< 1 Sarakuna 22 >

1 Aka yi shekaru uku ba a yi yaƙi tsakanin Aram da Isra’ila ba.
Trois ans se passèrent donc sans guerre entre la Syrie et Israël.
2 Amma a shekara ta uku, Yehoshafat sarkin Yahuda ya gangara don yă ga sarki Isra’ila.
Mais, en la troisième année, Josaphat, roi de Juda, descendit vers le roi d’Israël.
3 Sarkin Isra’ila ya ce wa shugabanninsa, “Ba ku san cewa Ramot Gileyad namu ne ba, duk da haka ba mu yi kome ba don mu sāke karɓanta daga sarkin Aram?”
(Et le roi d’Israël dit à ses serviteurs: Ignorez-vous que la ville de Ramoth en Galaad est à nous, et nous négligeons de l’enlever de la main du roi de Syrie?)
4 Saboda haka ya tambayi Yehoshafat, ya ce, “Za ka tafi tare da ni don in yi yaƙi da Ramot Gileyad?” Yehoshafat ya amsa wa sarkin Isra’ila, ya ce, “Ni ma kamar ka ne, mutanena kuwa kamar mutanenka, dawakaina kamar dawakanka.”
Et il demanda à Josaphat: Viendrez-vous avec moi pour combattre contre Ramoth-Galaad?
5 Amma Yehoshafat ya ce wa sarkin Isra’ila, “Da farko mu nemi nufin Ubangiji.”
Et Josaphat répondit au roi d’Israël: Comme je suis, ainsi vous êtes vous-même: mon peuple et votre peuple sont une seule chose, et ma cavalerie est votre cavalerie. Il dit encore au roi d’Israël: Consultez, je vous prie, aujourd’hui la parole du Seigneur.
6 Saboda haka sarkin Isra’ila ya tattara annabawa, kamar ɗari huɗu, ya tambaye su, “In kai yaƙi a kan Ramot Gileyad, ko kada in kai?” Suka amsa, “Ka tafi, gama Ubangiji zai ba ka ita a hannunka.”
Le roi d’Israël assembla donc les prophètes, environ quatre cents hommes, et il leur dit: Dois-je aller combattre contre Ramoth-Galaad, ou me tenir en repos? Ceux-ci lui répondirent: Montez, et le Seigneur la mettra dans la main du roi.
7 Amma Yehoshafat ya yi tambaya, ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu tambaya?”
Mais Josaphat lui demanda: N’y a-t-il pas ici quelque prophète du Seigneur, afin que nous le consultions par lui?
8 Sarkin Isra’ila ya amsa wa Yehoshafat, ya ce, “Akwai mutum guda har yanzu wanda ta wurinsa za mu iya nemi nufin Ubangiji, amma na ƙi jininsa domin bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni ba, sai dai mummuna kullum. Shi ne Mikahiya ɗan Imla.” Yehoshafat ya ce, “Kada sarki ya ce haka.”
Et le roi d’Israël répondit à Josaphat: Il est demeuré un homme par qui nous pouvons consulter le Seigneur; mais, moi, je le hais, parce qu’il ne me prophétise point du bien, mais du mal: c’est Michée, fils de Jemla. Josaphat lui dit: Ne parlez pas ainsi, ô roi.
9 Saboda haka sarkin Isra’ila ya kira ɗaya daga cikin shugabanninsa ya ce, “Kawo Mikahiya ɗan Imla nan take.”
Le roi d’Israël appela donc un certain eunuque, et lui dit: Hâte-toi d’amener Michée, fils de Jemla.
10 Saye da rigunansu na sarauta, sarkin Isra’ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suna zama a kujerun sarautarsu a masussuka ta mashigin ƙofar Samariya, tare da dukan annabawa suna ta annabci a gabansu.
Mais le roi d’Israël et Josaphat, roi de Juda, étaient assis chacun sur leur trône, vêtus avec une magnificence royale, dans une aire près de la porte de Samarie, et tous les prophètes prophétisaient en leur présence.
11 Zedekiya ɗan Kena’ana kuwa ya yi ƙahonin ƙarfe ya kuma furta, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Da waɗannan za ka tunkuyi Arameyawa har su hallaka.’”
Sédécias, fils de Chanaana se fit aussi des cornes de fer, et dit: Voici ce que dit le Seigneur: Tu agiteras la Syrie avec ces cornes, jusqu’à ce que tu l’aies détruite.
12 Dukan sauran annabawan suka yi annabci iri abu ɗaya. Suka ce, “Ka yaƙi Ramot Gileyad, ka kuma yi nasara, gama Ubangiji zai ba da ita cikin hannun sarki.”
Et tous les prophètes prophétisaient de même, disant: Montez contre Ramoth-Galaad, et marchez heureusement, et le Seigneur la mettra dans la main du roi.
13 Ɗan aikan da ya je yă kawo Mikahiya, ya ce masa, “Duba, sauran annabawa suna maganar nasara wa sarki, sai ka ce mutum guda. Bari maganarka tă yarda da tasu, ka kuma yi maganar alheri.”
Or le messager qui était allé pour appeler Michée, lui parla, disant: Voilà que les paroles des prophètes prédisent unanimement au roi de bonnes choses: que votre parole soit donc semblable à la leur, et dites de bonnes choses.
14 Amma Mikahiya ya ce, “Na rantse da Ubangiji mai rai, zan faɗa masa kawai abin da Ubangiji ya faɗa mini.”
Michée lui répondit: Le Seigneur vit! tout ce que m’aura dit le Seigneur, c’est ce que je dirai.
15 Da suka kai, sai sarki ya tambaye shi, ya ce, “Mikahiya, mu kai yaƙi a kan Ramot Gileyad, ko kada mu kai?” Ya amsa ya ce, “Yaƙe ta, za ka kuwa yi nasara, gama Ubangiji zai ba da ita cikin hannun sarki.”
Michée vint donc vers le roi, et le roi lui dit: Michée, devons-nous aller contre Ramoth-Galaad pour combattre, ou nous reposer? Celui-ci lui répondit: Montez, marchez heureusement, et le Seigneur la mettra dans la main du roi.
16 Sai sarki ya ce masa, “Sau nawa ne zan sa ka rantse cewa ba za ka faɗa mini kome ba sai dai gaskiya a cikin sunan Ubangiji?”
Mais le roi lui dit: Je t’adjure de nouveau et encore de nouveau de ne me dire que ce qui est vrai, au nom du Seigneur.
17 Sa’an nan Mikahiya ya amsa, “Na ga dukan Isra’ila a warwatse a kan tuddai kamar tumakin da ba su da makiyayi, kuma Ubangiji ya ce, ‘Waɗannan mutane ba su da maigida. Bari kowa yă tafi gida cikin salama.’”
Alors il lui dit: J’ai vu tout Israël dispersé dans les montagnes, comme des brebis qui n’ont point de pasteur; et le Seigneur a dit: Ceux-ci n’ont pas de maître; que chacun retourne dans sa maison en paix.
18 Sai sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Ban faɗa maka cewa bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni, sai mummuna kawai ba?”
(Le roi d’Israël dit donc à Josaphat: Ne vous ai-je pas dit qu’il ne me prophétise point du bien, mais du mal?)
19 Mikahiya ya ci gaba, “Saboda haka ka ji maganar Ubangiji. I, na ga Ubangiji zaune a kursiyinsa tare da dukan rundunar sama tsaye kewaye da shi a dama da hagunsa.
Mais Michée continuant, dit: C’est pourquoi écoutez la parole du Seigneur: J’ai vu le Seigneur assis sur son trône, et toute l’armée du ciel se tenant près de lui à droite et à gauche;
20 Kuma Ubangiji ya ce, ‘Wa zai ruɗi Ahab zuwa yaƙi da Ramot Gileyad, yă kuma kai shi mutuwarsa a can?’ “Wani ya ce wannan, wani ya ce wancan.
Et le Seigneur a dit: Qui trompera Achab, roi d’Israël, afin qu’il monte et qu’il succombe à Ramoth-Galaad? Et l’un dit de telles choses, et l’autre autrement.
21 A ƙarshe, wani ruhu ya zo gaba, ya tsaya a gaban Ubangiji ya ce, ‘Zan ruɗe shi.’
Mais l’esprit malin sortit, et se tint devant le Seigneur, et dit: C’est moi qui le tromperai. Le Seigneur lui dit: En quoi?
22 “Ubangiji ya yi tambaya ‘Ta wace hanya?’ Ya ce, “‘Zan tafi in zama ruhun ƙarya a bakunan dukan annabawansa.’ “Ubangiji ya ce, ‘Za ka yi nasara a ruɗinsa. Ka tafi, ka yi haka.’
Et il répondit: Je sortirai, et je serai un esprit menteur dans la bouche de tous ses prophètes. Et le Seigneur dit: Tu le tromperas et tu prévaudras. Sors, et fais ainsi.
23 “Saboda haka yanzu Ubangiji ya sa ruhun ƙarya a bakunan dukan annabawanka. Ubangiji ya zartar maka da masifa.”
Maintenant donc, voilà que le Seigneur a mis un esprit de mensonge dans la bouche de tous vos prophètes qui sont ici, et le Seigneur a prononcé contre vous malheur.
24 Sai Zedekiya ɗan Kena’ana ya hau ya mari Mikahiya a fuska. Ya yi tambaya, “A wace hanya ce ruhu daga Ubangiji ya bar ni ya yi maka magana?”
Or Sédécias, fils de Chanaana, s’approcha et frappa Michée sur la joue, et dit: Est-ce donc moi que l’esprit du Seigneur a quitté, et t’a-t-il parlé à toi?
25 Mikahiya ya amsa, “Za ka gane a ranar da ka je ka ɓuya a ciki cikin ɗaki.”
Et Michée dit: Vous le verrez au jour même où vous entrerez dans une chambre, qui est dans une chambre, pour vous cacher.
26 Sa’an nan sarkin Isra’ila ya umarta, “Ku kama Mikahiya, ku kai shi wurin Amon, shugaban birnin, da wurin Yowash ɗan sarki.
Alors le roi d’Israël dit: Prenez Michée, et qu’il demeure chez Amon, gouverneur de la ville, et chez Joas, fils d’Amélech,
27 Ku ce ga abin da sarki ya ce, ‘Ku sa wannan mutum a kurkuku, kuma kada ku ba shi wani abu sai dai burodi da ruwa, sai na dawo lafiya.’”
Et dites-leur: Voici ce que dit le roi: Envoyez cet homme dans la prison, et sustentez-le d’un pain de tribulation et d’une eau d’angoisse, jusqu’à ce que je revienne en paix.
28 Mikahiya ya furta, “Idan har ka dawo lafiya, to, Ubangiji bai yi magana ta wurina ba.” Ya kuma ƙara da cewa, “Ku lura da maganata, dukanku mutane!”
Et Michée dit: Si vous revenez en paix, le Seigneur n’a point parlé par moi. Et il ajouta: Peuples, tous tant que vous êtes, écoutez.
29 Sai sarkin Isra’ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suka haura zuwa Ramot Gileyad.
Le roi d’Israël monta donc, et Josaphat, roi de Juda, contre Ramoth-Galaad.
30 Sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Zan ɓad da kama in shiga wurin yaƙi, amma ka sa kayan sarautarka.” Saboda haka sarkin Isra’ila ya ɓad da kama, ya shiga cikin yaƙi.
C’est pourquoi le roi d’Israël dit à Josaphat: Prenez vos armes, entrez au combat, et revêtez-vous de vos vêtements. Mais le roi d’Israël changea ses vêtements, puis entra au combat.
31 Sarkin Aram kuwa ya umarci shugabanni kekunan yaƙinsa talatin da biyu, ya ce, “Kada ku yaƙe kowa, ƙarami ko babba, sai dai sarkin Isra’ila.”
Or le roi de Syrie avait ordonné aux trente-deux commandants de ses chariots, disant: Ne combattez point contre un petit et un grand, quel qu’il soit, si ce n’est contre le roi d’Israël seul.
32 Sa’ad da shugabannin kekunan yaƙin suka ga Yehoshafat, suka yi tsammani, suka ce, “Tabbatacce wannan shi ne sarkin Isra’ila.” Saboda haka suka juye don su yaƙe shi, amma sa’ad da Yehoshafat ya yi ihu,
Lors donc que les commandants des chariots eurent vu Josaphat, ils supposèrent que c’était le roi d’Israël; et, se précipitant, ils combattaient contre lui; alors Josaphat jeta un grand cri;
33 sai shugabannin kekunan yaƙin suka ga ashe ba sarkin Isra’ila ba ne, sai suka daina binsa.
Et les commandants des chariots reconnurent que ce n’était pas le roi d’Israël, et ils le laissèrent.
34 Amma wani ya ja bakansa kawai ya bugi Ahab sarkin Isra’ila a tsakanin sassan kayan yaƙinsa. Sai sarki ya ce wa mahayin keken yaƙinsa, “Juye, ka fitar da ni daga yaƙin. An ji mini rauni.”
Mais un certain homme tendit son arc, tirant une flèche à l’aventure, et par hasard, il frappa le roi d’Israël entre le poumon et l’estomac. Mais le roi dit au conducteur de son char: Tourne ta main, et retire-moi de l’armée, parce que je suis grièvement blessé.
35 Dukan yini aka yi ta yaƙi, aka kuma riƙe sarki a keken yaƙinsa yana fuskanci Arameyawa. Jini daga mikinsa ya yi ta zuba a ƙasan keken yaƙin, a wannan yamma kuwa ya mutu.
Le combat fut donc engagé ce jour-là, et le roi d’Israël se tenait sur son char en face des Syriens, et il mourut vers le soir; or le sang de la plaie coulait dans l’intérieur du char.
36 Da rana tana fāɗuwa, sai kuka ta bazu cikin mayaƙa, “Kowane mutum ya tafi garinsu; kowa ya tafi ƙasarsa!”
Et le héraut, avant que le soleil fût couché; sonna de la trompette dans toute l’armée, disant: Que chacun retourne en sa ville et en sa terre.
37 Sai sarki ya mutu, aka kuwa kawo shi Samariya, aka binne shi a can.
Le roi mourut donc, et il fut porté à Samarie; ainsi, on ensevelit le roi à Samarie.
38 Suka wanke keken yaƙi a tafki, a Samariya (inda karuwai suke wanka), sai karnuka suka lashe jininsa, kamar yadda maganar Ubangiji ta furta.
Et on lava son char dans la piscine de Samarie, et les chiens léchèrent son sang, et on lava les rênes, selon la parole que le Seigneur avait dite.
39 Game da sauran ayyukan mulkin Ahab, haɗe da dukan abin da ya yi, da fadan da ya gina ya kuma shimfiɗa da hauren giwa, da biranen da ya gina, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Mais le reste des actions d’Achab, et tout ce qu’il fit, la maison d’ivoire qu’il bâtit, et toutes les villes qu’il construisit, n’est-ce pas écrit dans le Livre des actions des jours des rois d’Israël?
40 Ahab ya huta da kakanninsa. Ahaziya ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Achab dormit donc avec ses pères, et Ochozias, son fils, régna en sa place.
41 Yehoshafat ɗan Asa ya zama sarkin Yahuda a shekara ta huɗu ta Ahab sarkin Isra’ila.
Or Josaphat, fils d’Asa, avait commencé à régner sur Juda la quatrième année d’Achab, roi d’Israël.
42 Yehoshafat yana da shekara talatin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru ashirin da biyar. Sunan mahaifiyarsa, Azuba’yar Shilhi.
Il avait trente-cinq ans lorsqu’il commença à régner, et il régna vingt-cinq ans dans Jérusalem. Le nom de sa mère était Azuba, fille de Salaï.
43 A cikin kome ya yi tafiya a hanyoyin mahaifinsa Asa, bai kuma kauce daga gare su ba; ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji. Amma bai rurrushe masujadai da suke kan tuddai ba, mutane kuwa suka ci gaba da miƙa hadayu suna kuma ƙone turare a can.
Et il marcha dans toute la voie d’Aza son père, et il ne s’en détourna point, et il fit ce qui était droit en la présence du Seigneur. Cependant il ne détruisit pas les hauts lieux; car le peuple sacrifiait encore et brûlait de l’encens sur les hauts lieux.
44 Yehoshafat kuma ya zauna lafiya da sarkin Isra’ila.
Et Josaphat eut la paix avec le roi d’Israël.
45 Game da sauran ayyukan mulkin Yehoshafat da abubuwan da ya yi, da kuma yaƙe-yaƙensa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Mais le reste des actions de Josaphat, et ses œuvres qu’il fit, et ses combats, n’est-ce pas écrit dans le Livre des actions des jours des rois de Juda?
46 Ya kawar da karuwai maza na masujadai da suke kan tuddai waɗanda suka rage tun mulkin mahaifinsa Asa.
Mais aussi les restes des efféminés qui étaient demeurés dans les jours d’Asa son père, il les enleva de la terre.
47 Babu sarki a lokacin Edom, saboda haka sai mataimaki ya yi mulki.
Et il n’y avait point alors de roi établi dans Edom.
48 To, Yehoshafat ya gina jerin jiragen ruwan kasuwanci don su je Ofir saboda zinariya, amma ba su yi tafiya ba, gama sun farfashe a Eziyon Geber.
Or le roi Josaphat avait construit des flottes sur la mer, lesquelles firent voile vers Ophir, pour en apporter l’or; et elles ne purent pas y aller, parce qu’elles furent brisées à Asiongaber.
49 A lokacin Ahaziya ɗan Ahab ya ce wa Yehoshafat, “Bari mutanena su tafi tare da mutanenka,” amma Yehoshafat ya ƙi.
Alors Ochozias, fils d’Achab, dit à Josaphat: Que mes serviteurs aillent sur les vaisseaux avec les vôtres. Mais Josaphat ne voulut pas.
50 Yehoshafat kuwa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a birnin Dawuda kakansa. Sai Yehoram ɗansa ya gāje shi.
Et Josaphat dormit avec ses pères, et il fut enseveli avec eux dans la cité de David, son père; et Joram, son fils, régna en sa place.
51 Ahaziya ɗan Ahab ya zama sarkin Isra’ila a Samariya a shekara ta goma sha bakwai ta Yehoshafat sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila shekaru biyu.
Or Ochozias, fils d’Achab, avait commencé à régner sur Israël dans Samarie la dix-septième année de Josaphat, roi de Juda, et il régna deux ans sur Israël.
52 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, domin ya yi tafiya a hanyoyin mahaifinsa da na mahaifiyarsa, da kuma a hanyoyin Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila suka yi zunubi.
Et il fit le mal en la présence du Seigneur; il marcha dans la voie de son père et de sa mère, et dans la voie de Jéroboam, fils de Nabath, qui fit pécher Israël.
53 Ya bauta, ya kuma yi wa Ba’al sujada, ya tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila yă yi fushi, kamar yadda mahaifinsa ya yi.
Il servit aussi Baal et l’adora, et il irrita le Seigneur Dieu d’Israël, selon tout ce que son père avait fait.

< 1 Sarakuna 22 >