai dai gaskiya a cikin sunan Ubangiji?”
Men konungen sade till honom: "Huru många gånger skall jag besvärja dig att icke tala till mig annat än sanning i HERRENS namn?"
17 Sa’an nan Mikahiya ya amsa, “Na ga dukan Isra’ila a warwatse a kan tuddai kamar tumakin da ba su da makiyayi, kuma Ubangiji ya ce, ‘Waɗannan mutane ba su da maigida. Bari kowa yă tafi gida cikin salama.’”
Då sade han: "Jag såg hela Israel förskingrat på bergen, likt får som icke hava någon herde. Och HERREN sade: 'Dessa hava icke någon herre; må de vända tillbaka hem i frid, var och en till sitt.'"
18 Sai sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Ban faɗa maka cewa bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni, sai mummuna kawai ba?”
Då sade Israels konung till Josafat: "Sade jag dig icke att denne aldrig profeterar lycka åt mig, utan allenast olycka?"
19 Mikahiya ya ci gaba, “Saboda haka ka ji maganar Ubangiji. I, na ga Ubangiji zaune a kursiyinsa tare da dukan rundunar sama tsaye kewaye da shi a dama da hagunsa.
Men han sade: "Hör alltså HERRENS ord. Jag såg HERREN sitta på sin tron och himmelens hela härskara stå där hos honom, på hans högra sida och på hans vänstra.
20 Kuma Ubangiji ya ce, ‘Wa zai ruɗi Ahab zuwa yaƙi da Ramot Gileyad, yă kuma kai shi mutuwarsa a can?’ “Wani ya ce wannan, wani ya ce wancan.
Och HERREN sade: 'Vem vill locka Ahab att draga upp mot Ramot i Gilead, för att han må falla där?' Då sade den ene så och den andre så.
21 A ƙarshe, wani ruhu ya zo gaba, ya tsaya a gaban Ubangiji ya ce, ‘Zan ruɗe shi.’
Slutligen kom anden fram och ställde sig inför HERREN och sade: 'Jag vill locka honom därtill.' HERREN frågade honom: 'På vad sätt?'
22 “Ubangiji ya yi tambaya ‘Ta wace hanya?’ Ya ce, “‘Zan tafi in zama ruhun ƙarya a bakunan dukan annabawansa.’ “Ubangiji ya ce, ‘Za ka yi nasara a ruɗinsa. Ka tafi, ka yi haka.’
Han svarade: 'Jag vill gå ut och bliva en lögnens ande i alla hans profeters mun.' Då sade han: 'Du må försöka att locka honom därtill, och du skall också lyckas; gå ut och gör så.'
23 “Saboda haka yanzu Ubangiji ya sa ruhun ƙarya a bakunan dukan annabawanka. Ubangiji ya zartar maka da masifa.”
Och se, nu har HERREN lagt en lögnens ande i alla dessa dina profeters mun, medan HERREN ändå har beslutit att olycka skall komma över dig."
24 Sai Zedekiya ɗan Kena’ana ya hau ya mari Mikahiya a fuska. Ya yi tambaya, “A wace hanya ce ruhu daga Ubangiji ya bar ni ya yi maka magana?”
Då trädde Sidkia, Kenaanas son, fram och gav Mika ett slag på kinden och sade: "På vilken väg har då HERRENS Ande gått bort ifrån mig för att tala med dig?"
25 Mikahiya ya amsa, “Za ka gane a ranar da ka je ka ɓuya a ciki cikin ɗaki.”
Mika svarade: "Du skall få se det på den dag då du nödgas springa från kammare till kammare för att gömma dig."
26 Sa’an nan sarkin Isra’ila ya umarta, “Ku kama Mikahiya, ku kai shi wurin Amon, shugaban birnin, da wurin Yowash ɗan sarki.
Men Israels konung sade: "Tag Mika och för honom tillbaka till Amon, hövitsmannen i staden, och till Joas, konungasonen.
27 Ku ce ga abin da sarki ya ce, ‘Ku sa wannan mutum a kurkuku, kuma kada ku ba shi wani abu sai dai burodi da ruwa, sai na dawo lafiya.’”
Och säg: Så säger konungen: Sätten denne i fängelse och bespisen honom med fångkost, till dess jag kommer välbehållen hem."
28 Mikahiya ya furta, “Idan har ka dawo lafiya, to, Ubangiji bai yi magana ta wurina ba.” Ya kuma ƙara da cewa, “Ku lura da maganata, dukanku mutane!”
Mika svarade: "Om du kommer välbehållen tillbaka, så har HERREN icke talat genom mig." Och han sade ytterligare: "Hören detta, I folk, allasammans."
29 Sai sarkin Isra’ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suka haura zuwa Ramot Gileyad.
Så drog nu Israels konung jämte Josafat, Juda konung, upp till Ramot i Gilead.
30 Sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Zan ɓad da kama in shiga wurin yaƙi, amma ka sa kayan sarautarka.” Saboda haka sarkin Isra’ila ya ɓad da kama, ya shiga cikin yaƙi.
Och Israels konung sade till Josafat: "Jag vill förkläda mig, när jag drager ut i striden, men du må vara klädd i dina egna kläder." Så förklädde sig Israels konung, när han drog ut i striden.
31 Sarkin Aram kuwa ya umarci shugabanni kekunan yaƙinsa talatin da biyu, ya ce, “Kada ku yaƙe kowa, ƙarami ko babba, sai dai sarkin Isra’ila.”
Men konungen i Aram hade bjudit och sagt till sina trettiotvå vagnshövitsmän: "I skolen icke giva eder i strid med någon, vare sig liten eller stor, utom med Israels konung allena."
32 Sa’ad da shugabannin kekunan yaƙin suka ga Yehoshafat, suka yi tsammani, suka ce, “Tabbatacce wannan shi ne sarkin Isra’ila.” Saboda haka suka juye don su yaƙe shi, amma sa’ad da Yehoshafat ya yi ihu,
När då hövitsmännen över vagnarna fingo se Josafat, tänkte de: "Förvisso är detta Israels konung", och vände sig därför till anfall mot honom. Då gav Josafat upp ett rop.
33 sai shugabannin kekunan yaƙin suka ga ashe ba sarkin Isra’ila ba ne, sai suka daina binsa.
Så snart nu hövitsmännen över vagnarna märkte att det icke var Israels konung, vände de om och läto honom vara.
34 Amma wani ya ja bakansa kawai ya bugi Ahab sarkin Isra’ila a tsakanin sassan kayan yaƙinsa. Sai sarki ya ce wa mahayin keken yaƙinsa, “Juye, ka fitar da ni daga yaƙin. An ji mini rauni.”
Men en man som spände sin båge och sköt på måfå träffade Israels konung i en fog på rustningen. Då sade denne till sin körsven: "Sväng om vagnen och för mig ut ur hären, ty jag är sårad."
35 Dukan yini aka yi ta yaƙi, aka kuma riƙe sarki a keken yaƙinsa yana fuskanci Arameyawa. Jini daga mikinsa ya yi ta zuba a ƙasan keken yaƙin, a wannan yamma kuwa ya mutu.
Och striden blev på den dagen allt häftigare, och konungen stod upprätt i sin vagn, vänd mot araméerna; men om aftonen gav han upp andan. Och blodet från såret hade runnit ned i vagnen.
36 Da rana tana fāɗuwa, sai kuka ta bazu cikin mayaƙa, “Kowane mutum ya tafi garinsu; kowa ya tafi ƙasarsa!”
Och vid solnedgången gick ett rop genom hären: "Var och en till sin stad igen! Var och en till sitt land igen!"
37 Sai sarki ya mutu, aka kuwa kawo shi Samariya, aka binne shi a can.
Så dödades då konungen och blev förd till Samaria; och man begrov konungen där i Samaria.
38 Suka wanke keken yaƙi a tafki, a Samariya (inda karuwai suke wanka), sai karnuka suka lashe jininsa, kamar yadda maganar Ubangiji ta furta.
Och när man sköljde vagnen i dammen i Samaria, slickade hundarna hans blod, och skökorna badade sig däri -- såsom HERREN hade sagt.
39 Game da sauran ayyukan mulkin Ahab, haɗe da dukan abin da ya yi, da fadan da ya gina ya kuma shimfiɗa da hauren giwa, da biranen da ya gina, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Vad nu mer är att säga om Ahab och om allt vad han gjorde, om elfenbenshuset som han byggde, och om alla de städer som han byggde, det finnes upptecknat i Israels konungars krönika.
40 Ahab ya huta da kakanninsa. Ahaziya ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Och Ahab gick till vila hos sina fäder. Och hans son Ahasja blev konung efter honom.
41 Yehoshafat ɗan Asa ya zama sarkin Yahuda a shekara ta huɗu ta Ahab sarkin Isra’ila.
Men Josafat, Asas sons blev konung över Juda i Ahabs, Israels konungs, fjärde regeringsår.
42 Yehoshafat yana da shekara talatin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru ashirin da biyar. Sunan mahaifiyarsa, Azuba’yar Shilhi.
Trettiofem år gammal var Josafat, när han blev konung, och han regerade tjugufem år i Jerusalem. Hans moder hette Asuba, Silhis dotter.
43 A cikin kome ya yi tafiya a hanyoyin mahaifinsa Asa, bai kuma kauce daga gare su ba; ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji. Amma bai rurrushe masujadai da suke kan tuddai ba, mutane kuwa suka ci gaba da miƙa hadayu suna kuma ƙone turare a can.
Och han vandrade i allt på sin fader Asas väg, utan att vika av ifrån den; han gjorde nämligen vad rätt var i HERRENS ögon. Dock blevo offerhöjderna icke avskaffade, utan folket fortfor att frambära offer och tända offereld på höjderna.
44 Yehoshafat kuma ya zauna lafiya da sarkin Isra’ila.
Och Josafat höll fred med Israels konung.
45 Game da sauran ayyukan mulkin Yehoshafat da abubuwan da ya yi, da kuma yaƙe-yaƙensa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Vad nu mer är att säga om Josafat och om de bedrifter han utförde och om hans krig, det finnes upptecknat i Juda konungars krönika.
46 Ya kawar da karuwai maza na masujadai da suke kan tuddai waɗanda suka rage tun mulkin mahaifinsa Asa.
Han utrotade ock ur landet de tempelbolare som ännu funnos där, vilka hade lämnats kvar i hans fader Asas tid.
47 Babu sarki a lokacin Edom, saboda haka sai mataimaki ya yi mulki.
I Edom fanns då ingen konung, utan en ståthållare regerade där.
48 To, Yehoshafat ya gina jerin jiragen ruwan kasuwanci don su je Ofir saboda zinariya, amma ba su yi tafiya ba, gama sun farfashe a Eziyon Geber.
Och Josafat hade låtit bygga Tarsis-skepp, som skulle gå till Ofir för att hämta guld; men de kommo aldrig åstad, ty de ledo skeppsbrott vid Esjon-Geber.
49 A lokacin Ahaziya ɗan Ahab ya ce wa Yehoshafat, “Bari mutanena su tafi tare da mutanenka,” amma Yehoshafat ya ƙi.
Då sade Ahasja, Ahabs son, till Josafat: "Låt mitt folk fara med ditt folk på skeppen." Men Josafat ville icke.
50 Yehoshafat kuwa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a birnin Dawuda kakansa. Sai Yehoram ɗansa ya gāje shi.
Och Josafat gick till vila hos sina fäder och blev begraven hos sina fäder i sin fader Davids stad. Och hans son Joram blev konung efter honom.
51 Ahaziya ɗan Ahab ya zama sarkin Isra’ila a Samariya a shekara ta goma sha bakwai ta Yehoshafat sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila shekaru biyu.
Ahasja, Ahabs son, blev konung över Israel i Samaria i Josafats, Juda konungs, sjuttonde regeringsår, och han regerade över Israel i två år.
52 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, domin ya yi tafiya a hanyoyin mahaifinsa da na mahaifiyarsa, da kuma a hanyoyin Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila suka yi zunubi.
Han gjorde vad ont var i HERRENS ögon och vandrade på sin faders och sin moders väg och på Jerobeams, Nebats sons, väg, hans som hade kommit Israel att synda.
53 Ya bauta, ya kuma yi wa Ba’al sujada, ya tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila yă yi fushi, kamar yadda mahaifinsa ya yi.
Och han tjänade Baal och tillbad honom och förtörnade HERREN, Israels Gud, alldeles såsom hans fader hade gjort.

< 1 Sarakuna 22 >