< 1 Sarakuna 22 >
1 Aka yi shekaru uku ba a yi yaƙi tsakanin Aram da Isra’ila ba.
Il se passa trois ans sans guerre entre la Syrie et Israël.
2 Amma a shekara ta uku, Yehoshafat sarkin Yahuda ya gangara don yă ga sarki Isra’ila.
La troisième année, Josaphat, roi de Juda, descendit auprès du roi d'Israël.
3 Sarkin Isra’ila ya ce wa shugabanninsa, “Ba ku san cewa Ramot Gileyad namu ne ba, duk da haka ba mu yi kome ba don mu sāke karɓanta daga sarkin Aram?”
Le roi d'Israël dit à ses serviteurs: « Savez-vous que Ramoth Galaad est à nous, que nous ne faisons rien et que nous ne l'arrachons pas à la main du roi de Syrie? »
4 Saboda haka ya tambayi Yehoshafat, ya ce, “Za ka tafi tare da ni don in yi yaƙi da Ramot Gileyad?” Yehoshafat ya amsa wa sarkin Isra’ila, ya ce, “Ni ma kamar ka ne, mutanena kuwa kamar mutanenka, dawakaina kamar dawakanka.”
Il dit à Josaphat: « Veux-tu aller avec moi au combat à Ramoth Galaad? » Josaphat dit au roi d'Israël: « Je suis comme toi, mon peuple comme ton peuple, mes chevaux comme tes chevaux. »
5 Amma Yehoshafat ya ce wa sarkin Isra’ila, “Da farko mu nemi nufin Ubangiji.”
Josaphat dit au roi d'Israël: « Je te prie de t'enquérir d'abord de la parole de Yahvé. »
6 Saboda haka sarkin Isra’ila ya tattara annabawa, kamar ɗari huɗu, ya tambaye su, “In kai yaƙi a kan Ramot Gileyad, ko kada in kai?” Suka amsa, “Ka tafi, gama Ubangiji zai ba ka ita a hannunka.”
Alors le roi d'Israël rassembla les prophètes, environ quatre cents hommes, et leur dit: « Dois-je aller combattre à Ramoth Galaad, ou dois-je m'abstenir? » Ils ont dit: « Monte, car le Seigneur la livrera entre les mains du roi. »
7 Amma Yehoshafat ya yi tambaya, ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu tambaya?”
Mais Josaphat dit: « N'y a-t-il pas ici un prophète de Yahvé, pour que nous le consultions? »
8 Sarkin Isra’ila ya amsa wa Yehoshafat, ya ce, “Akwai mutum guda har yanzu wanda ta wurinsa za mu iya nemi nufin Ubangiji, amma na ƙi jininsa domin bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni ba, sai dai mummuna kullum. Shi ne Mikahiya ɗan Imla.” Yehoshafat ya ce, “Kada sarki ya ce haka.”
Le roi d'Israël dit à Josaphat: « Il y a encore un homme par qui nous pouvons consulter Yahvé, Michée, fils d'Imla; mais je le déteste, car il ne prophétise pas le bien à mon sujet, mais le mal. » Josaphat a dit: « Que le roi ne le dise pas. »
9 Saboda haka sarkin Isra’ila ya kira ɗaya daga cikin shugabanninsa ya ce, “Kawo Mikahiya ɗan Imla nan take.”
Alors le roi d'Israël appela un officier, et dit: « Va vite chercher Michée, fils d'Imla. »
10 Saye da rigunansu na sarauta, sarkin Isra’ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suna zama a kujerun sarautarsu a masussuka ta mashigin ƙofar Samariya, tare da dukan annabawa suna ta annabci a gabansu.
Le roi d'Israël et Josaphat, roi de Juda, étaient assis chacun sur son trône, revêtus de leurs robes, sur une place ouverte à l'entrée de la porte de Samarie, et tous les prophètes prophétisaient devant eux.
11 Zedekiya ɗan Kena’ana kuwa ya yi ƙahonin ƙarfe ya kuma furta, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Da waɗannan za ka tunkuyi Arameyawa har su hallaka.’”
Sédécias, fils de Chenaana, se fit des cornes de fer, et dit: « Yahvé dit: C'est avec elles que tu pousseras les Syriens, jusqu'à ce qu'ils soient consumés. »
12 Dukan sauran annabawan suka yi annabci iri abu ɗaya. Suka ce, “Ka yaƙi Ramot Gileyad, ka kuma yi nasara, gama Ubangiji zai ba da ita cikin hannun sarki.”
Tous les prophètes prophétisaient ainsi: « Monte à Ramoth Galaad et prospère, car Yahvé la livrera entre les mains du roi. »
13 Ɗan aikan da ya je yă kawo Mikahiya, ya ce masa, “Duba, sauran annabawa suna maganar nasara wa sarki, sai ka ce mutum guda. Bari maganarka tă yarda da tasu, ka kuma yi maganar alheri.”
Le messager qui était allé appeler Michée lui parla ainsi: « Vois maintenant, les prophètes disent du bien au roi d'une seule bouche. Je te prie de faire en sorte que ta parole soit semblable à la parole de l'un d'eux, et qu'elle soit bonne. »
14 Amma Mikahiya ya ce, “Na rantse da Ubangiji mai rai, zan faɗa masa kawai abin da Ubangiji ya faɗa mini.”
Michée dit: « L'Éternel est vivant, et je dirai ce que l'Éternel me dira. »
15 Da suka kai, sai sarki ya tambaye shi, ya ce, “Mikahiya, mu kai yaƙi a kan Ramot Gileyad, ko kada mu kai?” Ya amsa ya ce, “Yaƙe ta, za ka kuwa yi nasara, gama Ubangiji zai ba da ita cikin hannun sarki.”
Lorsqu'il fut arrivé auprès du roi, celui-ci lui dit: « Michée, irons-nous à Ramoth Galaad pour combattre, ou bien nous abstiendrons-nous? » Il lui répondit: « Monte et prospère, et Yahvé le livrera entre les mains du roi. »
16 Sai sarki ya ce masa, “Sau nawa ne zan sa ka rantse cewa ba za ka faɗa mini kome ba sai dai gaskiya a cikin sunan Ubangiji?”
Le roi lui dit: « Combien de fois dois-je t'adjurer de ne me dire que la vérité au nom de Yahvé? »
17 Sa’an nan Mikahiya ya amsa, “Na ga dukan Isra’ila a warwatse a kan tuddai kamar tumakin da ba su da makiyayi, kuma Ubangiji ya ce, ‘Waɗannan mutane ba su da maigida. Bari kowa yă tafi gida cikin salama.’”
Il dit: « J'ai vu tout Israël dispersé sur les montagnes, comme des brebis qui n'ont pas de berger. Yahvé a dit: « Elles n'ont pas de maître. Que chacun retourne en paix dans sa maison ».
18 Sai sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Ban faɗa maka cewa bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni, sai mummuna kawai ba?”
Le roi d'Israël dit à Josaphat: « Ne t'ai-je pas dit qu'il ne prophétiserait pas du bien à mon sujet, mais du mal? »
19 Mikahiya ya ci gaba, “Saboda haka ka ji maganar Ubangiji. I, na ga Ubangiji zaune a kursiyinsa tare da dukan rundunar sama tsaye kewaye da shi a dama da hagunsa.
Michée dit: « Écoutez donc la parole de Yahvé. J'ai vu Yahvé assis sur son trône, et toute l'armée des cieux qui se tenait près de lui, à sa droite et à sa gauche.
20 Kuma Ubangiji ya ce, ‘Wa zai ruɗi Ahab zuwa yaƙi da Ramot Gileyad, yă kuma kai shi mutuwarsa a can?’ “Wani ya ce wannan, wani ya ce wancan.
Yahvé dit: « Qui séduira Achab, pour qu'il monte et tombe à Ramoth Galaad? L'un disait une chose, l'autre une autre.
21 A ƙarshe, wani ruhu ya zo gaba, ya tsaya a gaban Ubangiji ya ce, ‘Zan ruɗe shi.’
Un esprit sortit et se tint devant Yahvé, et dit: « Je vais le séduire.
22 “Ubangiji ya yi tambaya ‘Ta wace hanya?’ Ya ce, “‘Zan tafi in zama ruhun ƙarya a bakunan dukan annabawansa.’ “Ubangiji ya ce, ‘Za ka yi nasara a ruɗinsa. Ka tafi, ka yi haka.’
Yahvé lui dit: « Comment? Il a dit: « Je sortirai et je serai un esprit de mensonge dans la bouche de tous ses prophètes. Il dit: « Tu le séduiras, et tu l'emporteras. Sors et fais-le.
23 “Saboda haka yanzu Ubangiji ya sa ruhun ƙarya a bakunan dukan annabawanka. Ubangiji ya zartar maka da masifa.”
Maintenant, voici, Yahvé a mis un esprit de mensonge dans la bouche de tous vos prophètes, et Yahvé a dit du mal de vous. »
24 Sai Zedekiya ɗan Kena’ana ya hau ya mari Mikahiya a fuska. Ya yi tambaya, “A wace hanya ce ruhu daga Ubangiji ya bar ni ya yi maka magana?”
Alors Sédécias, fils de Chenaana, s'approcha et frappa Michée sur la joue, et dit: « Par où l'Esprit de Yahvé est-il sorti de moi pour te parler? »
25 Mikahiya ya amsa, “Za ka gane a ranar da ka je ka ɓuya a ciki cikin ɗaki.”
Michée dit: « Voici ce que tu verras, ce jour-là, quand tu iras te cacher dans une pièce intérieure. »
26 Sa’an nan sarkin Isra’ila ya umarta, “Ku kama Mikahiya, ku kai shi wurin Amon, shugaban birnin, da wurin Yowash ɗan sarki.
Le roi d'Israël dit: « Prends Michée, et porte-le à Amon, gouverneur de la ville, et à Joas, fils du roi.
27 Ku ce ga abin da sarki ya ce, ‘Ku sa wannan mutum a kurkuku, kuma kada ku ba shi wani abu sai dai burodi da ruwa, sai na dawo lafiya.’”
Tu diras: « Le roi dit: Mets cet homme dans la prison, et nourris-le de pain de souffrance et d'eau de souffrance, jusqu'à ce que je vienne en paix ».
28 Mikahiya ya furta, “Idan har ka dawo lafiya, to, Ubangiji bai yi magana ta wurina ba.” Ya kuma ƙara da cewa, “Ku lura da maganata, dukanku mutane!”
Michée dit: « Si vous revenez en paix, Yahvé n'a pas parlé par moi. » Il dit: « Écoutez, vous tous! »
29 Sai sarkin Isra’ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suka haura zuwa Ramot Gileyad.
Le roi d'Israël et Josaphat, roi de Juda, montèrent donc à Ramoth Galaad.
30 Sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Zan ɓad da kama in shiga wurin yaƙi, amma ka sa kayan sarautarka.” Saboda haka sarkin Isra’ila ya ɓad da kama, ya shiga cikin yaƙi.
Le roi d'Israël dit à Josaphat: « Je me déguiserai et j'irai au combat, mais toi, mets tes vêtements. » Le roi d'Israël se déguisa et alla au combat.
31 Sarkin Aram kuwa ya umarci shugabanni kekunan yaƙinsa talatin da biyu, ya ce, “Kada ku yaƙe kowa, ƙarami ko babba, sai dai sarkin Isra’ila.”
Or le roi de Syrie avait donné cet ordre aux trente-deux chefs de ses chars: « Ne combattez ni petits ni grands, si ce n'est contre le roi d'Israël. »
32 Sa’ad da shugabannin kekunan yaƙin suka ga Yehoshafat, suka yi tsammani, suka ce, “Tabbatacce wannan shi ne sarkin Isra’ila.” Saboda haka suka juye don su yaƙe shi, amma sa’ad da Yehoshafat ya yi ihu,
Lorsque les chefs des chars virent Josaphat, ils dirent: « C'est bien là le roi d'Israël » et ils vinrent le combattre. Josaphat poussa un cri.
33 sai shugabannin kekunan yaƙin suka ga ashe ba sarkin Isra’ila ba ne, sai suka daina binsa.
Quand les chefs des chars virent que ce n'était pas le roi d'Israël, ils cessèrent de le poursuivre.
34 Amma wani ya ja bakansa kawai ya bugi Ahab sarkin Isra’ila a tsakanin sassan kayan yaƙinsa. Sai sarki ya ce wa mahayin keken yaƙinsa, “Juye, ka fitar da ni daga yaƙin. An ji mini rauni.”
Un homme tira son arc au hasard et frappa le roi d'Israël entre les jointures de l'armure. Il dit alors au conducteur de son char: « Fais demi-tour et emporte-moi hors de la bataille, car je suis gravement blessé. »
35 Dukan yini aka yi ta yaƙi, aka kuma riƙe sarki a keken yaƙinsa yana fuskanci Arameyawa. Jini daga mikinsa ya yi ta zuba a ƙasan keken yaƙin, a wannan yamma kuwa ya mutu.
Le combat s'intensifia ce jour-là. Le roi fut soutenu dans son char, face aux Syriens, et mourut le soir. Le sang coulait de la blessure dans le fond du char.
36 Da rana tana fāɗuwa, sai kuka ta bazu cikin mayaƙa, “Kowane mutum ya tafi garinsu; kowa ya tafi ƙasarsa!”
Vers le coucher du soleil, un cri se répandit dans l'armée: « Chacun dans sa ville, chacun dans son pays. »
37 Sai sarki ya mutu, aka kuwa kawo shi Samariya, aka binne shi a can.
Le roi mourut et fut amené à Samarie, et l'on enterra le roi à Samarie.
38 Suka wanke keken yaƙi a tafki, a Samariya (inda karuwai suke wanka), sai karnuka suka lashe jininsa, kamar yadda maganar Ubangiji ta furta.
On lava le char près de l'étang de Samarie, et les chiens léchèrent son sang là où les prostituées se lavaient, selon la parole que l'Éternel avait prononcée.
39 Game da sauran ayyukan mulkin Ahab, haɗe da dukan abin da ya yi, da fadan da ya gina ya kuma shimfiɗa da hauren giwa, da biranen da ya gina, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Et le reste des actes d'Achab, et tout ce qu'il a fait, et la maison d'ivoire qu'il a bâtie, et toutes les villes qu'il a bâties, cela n'est-il pas écrit dans le livre des chroniques des rois d'Israël?
40 Ahab ya huta da kakanninsa. Ahaziya ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Achab se coucha avec ses pères, et Achazia, son fils, régna à sa place.
41 Yehoshafat ɗan Asa ya zama sarkin Yahuda a shekara ta huɗu ta Ahab sarkin Isra’ila.
Josaphat, fils d'Asa, commença à régner sur Juda la quatrième année d'Achab, roi d'Israël.
42 Yehoshafat yana da shekara talatin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru ashirin da biyar. Sunan mahaifiyarsa, Azuba’yar Shilhi.
Josaphat avait trente-cinq ans lorsqu'il devint roi, et il régna vingt-cinq ans à Jérusalem. Le nom de sa mère était Azuba, fille de Schilchi.
43 A cikin kome ya yi tafiya a hanyoyin mahaifinsa Asa, bai kuma kauce daga gare su ba; ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji. Amma bai rurrushe masujadai da suke kan tuddai ba, mutane kuwa suka ci gaba da miƙa hadayu suna kuma ƙone turare a can.
Il marcha dans toute la voie d'Asa, son père. Il ne s'en détourna pas, faisant ce qui était juste aux yeux de l'Éternel. Cependant, les hauts lieux ne furent pas supprimés. Le peuple continuait à offrir des sacrifices et à brûler des encens sur les hauts lieux.
44 Yehoshafat kuma ya zauna lafiya da sarkin Isra’ila.
Josaphat fit la paix avec le roi d'Israël.
45 Game da sauran ayyukan mulkin Yehoshafat da abubuwan da ya yi, da kuma yaƙe-yaƙensa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Le reste des actes de Josaphat, la force qu'il déploya et la manière dont il combattit, cela n'est-il pas écrit dans le livre des Chroniques des rois de Juda?
46 Ya kawar da karuwai maza na masujadai da suke kan tuddai waɗanda suka rage tun mulkin mahaifinsa Asa.
Il chassa du pays le reste des sodomites qui subsistaient du temps d'Asa, son père.
47 Babu sarki a lokacin Edom, saboda haka sai mataimaki ya yi mulki.
Il n'y avait pas de roi à Édom. Un député régnait.
48 To, Yehoshafat ya gina jerin jiragen ruwan kasuwanci don su je Ofir saboda zinariya, amma ba su yi tafiya ba, gama sun farfashe a Eziyon Geber.
Josaphat fit faire des navires de Tarsis pour aller chercher de l'or à Ophir, mais ils n'y allèrent pas, car les navires firent naufrage à Ezion Geber.
49 A lokacin Ahaziya ɗan Ahab ya ce wa Yehoshafat, “Bari mutanena su tafi tare da mutanenka,” amma Yehoshafat ya ƙi.
Alors Achazia, fils d'Achab, dit à Josaphat: « Laisse mes serviteurs aller avec tes serviteurs dans les navires. » Mais Josaphat ne voulut pas.
50 Yehoshafat kuwa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a birnin Dawuda kakansa. Sai Yehoram ɗansa ya gāje shi.
Josaphat se coucha avec ses pères, et il fut enterré avec ses pères dans la ville de David, son père. Joram, son fils, régna à sa place.
51 Ahaziya ɗan Ahab ya zama sarkin Isra’ila a Samariya a shekara ta goma sha bakwai ta Yehoshafat sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila shekaru biyu.
Achazia, fils d'Achab, commença à régner sur Israël à Samarie, la dix-septième année de Josaphat, roi de Juda, et il régna deux ans sur Israël.
52 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, domin ya yi tafiya a hanyoyin mahaifinsa da na mahaifiyarsa, da kuma a hanyoyin Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila suka yi zunubi.
Il fit ce qui est mal aux yeux de l'Éternel, et il marcha dans la voie de son père, dans la voie de sa mère, et dans la voie de Jéroboam, fils de Nebat, par laquelle il avait fait pécher Israël.
53 Ya bauta, ya kuma yi wa Ba’al sujada, ya tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila yă yi fushi, kamar yadda mahaifinsa ya yi.
Il servit Baal et se prosterna devant lui, et il provoqua la colère de Yahvé, le Dieu d'Israël, selon toutes les manières dont son père avait agi.