< 1 Sarakuna 22 >

1 Aka yi shekaru uku ba a yi yaƙi tsakanin Aram da Isra’ila ba.
Then three years passed without war between Syria and Israel.
2 Amma a shekara ta uku, Yehoshafat sarkin Yahuda ya gangara don yă ga sarki Isra’ila.
But in the third year, Jehoshaphat, the king of Judah, descended to the king of Israel.
3 Sarkin Isra’ila ya ce wa shugabanninsa, “Ba ku san cewa Ramot Gileyad namu ne ba, duk da haka ba mu yi kome ba don mu sāke karɓanta daga sarkin Aram?”
And the king of Israel said to his servants, “Are you ignorant that Ramoth Gilead is ours, and that we have neglected to take it from the hand of the king of Syria?”
4 Saboda haka ya tambayi Yehoshafat, ya ce, “Za ka tafi tare da ni don in yi yaƙi da Ramot Gileyad?” Yehoshafat ya amsa wa sarkin Isra’ila, ya ce, “Ni ma kamar ka ne, mutanena kuwa kamar mutanenka, dawakaina kamar dawakanka.”
And so he said to Jehoshaphat, “Will you come to the battle with me at Ramoth Gilead?”
5 Amma Yehoshafat ya ce wa sarkin Isra’ila, “Da farko mu nemi nufin Ubangiji.”
And Jehoshaphat said to the king of Israel: “As I am, so also are you. My people and your people are one. And my horsemen are your horsemen.” And Jehoshaphat said to the king of Israel, “I beg you to inquire today of the word of the Lord.”
6 Saboda haka sarkin Isra’ila ya tattara annabawa, kamar ɗari huɗu, ya tambaye su, “In kai yaƙi a kan Ramot Gileyad, ko kada in kai?” Suka amsa, “Ka tafi, gama Ubangiji zai ba ka ita a hannunka.”
Therefore, the king of Israel gathered together the prophets, about four hundred men, and he said to them, “Should I go to Ramoth Gilead to make war, or should I be at peace?” They responded, “Ascend, and the Lord will give it into the hand of the king.”
7 Amma Yehoshafat ya yi tambaya, ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu tambaya?”
Then Jehoshaphat said, “Is there not here a particular prophet of the Lord, so that we may inquire by him?”
8 Sarkin Isra’ila ya amsa wa Yehoshafat, ya ce, “Akwai mutum guda har yanzu wanda ta wurinsa za mu iya nemi nufin Ubangiji, amma na ƙi jininsa domin bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni ba, sai dai mummuna kullum. Shi ne Mikahiya ɗan Imla.” Yehoshafat ya ce, “Kada sarki ya ce haka.”
And the king of Israel said to Jehoshaphat: “One man remains, by whom we may be able to inquire of the Lord: Micaiah, the son of Imlah. But I hate him. For he does not prophecy good to me, but evil.” And Jehoshaphat said, “You should not speak in this way, O king.”
9 Saboda haka sarkin Isra’ila ya kira ɗaya daga cikin shugabanninsa ya ce, “Kawo Mikahiya ɗan Imla nan take.”
Therefore, the king of Israel called a certain eunuch, and he said to him, “Hurry to bring here Micaiah, the son of Imlah.”
10 Saye da rigunansu na sarauta, sarkin Isra’ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suna zama a kujerun sarautarsu a masussuka ta mashigin ƙofar Samariya, tare da dukan annabawa suna ta annabci a gabansu.
Now the king of Israel, and Jehoshaphat, the king of Judah, were each sitting upon his own throne, clothed in the habit of royal vestments, in a courtyard beside the entrance of the gate of Samaria. And all the prophets were prophesying in their sight.
11 Zedekiya ɗan Kena’ana kuwa ya yi ƙahonin ƙarfe ya kuma furta, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Da waɗannan za ka tunkuyi Arameyawa har su hallaka.’”
Also, Zedekiah, the son of Chenaanah, made for himself horns of iron, and he said, “Thus says the Lord: With these, you shall threaten Syria, until you destroy it.”
12 Dukan sauran annabawan suka yi annabci iri abu ɗaya. Suka ce, “Ka yaƙi Ramot Gileyad, ka kuma yi nasara, gama Ubangiji zai ba da ita cikin hannun sarki.”
And all the prophets were prophesying similarly, saying: “Ascend to Ramoth Gilead, and go forth to success. For the Lord will deliver it into the hands of the king.”
13 Ɗan aikan da ya je yă kawo Mikahiya, ya ce masa, “Duba, sauran annabawa suna maganar nasara wa sarki, sai ka ce mutum guda. Bari maganarka tă yarda da tasu, ka kuma yi maganar alheri.”
Then truly, the messenger who had gone to summon Micaiah spoke to him, saying: “Behold, the words of the prophets, as if with one mouth, are predicting good to the king. Therefore, let your word be like theirs, and speak what is good.”
14 Amma Mikahiya ya ce, “Na rantse da Ubangiji mai rai, zan faɗa masa kawai abin da Ubangiji ya faɗa mini.”
But Micaiah said to him, “As the Lord lives, whatever the Lord will have said to me, this shall I speak.”
15 Da suka kai, sai sarki ya tambaye shi, ya ce, “Mikahiya, mu kai yaƙi a kan Ramot Gileyad, ko kada mu kai?” Ya amsa ya ce, “Yaƙe ta, za ka kuwa yi nasara, gama Ubangiji zai ba da ita cikin hannun sarki.”
And so he went to the king. And the king said to him, “Micaiah, should we go to Ramoth Gilead to do battle, or should we cease?” And he responded to him, “Ascend, and go forth to success, and the Lord will deliver it into the hands of the king.”
16 Sai sarki ya ce masa, “Sau nawa ne zan sa ka rantse cewa ba za ka faɗa mini kome ba sai dai gaskiya a cikin sunan Ubangiji?”
But the king said to him, “I require you under oath, again and again, that you not say to me anything except what is true, in the name of the Lord.”
17 Sa’an nan Mikahiya ya amsa, “Na ga dukan Isra’ila a warwatse a kan tuddai kamar tumakin da ba su da makiyayi, kuma Ubangiji ya ce, ‘Waɗannan mutane ba su da maigida. Bari kowa yă tafi gida cikin salama.’”
And he said: “I saw all of Israel scattered among the hills, like sheep that have no shepherd. And the Lord said: ‘These have no master. Let each of them return to his own house in peace.’”
18 Sai sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Ban faɗa maka cewa bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni, sai mummuna kawai ba?”
Therefore, the king of Israel said to Jehoshaphat: “Did I not tell you that he prophesies nothing good to me, but always evil?”
19 Mikahiya ya ci gaba, “Saboda haka ka ji maganar Ubangiji. I, na ga Ubangiji zaune a kursiyinsa tare da dukan rundunar sama tsaye kewaye da shi a dama da hagunsa.
Yet truly, continuing, he said: “Because of his, listen to the word of the Lord. I saw the Lord sitting upon his throne. And the entire army of heaven was standing beside him, to the right and to the left.
20 Kuma Ubangiji ya ce, ‘Wa zai ruɗi Ahab zuwa yaƙi da Ramot Gileyad, yă kuma kai shi mutuwarsa a can?’ “Wani ya ce wannan, wani ya ce wancan.
And the Lord said, ‘Who will mislead Ahab, the king of Israel, so that he may ascend and fall at Ramoth Gilead?’ And one spoke words in this manner, and another spoke otherwise.
21 A ƙarshe, wani ruhu ya zo gaba, ya tsaya a gaban Ubangiji ya ce, ‘Zan ruɗe shi.’
But then a spirit went out and stood before the Lord. And he said, ‘I will mislead him.’ And the Lord said to him, ‘By what means?’
22 “Ubangiji ya yi tambaya ‘Ta wace hanya?’ Ya ce, “‘Zan tafi in zama ruhun ƙarya a bakunan dukan annabawansa.’ “Ubangiji ya ce, ‘Za ka yi nasara a ruɗinsa. Ka tafi, ka yi haka.’
And he said, ‘I will go forth, and I will be a lying spirit in the mouth of all his prophets.’ And the Lord said: ‘You will deceive him, and you will prevail. Go forth, and do so.’
23 “Saboda haka yanzu Ubangiji ya sa ruhun ƙarya a bakunan dukan annabawanka. Ubangiji ya zartar maka da masifa.”
So now, behold: the Lord has given a lying spirit into the mouth of all your prophets who are here. And the Lord has spoken evil against you.”
24 Sai Zedekiya ɗan Kena’ana ya hau ya mari Mikahiya a fuska. Ya yi tambaya, “A wace hanya ce ruhu daga Ubangiji ya bar ni ya yi maka magana?”
Then Zedekiah, the son of Chenaanah, drew near and struck Micaiah on the jaw, and he said, “So then, has the Spirit of the Lord left me, and spoken to you?”
25 Mikahiya ya amsa, “Za ka gane a ranar da ka je ka ɓuya a ciki cikin ɗaki.”
And Micaiah said, “You shall see in the day when you will enter into a room within a room, so that you may conceal yourself.”
26 Sa’an nan sarkin Isra’ila ya umarta, “Ku kama Mikahiya, ku kai shi wurin Amon, shugaban birnin, da wurin Yowash ɗan sarki.
And the king of Israel said: “Take Micaiah, and let him dwell with Amon, the ruler of the city, and with Joash, the son of Amalech.
27 Ku ce ga abin da sarki ya ce, ‘Ku sa wannan mutum a kurkuku, kuma kada ku ba shi wani abu sai dai burodi da ruwa, sai na dawo lafiya.’”
And tell them: ‘Thus says the king: Put this man in prison, and sustain him with the bread of affliction, and with the water of distress, until I return in peace.’”
28 Mikahiya ya furta, “Idan har ka dawo lafiya, to, Ubangiji bai yi magana ta wurina ba.” Ya kuma ƙara da cewa, “Ku lura da maganata, dukanku mutane!”
And Micaiah said, “If you will have returned in peace, the Lord has not spoken through me.” And he said, “May all the people hear it.”
29 Sai sarkin Isra’ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suka haura zuwa Ramot Gileyad.
And so, the king of Israel, and Jehoshaphat, the king of Judah, ascended to Ramoth Gilead.
30 Sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Zan ɓad da kama in shiga wurin yaƙi, amma ka sa kayan sarautarka.” Saboda haka sarkin Isra’ila ya ɓad da kama, ya shiga cikin yaƙi.
Then the king of Israel said to Jehoshaphat: “Take up your armor, and enter the battle. And be clothed in your own garments.” But the king of Israel changed his clothing, and he entered the war.
31 Sarkin Aram kuwa ya umarci shugabanni kekunan yaƙinsa talatin da biyu, ya ce, “Kada ku yaƙe kowa, ƙarami ko babba, sai dai sarkin Isra’ila.”
Now the king of Syria had instructed the thirty-two commanders of the chariots, saying, “You shall not fight against anyone, small or great, except against the king of Israel alone.”
32 Sa’ad da shugabannin kekunan yaƙin suka ga Yehoshafat, suka yi tsammani, suka ce, “Tabbatacce wannan shi ne sarkin Isra’ila.” Saboda haka suka juye don su yaƙe shi, amma sa’ad da Yehoshafat ya yi ihu,
Therefore, when the commanders of the chariots saw Jehoshaphat, they suspected that he was the king of Israel. And making a violent assault, they fought against him. And Jehoshaphat cried out.
33 sai shugabannin kekunan yaƙin suka ga ashe ba sarkin Isra’ila ba ne, sai suka daina binsa.
And the commanders of the chariots understood that he was not the king of Israel, and so they turned away from him.
34 Amma wani ya ja bakansa kawai ya bugi Ahab sarkin Isra’ila a tsakanin sassan kayan yaƙinsa. Sai sarki ya ce wa mahayin keken yaƙinsa, “Juye, ka fitar da ni daga yaƙin. An ji mini rauni.”
But a certain man bent his bow, aiming the arrow without certitude, and by chance he struck the king of Israel, between the lungs and the stomach. Then he said to the driver of his chariot, “Turn your hand, and carry me away from the army, for I have been grievously wounded.”
35 Dukan yini aka yi ta yaƙi, aka kuma riƙe sarki a keken yaƙinsa yana fuskanci Arameyawa. Jini daga mikinsa ya yi ta zuba a ƙasan keken yaƙin, a wannan yamma kuwa ya mutu.
Then the battle was undertaken throughout that day. And the king of Israel was standing on his chariot opposite the Syrians, and he died in the evening. For the blood was flowing from the wound into the joints of the chariot.
36 Da rana tana fāɗuwa, sai kuka ta bazu cikin mayaƙa, “Kowane mutum ya tafi garinsu; kowa ya tafi ƙasarsa!”
And a herald proclaimed throughout the entire army, before the setting of the sun, saying: “Let each one return to his own city, and to his own land.”
37 Sai sarki ya mutu, aka kuwa kawo shi Samariya, aka binne shi a can.
Then the king died, and he was carried into Samaria. And they buried the king in Samaria.
38 Suka wanke keken yaƙi a tafki, a Samariya (inda karuwai suke wanka), sai karnuka suka lashe jininsa, kamar yadda maganar Ubangiji ta furta.
And they washed his chariot in the pool of Samaria. And the dogs licked up his blood. And they washed the reins, in accord with the word of the Lord which he had spoken.
39 Game da sauran ayyukan mulkin Ahab, haɗe da dukan abin da ya yi, da fadan da ya gina ya kuma shimfiɗa da hauren giwa, da biranen da ya gina, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
But the rest of the words of Ahab, and all that he did, and the house of ivory that he built, and all the cities that he constructed, were these not written in the book of the words of the days of the kings of Israel?
40 Ahab ya huta da kakanninsa. Ahaziya ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
And so, Ahab slept with his fathers. And Ahaziah, his son, reigned in his place.
41 Yehoshafat ɗan Asa ya zama sarkin Yahuda a shekara ta huɗu ta Ahab sarkin Isra’ila.
Yet truly, Jehoshaphat, the son of Asa, had begun to reign over Judah in the fourth year of Ahab, the king of Israel.
42 Yehoshafat yana da shekara talatin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru ashirin da biyar. Sunan mahaifiyarsa, Azuba’yar Shilhi.
He was thirty-five years old when he had begun to reign, and he reigned for twenty-five years in Jerusalem. The name of his mother was Azubah, the daughter of Shilhi.
43 A cikin kome ya yi tafiya a hanyoyin mahaifinsa Asa, bai kuma kauce daga gare su ba; ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji. Amma bai rurrushe masujadai da suke kan tuddai ba, mutane kuwa suka ci gaba da miƙa hadayu suna kuma ƙone turare a can.
And he walked in the entire way of Asa, his father, and he did not decline from it. And he did what was right in the sight of the Lord. Yet truly, he did not take away the high places. For still the people were sacrificing and burning incense in the high places.
44 Yehoshafat kuma ya zauna lafiya da sarkin Isra’ila.
And Jehoshaphat had peace with the king of Israel.
45 Game da sauran ayyukan mulkin Yehoshafat da abubuwan da ya yi, da kuma yaƙe-yaƙensa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
But the rest of the words of Jehoshaphat, and his works that he did, and the battles, were these not written in the book of the words of the days of the kings of Judah?
46 Ya kawar da karuwai maza na masujadai da suke kan tuddai waɗanda suka rage tun mulkin mahaifinsa Asa.
Then, too, the remnant of the effeminate, who had remained in the days of Asa, his father, he took away from the land.
47 Babu sarki a lokacin Edom, saboda haka sai mataimaki ya yi mulki.
At that time, there was no king appointed in Idumea.
48 To, Yehoshafat ya gina jerin jiragen ruwan kasuwanci don su je Ofir saboda zinariya, amma ba su yi tafiya ba, gama sun farfashe a Eziyon Geber.
Yet truly, king Jehoshaphat had made a navy on the sea, which would sail to Ophir for gold. But they were unable to go, because the ships were broken down at Eziongeber.
49 A lokacin Ahaziya ɗan Ahab ya ce wa Yehoshafat, “Bari mutanena su tafi tare da mutanenka,” amma Yehoshafat ya ƙi.
Then Ahaziah, the son of Ahab, said to Jehoshaphat, “Let my servants go with your servants on the ships.” But Jehoshaphat was not willing.
50 Yehoshafat kuwa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a birnin Dawuda kakansa. Sai Yehoram ɗansa ya gāje shi.
And Jehoshaphat slept with his fathers, and he was buried with them in the city of David, his father. And Jehoram, his son, reigned in his place.
51 Ahaziya ɗan Ahab ya zama sarkin Isra’ila a Samariya a shekara ta goma sha bakwai ta Yehoshafat sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila shekaru biyu.
Then Ahaziah, the son of Ahab, began to reign over Israel, in Samaria, in the seventeenth year of Jehoshaphat, the king of Judah. And he reigned over Israel for two years.
52 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, domin ya yi tafiya a hanyoyin mahaifinsa da na mahaifiyarsa, da kuma a hanyoyin Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila suka yi zunubi.
And he did evil in the sight of the Lord. And he walked in the way of his father and his mother, and in the way of Jeroboam, the son of Nebat, who caused Israel to sin.
53 Ya bauta, ya kuma yi wa Ba’al sujada, ya tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila yă yi fushi, kamar yadda mahaifinsa ya yi.
Also, he served Baal, and he adored him, and he provoked the Lord, the God of Israel, in accord with all that his father had done.

< 1 Sarakuna 22 >